Aminiya:
2025-10-13@15:50:23 GMT

2027: Zan kare muradun Yarbawa idan aka zaɓe ni Shugaban Ƙasa — Atiku

Published: 25th, September 2025 GMT

Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar ya yi alƙawarin cewa muradin Yarbawa za su zama a matsayi mafi girma a cikin manufofin gwamnatinsa idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Ya bayyana cewa akwai labari mara tushe ko kuma fargabar cewa, a shugabancinsa idan aka zaɓe shi, “zai maida hankali ne kan Hausa/Fulani fiye da Yarbawa ko wasu ƙabilu.

An gurfanar da malamai kan zargin lalata da ɗalibarsu a Zariya Hajjin 2025: Mun samu nasarori a Yobe — Mai Aliyu Biriri

“Yarbawa suna cikin dangina ne kuma surikaina,” Atiku ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja ta hannun mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Kola Johnson.

Tsohon mataimakin shugaban Ƙasar ya jaddada cewa alaƙar aurensa da Yarbawa ya sa irin wannan fargabar bata da tushe balle makama.

Ya ce, “Na yi matuƙar farin ciki da na sami mata daga cikin wannan nau’in jinsin, wanda hakan ke nuna cewa dangantakar da ke tsakanina da Yarbawa ta yi daidai da nasabar jinsin iyali.

“Wannan shi ne dalilin da ya sa Yarbawa, ko ɗaiɗaiku ko kuma rukunin jama’a, sun kasance suna da matsayi na musamman a cikin zuciyata.”

Ya yi alƙawarin cewa idan aka zaɓe shi, yankin Kudu-maso-maso-Yamma zai kasance jigon aiwatar da manufofinsa.

“Haka kuma a dalilin haka ne muradin Yarbawa za su kasance a kodayaushe wajen aiwatar da manufofina da gudanar da mulkina da yardar Allah idan na yi sa’ar nasarar zama shugaban ƙasa a 2027.

“Saboda haka, tsoron zama na shugaban ƙasa na iya haifar da mulkin bai wa Hausa/Fulani fifiko a kan Yarabawa ko wasu ƙabilu kawai bai taso ba, har ma ba shi da tushe balle makama domin ɗaukacin kabilar Yarabawa dangi ne da kuma surukaina,” in ji shi.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya bayar da misali da aurensa na farko da Titi ’yar Yarbawa ce ’yar Ijesha, wadda ya aura a shekarun 1970, a matsayin hujjar alaƙarsa da yankin Kudu maso Yamma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar idan aka zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk

Shugaban kasar Amurka ya yi barazana ga shugaban kasar Rasha na aike wa Ukraine makamai masu linzami kirar Tomahawk

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce: Zai gargadi takwaransa na Rasha Vladimir Putin cewa: Akwai yiwuwar Ukraine za ta iya samun makamai masu linzami kirar “Tomahawk” idan Rasha ba ta kawo karshen yakin Ukraine ba.

Da aka tambaye shi a cikin jirgin Air Force One da ke kan hanyarsa ta zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila da Masar da yammacin ranar Lahadi ko shi da kansa zai tattauna da Putin kan batun, Trump ya ce, “Yana iya magana da shi. Yana cewa: Idan ba a warware wannan yakin ba, zai aika wa Ukraine da makamai masu linzami na Tomahawk.”

Trump ya kara da cewa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya bukaci makamai masu linzami na Tomahawk lokacin da suka tattauna sabbin makamai ga kasar ke bukata ta wayar tarho a ranar Asabar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice   October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
  • 2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe