Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@15:53:19 GMT

Gwamnatin Kano Ta Rarraba Takardun Guraben Karatu Ga Dalibai

Published: 25th, September 2025 GMT

Gwamnatin Kano Ta Rarraba Takardun Guraben Karatu Ga Dalibai

Gwamnatin jihar Kano, ta raba wa daliban da suka kamala karatun Furamare takardun gurbin karatu zuwa manyan makarantun sakandare a fadin jihar.

 

Da yake jawabi yayin bikin kaddamarwar a makarantar sakandiren ’yan mata ta Maryam Aloma da ke Kano, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya ce shirin ya nuna yadda gwamnati ta himmatu wajen samar da ilimi kyauta da kuma wayar da kan al’umma don bunkasa ilimi.

 

Dokta Makoda ya bayyana sauye-sauyen da gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta bullo da su, da suka hada da daukar malamai aiki, gyaran makarantu, da samar da kayayyakin koyarwa, inda ya bayyana su a matsayin matakan farfado da harkar ilimi.

 

Ya danganta fitowar jihar Kano a matsayin jihar da ta zo kan gaba a jarabawar NECO ta shekarar 2025 ga yadda Gwamna Yusuf ya ba da fifiko a fannin ilimi, inda ya yaba wa gwamnan kan yadda ya rika tallafa wa bukatun ma’aikatar.

 

“Mai girma Alhaji Abba Kabir Yusuf yana aiki tukuru, shi ya sa harkar ilimi ta Kano ke tafiya cikin hanzari, misali, don magance matsalar karancin malaman lissafi, gwamna ya amince da daukar sabbin ma’aikata, kuma nan ba da dadewa ba za a tura su makarantu a fadin jihar.” Inji Dr. Makoda.

 

Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyaye da su kara kaimi ga kokarin gwamnati ta hanyar tabbatar da ‘ya’yansu na zuwa makaranta akai-akai domin samun ilimi mai inganci.

 

A nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da manyan makarantun sakandire ta jihar Kano, Alhaji Rabi’u Saleh Gwarzo, ya bayyana cewa, Kano ba ta taba shiga matsayi na gaba na NECO ba sai a yanzu, inda ya ce wannan nasarar ta samu ne sakamakon yadda Gwamna Yusuf ya himmatu wajen inganta ilimi.

 

Ya jaddada bukatar yin aiki tare tsakanin Hukumar Kula da Ilimi ta (SUBEB), Hukumar Kula da Manyan Makarantu ta Sakandare, da Sashen Albarkatun Ilimi don ba da tabbacin samun sauyi ga dalibai.

 

Hakazalika, shugaban kungiyar iyaye da malamai ta jiha (PTA), Alhaji Dahiru Salisu Mai Jimiri da shugaban kwamitin kula da makarantu (SBMC), Tijjani Haladu Baraya, sun yaba da kokarin gwamnati na farfado da ilimi tare da yin kira ga iyaye da kungiyoyin farar hula da su ci gaba da tallafawa gwamnati.

 

Shirin wanda ake ganin wani muhimmin mataki ne na dorewar ci gaban ilimi a Kano, ya samu halartar daraktocin shiyya, jami’an ma’aikatar, da manyan wakilan SUBEB da kuma hukumar kula da manyan makarantun sakandire.

 

COV/KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025 Manyan Labarai An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro October 12, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22 October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki