Aminiya:
2025-10-13@15:47:16 GMT

An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna Zulum

Published: 25th, September 2025 GMT

Wasu da ake kyautata zaton ’yan bangar ’yan siyasa ne sun kashe wasu yara biyu na Zannah Jaridama Bornoye wani mai goyon bayan Gwamnan Borno Babagana Zulum, da na maƙwabcinsa kwanaki kaɗan bayan da Zannan ya fito ƙarara ya caccaki waɗanda ake zargin ’yan siyasa ne a jihar da ke zagon ƙasa ga gwamnatin Zulum.

Kamar yadda rahoton ke nunawa Zannah Jaridama, wanda ya zargi wasu manyan mutane da munafunci da zagon ƙasa ga gwamnatin mai gidansa Gwamna Zulum, ya koka a cikin wani faifan bidiyo.

Zan kare muradun Yarbawa idan aka zaɓe ni a 2027 — Atiku Hajjin 2025: Mun samu nasarori a Yobe — Mai Aliyu Biriri

Yana cewa, wasu mutane na kusa da gwamnan suna nuna cewa masu biyayya ne tare da wadatar da kansu da kwangiloli, muƙamai da dukiyar gwamnati ba tare da nuna kishin gaskiya ga jama’a ko hangen nesa na gwamna ba.

Ya koka da cewa, yayin da Farfesa Zulum ke ɗaukar nauyin mulki da ayyuka da yawa daga cikin waɗanda ke da’awar cewa su ne masu yi masa biyayya, yadda suke gina manyan gidaje na alfarma sai ga shi suna zagon ƙasa ga gwamnatinsa.

Daga bisani ya jajirce kan duk wanda ya ji bai masa daɗi ba ya kai shi kotu, yana mai cewa zai bayyana sunayensu a bainar jama’a nan gaba kaɗan.

Majiyar na cewar, bayan kusan awanni 24 bayan kalaman nasa, wannan kisan gilla na kashe waɗannan yara ya afku.

Waɗannan yara biyu da aka yi wa kisan gilla sun haɗa da Mama yarinya ’yar shekara 14 da Anwar ɗan wata 28 waɗanda daga farko aka neme su aka rasa waɗanda ana zargin an sace su ne a ƙofar gidansu, amma kwanaki kaɗan sai aka tsinci gawarwakin yaran da sanyin safiyar yau Alhamis a boot ɗin motarsa.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Borno, Nazir Abdulmajid wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an gano gawarwakin yaran a cikin boot ɗin a wata tsohuwar motarsa ​​da aka kulle a harabar gidan.

A yanzu dai haka an baza jami’an rundunar ’yan sanda inda lamarin ya faru kuma an ɗauki hotuna, kuma an kai gawarwakin su zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri domin a tantance ko an yi garkuwa da su ne aka kashe su ko kuma sun shiga boot ne suka kulle kansu har suka mutu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno

Rundunar sojin Najeriya, ta bayyana cewa dakarunta sun kashe ’yan ta’adda biyar a wani samame da suka kai yankin Magumeri da Gajiram, a Jihar Borno.

Kakakin rundunar Operation Haɗin Kai, Kanar Sani Uba, ya ce dakarun sun yi arangama da wasu ’yan ta’adda 24 da ke tafe a ƙafa a ranar Juma’a.

Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina

A cewar sanarwar da ya fitar, sojojin sun yi nasarar kashe biyar daga cikinsu tare da ƙwato kuɗi Naira miliyan biyar.

“An hangi ’yan ta’addan suna ƙone gidaje da kuma kai wa mutane hari, sai dakarun suka fara bin su, inda suka tsere zuwa ƙauyen Damjiyakiri,” in ji Kanar Sani.

Ya ƙara da cewa bayan awanni huɗu ana bin su, sojoji suka sake kai musu farmaki, inda suka kashe biyar daga cikinsu, sauran 19 kuma suka tsere da raunuka.

Abubuwan da aka ƙwato daga hannunsu, sun haɗa da bindiga ƙirar AK-47, jakar harsashi gyda biyar, waya guda ɗaya da wuƙa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno