Aminiya:
2025-10-13@17:59:27 GMT

Yadda ’yan haya za su samu ragin N500,000 a shekara 

Published: 26th, September 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta amince da sabuwar dokar haraji wadda za ta bai wa ’yan haya damar samun ragin har Naira dubu ɗari biyar.

Dokar ta amince da yi wa ’yan haya ragin kashi 20% daga harajin kudin shiga a kan kuɗin hayar da suke biya a shekara.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda tare da ƙwato makamai a Neja Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso

Sai dai kuma, wannnan ragin ba zai haura haura Naira 500,000 ba.

Kafa sabuwar dokar

A watan Agustan shekarar 2023 Shugaba Bola Tinubu ya kafa kwamitin sake fasalin haraji karkashin jagorancin Taiwo Oyedele.

Bayan shekaru biyu, Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da sabbin dokoki guda hudu, wadanda shugaban kasar ya rattaba hannu kuma aka buga a kundin gwamnati a ranar 10 ga Satumba, 2025.

Wadannan sabbin dokokin haraji za su fara aiki daga 1 ga Janairu, 2026.

Sabbin dokokin sun hada da:

1- Dokar Haraji ta Nijeriya (NTA)

2- Dokagar Gudanar da Haraji

3- Dokar Hukumar Haraji ta Nijeria (NRS)Nigeria

4- Dokar Hukuamr Haraji ta Bai-daya

Sababbin dokoki sun maye gurbin dokoki fiye da guda 12 da suka dade suna aiki a bangaren harajin Nijeiya.

Ragin kudin hararji ga ’yan haya

Sashe na 30 (26) na Dokar Haraji ta Kasa (NTA), ya amince wa ’yan haya samun ragin haraji ta hanyar cire kashi 20 cikin 100 na kudin hayarsu na shekara daga abin da za su biya. Sai dai wannan rangwamen ba zai wuce Naira 500,000 ba.

Misali:

Idan kudin hayarka ta shekara Naira miliyan daya da dubu dari biyar ne, za ka iya samun ragin N300,000 (20%) daga haraji.

Idan kuma kudin hayarka ya kai N3,000,000, to N500,000 kawai za ka iya ragewa, duk da cewa 20% ya fi haka.

Wani hanzari ba gudu ba! Mutum ba zai ci gajiyar wannan rangwamen ba, sai idan ya bayyana kudin hayarsa daidai tare da gabatar da takardun da ke tabbatar da hakan.

Haka kuma, masu gidaje da kuma wadanda ke zaune a gidajen da ba sa biyan haya ba sa cikin masu cin gajiyar wannan rangwamen.

Wadanda dokar ta shafa su ne:

– Masu haya da ke da yarjejeniyar kwangilar haya a rubuce.

– Ba ta shafi masu gidaje da masu zama a gidajen gwamnati ko na kamfani ba tare da biyan haya ba.

Wani Karin sauki a dokar shi ne:

– An soke biyan harajin BAT a kan kayan abinci da ilimi.

– Masu karbar albashin kasa da Naira 800,000 a shekara ba za su biya harajin kudin shiga ba.

– Kananan ’yan kasuwa da cinikinsu a shekara bai fi Naira miliyan 100 ba, za su ci gaba da aiki ba tare da biyan harajin kamfani ba, amma dole su yi rajista da Hukumar Rajisar Kamfanoni (CAC) tare da amfani da tsarin e-inboicing.

– Sa’annan, an soke harajin tambari daga yarjejeniyar haya da kudinta bai fi Naira miliyan 10 ba a kowane wata.

Haka kuma;

– Masu saka hannun jari a harkar gidaje za su ci gajiyar rangwamen haraji ta hanyar REITs.

– Harajin rikon kudi (withholdin tad) a kan haya ya sauka zuwa kashi 2 cikin 100 ga ’yan kasa, yayin da ’yan kasashen waje za su biya kashi 5 cikin 100.

Wasu karin dokoki su ne:

– Masu samun kudaden shiga sama da Naira miliyan 50 za su biya haraji har na kimanin kashi 25 cikin 100.

– Wannan sabon tsarin ya hada da dukiyar da ake samu daga kasashen waje, ribar jarin da aka samu (har da kadarorin crypto), da kuma fa’idodin da ba a ba da su kai tsaye ba.

– Manyan kamfanoni za su ci gaba da biyan harajin kamfani na kashi 30 cikin 100, duk da cewa wasu muhimman sassa na tattalin arziki na iya samun rangwame zuwa kashi 25 cikin 100.

– Kamfanonin kasa da kasa za su fara biyan mafi karancin haraji na kashi 15 cikin 100, tare da karin haraji a kan ribar da ba a raba ba da ke waje.

Sabon tsarin harajin ya nufi karfafa gaskiya da bin doka a cikin tsarin kudi na kasa.

Masana irin su Barista Festus Adebayo, daraktan cibiyar kare hakkokin gidaje (HDAN), na ganin  sabuwar dokar na da na da amfani sosai.

“Babban sauki ne ga masu haya saboda mun shawarci kwamitin haraji da a yi doka dam za ta kawo mana sauki mana a fannin gidaje, kuma sun yi abin da muka roka.

“Mun fi son a dora wa masu kudi nauyi, a yi wa talakawa rangwame,” in ji shi.

Ya kuma yi kira da a fara dora haraji kan gidajen da aka gina amma aka bar su ba a amfani da su domin tilasta masu su yin amfani da su yadda ya dace.

Ku mene ne ra’ayinku?

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Haraji Gwamnatin tarayya haya Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%

Kasar China ta maida martani kan kasar Donal Trump na kasar Amurka, wanda ya karawa kasar kudaden fito 100% na kayakin kasar da ke shigowa Amurka.

SHafin yanar gizo na ArabNews ya nakalto kasar China a jiya Asabar tana cewa zata dauki matakan da suka dace kan Karin kudanen fito na 100% wanda shugaban Trump yayi. Kuma ta yi kira ga Trump kan cewa ya rungumi tattaunawa da kasar China ya fi masa kan barazana gareta.

Ma’aikatar kasuwanci na kasar China ta bayyana cewa, basa son yakin kudaden fito amma basa tsoronta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba
  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100%
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe