Aminiya:
2025-11-27@22:01:25 GMT

Zan kare muradun Yarbawa idan aka zaɓe ni a 2027 — Atiku

Published: 25th, September 2025 GMT

Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar ya yi alƙawarin cewa muradin Yarbawa za su zama a matsayi mafi girma a cikin manufofin gwamnatinsa idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Ya bayyana cewa akwai labari mara tushe ko kuma fargabar cewa, a shugabancinsa idan aka zaɓe shi, “zai maida hankali ne kan Hausa/Fulani fiye da Yarbawa ko wasu ƙabilu.

An gurfanar da malamai kan zargin lalata da ɗalibarsu a Zariya Hajjin 2025: Mun samu nasarori a Yobe — Mai Aliyu Biriri

“Yarbawa suna cikin dangina ne kuma surikaina,” Atiku ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja ta hannun mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Kola Johnson.

Tsohon mataimakin shugaban Ƙasar ya jaddada cewa alaƙar aurensa da Yarbawa ya sa irin wannan fargabar bata da tushe balle makama.

Ya ce, “Na yi matuƙar farin ciki da na sami mata daga cikin wannan nau’in jinsin, wanda hakan ke nuna cewa dangantakar da ke tsakanina da Yarbawa ta yi daidai da nasabar jinsin iyali.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa Yarbawa, ko ɗaiɗaiku ko kuma rukunin jama’a, sun kasance suna da matsayi na musamman a cikin zuciyata.”

Ya yi alƙawarin cewa idan aka zaɓe shi, yankin Kudu-maso-maso-Yamma zai kasance jigon aiwatar da manufofinsa.

“Haka kuma a dalilin haka ne muradin Yarbawa za su kasance a kodayaushe wajen aiwatar da manufofina da gudanar da mulkina da yardar Allah idan na yi sa’ar nasarar zama shugaban ƙasa a 2027.

“Saboda haka, tsoron zama na shugaban ƙasa na iya haifar da mulkin bai wa Hausa/Fulani fifiko a kan Yarabawa ko wasu ƙabilu kawai bai taso ba, har ma ba shi da tushe balle makama domin ɗaukacin kabilar Yarabawa dangi ne da kuma surukaina,” in ji shi.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya bayar da misali da aurensa na farko da Titi ’yar Yarbawa ce ’yar Ijesha, wadda ya aura a shekarun 1970, a matsayin hujjar alaƙarsa da yankin Kudu maso Yamma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar idan aka zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A cikin shekarun nan, matsalolin tsaro a Najeriya—kamar ta’addanci, da garkuwa da mutane, da rikicin manoma da makiyaya, da kuma ayyukan ’yan bindiga—suna kara ta’azzara, lamarin da ya sanya al’umma da masana tsaro ke tambayar wace hanya ta fi dacewa gwamatani ta yi amfani da shi wajen kawo karshen wadannan matsaloli da suka ki ci suka ki cinyewa tsawon shekaru.

 

Yayin da wasu ke ganin amfani da karfin soji ne kadai hanyar da zai kawo karshen wannan matsala, wasu na ganin tattaunawa ne kadai mafita, wasu har ila yau na ganin idan aka yi amfani da gaurayen biyun zai fi dacewa.

NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?

Ko wanne daga cikin wadannan hanyoyi ne idan gwamnati ta yi amfai dashi ko da su don magance wannan matsala?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi