An rufe wurin haƙar zinare a Kebbi
Published: 26th, September 2025 GMT
Gwamna Nasir Idris ya ba da umarnin gaggauta rufe wurin haƙar zinare da ke Mararrabar Birnin Yauri a Karamar Hukumar Ngaski ta Jihar Kebbi.
Yayin da yake ba da wannan umarnin, ya ce an dauki matakin ne domin kawar da matsalar haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma daƙile duk wata barazana da za kawo tarnaƙi a cikin al’umma.
Aminiya ta ruwaito cewa, ziyarar bazata da gwamnan ya kai cibiyar haƙar zinaren a ranar Alhamis, na zuwa ne bayan rikicin da aka yi tsakanin mazauna yankin da kuma jami’an gwamnatin tarayya da ke aiki a wurin.
A cewarsa, za a ci gaba da harkar haƙar zinare da zarar an samu maslaha tsakanin gwamnatin Kebbi da kuma jami’an da ke aiwatar da shirin gwamnatin tarayya na haƙar zinare wato PAGMI.
Gwamnan ya kuma bai wa ma’aikatar haƙar maadanai ta jihar umarnin tattara bayanan duk wasu mutane, ƙungiyoyi ko kamfanoni da ke da rajistar haƙar zinare ko wasu ma’adanai a kowane sassa na Jihar Kebbi domin tsaftace harkar.
Ya bayyana cewa “ba za mu zuba ido wasu mutane daga ƙasashen ƙetare irin su Mali, Tanzania, Chadi da Nijar su riƙa shigowa suna haifar da barazanar tsaro a jiharmu ba.”
Ana iya tuna cewa, da yammacin Lahadin da ta gabata ne aka saka dokar hana fita a garin Yauri da ke Jihar Kebbi bayan wani tashin hankali tsakanin masu haƙar zinare da matasan gari, abin da ya yi sanadin mutuwar wani matashi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: haƙar zinare Jihar Kebbi haƙar zinare
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.
Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.
Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”
Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.
Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.