Leadership News Hausa:
2025-10-13@17:54:14 GMT

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Published: 26th, September 2025 GMT

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

A Benuwe, sojoji sun kashe wani, sun kuma ceto fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su, yayin da aka ceto wasu uku a Kwara.

A Nasarawa, an kama mutane biyu da ke safarar miyagun ƙwayoyi, a Imo kuma, an cafke masu safarar bindigu.

Hakazalika, a Anambra, sojoji sun daƙile ayyukan IPOB/ESN tare da ƙwato abubuwan fashewa.

A jihohin Delta da Bayelsa kuma, an ƙwato bindigogi, harsasai da miyagun ƙwayoyi da yawa.

Sama da lita 1,200 na man fetur da aka tace ba bisa ƙa’ida ba, ak kama a Ribas da Bayelsa.

Gaba ɗaya, sojojin sun ƙwato bindigogi, harsasai, abubuwan fashewa, babura, man fetur, takin zamani da miyagun ƙwayoyi daga hannun ‘yan ta’adda da sauran masu laifi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan ta adda Farmaki

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno

Sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram 9 tare da kwato kudi fansa kimanin Naira miliyan 5 a  yankunan Magumeri da Gajiram a jihar Borno.

Kakakin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), Laftanar Kanar Sani Uba , ya ce sojojin da suke sintiri a yankunan ne suka hallakan mayakan bayan sahihan bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan ta’addan a kusa da Goni Dunari a Karamar Hukumar Magumeri.

Sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025 ta ce, “Dakarun mu sun yi gaggawar daukar matakin dakile barazanar bayan da suka ga yadda ’yan ta’addan suka kona gidaje tare da tsoratar da mutanen yankin.”

Ya bayyana cewa sojoji sun yi artabu da ’yan ta’addan ne bayan sun shafe sa’o’i hudu suna bibiyar su, inda suka kashe mayaka biyar tare da tilasta wa sauran tserewa.

Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni

Kayayyakin da aka kwato sun haxa da bindiga kirar AK-47, alburusai, wuqa, da wayar hannu.

Uba ya qara da cewa “Babu asarar rayuka ko asarar kayan aiki da sojojin mu suka yi.”

A wani samamen kuma a hanyar Gajiram Bolori – Mile 40 – Gajiganna, sojoji sun yi arangama da mayakan Boko Haram a kusa da kauyen Zundur, inda suka kashe ’yan ta’adda hudu tare da kubutar da wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su daga Guzamala.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da wata mota, sabbin wayoyin hannu guda biyu, man fetur lita 30, da tsabar kudi da suka kai Naira miliyan 4.35.

Binciken farko ya nuna cewa ’yan ta’addan sun bukaci naira miliyan 2 da wayoyi biyu a matsayin kudin fansa ga dan uwan ​​wadanda suka kama kafin sojojin su kai dauki.

Laftanar Kanar Uba ya tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka matsin lamba kan ’yan ta’addan tare da hana su sakat.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano