Leadership News Hausa:
2025-10-13@15:47:18 GMT

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

Published: 25th, September 2025 GMT

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

A ƙarshe, Shugaban ya ce matakan da gwamnati ta ɗauka kamar cire tallafin mai da sauya tsarin kuɗi, duk duk sanya shan wahala amma wajibi ne domin tabbatar da cigaba. Ya jaddada cewa Nijeriya za ta ci gaba da kare haƙƙin ɗan Adam, da haɗin kai da zaman lafiya, inda ya gargaɗi duniya da cewa babu wanda zai tsira sai idan duk mun tsira tare.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majilisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar  shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
  • Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya