Aminiya:
2025-10-13@17:54:15 GMT

An rufe wurin haƙar zinare a Kebbi

Published: 26th, September 2025 GMT

Gwamna Nasir Idris ya ba da umarnin gaggauta rufe wurin haƙar zinare da ke Mararrabar Birnin Yauri a Karamar Hukumar Ngaski ta Jihar Kebbi.

Yayin da yake ba da wannan umarnin, ya ce an dauki matakin ne domin kawar da matsalar haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma daƙile duk wata barazana da za kawo tarnaƙi a cikin al’umma.

Majalisar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi Naira biliyan 75 Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato

Aminiya ta ruwaito cewa, ziyarar bazata da gwamnan ya kai cibiyar haƙar zinaren a ranar Alhamis, na zuwa ne bayan rikicin da aka yi tsakanin mazauna yankin da kuma jami’an gwamnatin tarayya da ke aiki a wurin.

A cewarsa, za a ci gaba da harkar haƙar zinare da zarar an samu maslaha tsakanin gwamnatin Kebbi da kuma jami’an da ke aiwatar da shirin gwamnatin tarayya na haƙar zinare wato PAGMI.

Gwamnan ya kuma bai wa ma’aikatar haƙar maadanai ta jihar umarnin tattara bayanan duk wasu mutane, ƙungiyoyi ko kamfanoni da ke da rajistar haƙar zinare ko wasu ma’adanai a kowane sassa na Jihar Kebbi domin tsaftace harkar.

Ya bayyana cewa “ba za mu zuba ido wasu mutane daga ƙasashen ƙetare irin su Mali, Tanzania, Chadi da Nijar su riƙa shigowa suna haifar da barazanar tsaro a jiharmu ba.”

Ana iya tuna cewa, da yammacin Lahadin da ta gabata ne aka saka dokar hana fita a garin Yauri da ke Jihar Kebbi bayan wani tashin hankali tsakanin masu haƙar zinare da matasan gari, abin da ya yi sanadin mutuwar wani matashi.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: haƙar zinare Jihar Kebbi haƙar zinare

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

“Shekaru goma da suka wuce, gudummawar da ma’adanai ke bayarwa ga GDP na kasarmu bai wuce 0.5% ba, amma a yau ya karu zuwa 1.8% – alkalumman NBS suka nuna a cikin rabi na biyu na 2025 wanda ba a taba ganin irinsa ba”.

 

Da yake tsokaci kan ci gaban fannin, Ministan ya bayyana cewa, makon hako ma’adanai na Nijeriya ya yi nuni da yadda masana’antar ke sauya tunani zuwa tsari mai kyau, da sabbin abubuwa, da ke lalubo masu zuba jari na kasa da kasa.

 

Ya bayyana cewa, sauye-sauyen sun tattara ne a kan gaskiya, rage haɗari, da inganta masana’antar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025 Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025 Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi” October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida