Aminiya:
2025-11-27@22:28:05 GMT

An rufe wurin haƙar zinare a Kebbi

Published: 26th, September 2025 GMT

Gwamna Nasir Idris ya ba da umarnin gaggauta rufe wurin haƙar zinare da ke Mararrabar Birnin Yauri a Karamar Hukumar Ngaski ta Jihar Kebbi.

Yayin da yake ba da wannan umarnin, ya ce an dauki matakin ne domin kawar da matsalar haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma daƙile duk wata barazana da za kawo tarnaƙi a cikin al’umma.

Majalisar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi Naira biliyan 75 Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato

Aminiya ta ruwaito cewa, ziyarar bazata da gwamnan ya kai cibiyar haƙar zinaren a ranar Alhamis, na zuwa ne bayan rikicin da aka yi tsakanin mazauna yankin da kuma jami’an gwamnatin tarayya da ke aiki a wurin.

A cewarsa, za a ci gaba da harkar haƙar zinare da zarar an samu maslaha tsakanin gwamnatin Kebbi da kuma jami’an da ke aiwatar da shirin gwamnatin tarayya na haƙar zinare wato PAGMI.

Gwamnan ya kuma bai wa ma’aikatar haƙar maadanai ta jihar umarnin tattara bayanan duk wasu mutane, ƙungiyoyi ko kamfanoni da ke da rajistar haƙar zinare ko wasu ma’adanai a kowane sassa na Jihar Kebbi domin tsaftace harkar.

Ya bayyana cewa “ba za mu zuba ido wasu mutane daga ƙasashen ƙetare irin su Mali, Tanzania, Chadi da Nijar su riƙa shigowa suna haifar da barazanar tsaro a jiharmu ba.”

Ana iya tuna cewa, da yammacin Lahadin da ta gabata ne aka saka dokar hana fita a garin Yauri da ke Jihar Kebbi bayan wani tashin hankali tsakanin masu haƙar zinare da matasan gari, abin da ya yi sanadin mutuwar wani matashi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: haƙar zinare Jihar Kebbi haƙar zinare

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Jami’an tsaro a Jihar Kaduna, sun fara gudanar da babban samame domin kawar da ’yan ta’adda da ’yan bindiga a wasu ƙananan hukumomin jihar.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gudanar da aikin tare haɗin gwiwar sojoji, DSS, NSCDC, KADVS, da kuma ƙungiyoyin sa-kai da mafarauta.

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

Aikin ya shafi ƙananan hukumomin Makarfi, Hunkuyi da Ikara.

Rundunar ta ce manufar wannan samame shi ne “share dukkanin maɓoyar miyagu, rushe sansanonin da suka kafa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.”

Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci dukkanin rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar nan su ƙara ƙaimi wajen yaƙi da aikata laifuka.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Rabiu Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa jami’an tsaro za su ci gaba da matsa wa miyagu lamba.

Ya ce za su ci gaba da yin gwiwa da rundunonin tsaro domin tabbatar da tsaro a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila