Muhimman abubuwa 7 da Najeriya ta fada yayin jawabinta a taron MDD
Published: 25th, September 2025 GMT
A yayin taron babban zauren Majalisar Dinkin Duniya (UNGA) karo na 80, Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya gabatar da jawabin Najeriya a madadin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Jawabinsa ya ƙunshi kira ga gyare-gyare, adalci a harkokin tattalin arziki, da goyon bayan zaman lafiya da haɗin kai na duniya.
Ga muhimman batutuwa bakwai da Najeriya ta jaddada a yayin jawabinta a wannan taron:
Bai wa Najeriya kujera a Kwamitin Tsaro na majalisarNajeriya ta buƙaci samun kujerar dindindin a Kwamitin Tsaro/Sulhu na majalisar, tana mai cewa rashin wakilcin Afirka a matakin yanke shawara na duniya yana rage kimar tsarin.
Shettima ya jaddada cewa rawar da Najeriya ke takawa a harkar zaman lafiya da tsaro ta cancanta a ba ta kujerar dindindin a kwamitin.
“Bukatar mu ta kujerar dindindin… kira ne na adalci, wakilci, da gyaran da zai dawo da martabar wannan majalisar da ke ɗauke da burin haɗin kai na duniya.”
A cikin kalamai masu ƙarfi, Shettima ya jaddada goyon bayan Najeriya ga samar da mafita ta kasashe biyu a rikicin Isra’ila da Falasdinu.
Ya buƙaci a bai wa Falasdinawa ’yanci da mutunci kamar sauran al’ummar kowacce kasa, yana mai kiran halin da ake ciki a yankin a matsayin babban tabo ga muradun duniya.
“Muna fada ba tare da wata shakka ba, cewa mafita ta kasashe biyu ita ce hanya mafi mutunci da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa ga al’ummar Falasdinu.”
Gyara tsarin kuɗi na duniyaShettima ya buƙaci a sake fasalin tsarin kuɗi na duniya don ya dace da halin da ƙasashe masu tasowa ke ciki.
Ya soki tsarin bashi da saka hannun jari da ke tauye ci gaban ƙasashe masu tasowa musamman na Afirka.
Najeriya ta soki yadda ake cin moriyar ma’adinan Afirka ba tare da amfani da su wajen bunƙasa al’umma ba. Shettima ya buƙaci a samar da ayyukan yi da masana’antu a yankunan da ake haƙar ma’adanan, tare da bunkasa haɗin gwiwa.
“Za mu ƙarfafa tsarin duniya idan ƙasashen da ke samar da ma’adanan duniya suka ci moriyar su ta fuskar zuba hannun jari, haɗin gwiwa, sarrafa su a gida da samar da ayyukan yi.”
Rage tazarar fasaha a AfirkaShettima ya gabatar da shirin haɗin gwiwa na duniya don rage gibin tazarar da aka yi wa nahiyar Afirka a fannin fasaha.
Ya buƙaci haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci, masana, da kamfanoni masu zaman kansu don tabbatar da cewa ci gaban fasaha ya shafi kowa.
Yaki da yaɗa labaran karyaShettima ya bayyana haɗarin da ke tattare da kirkira da kuma yada labaran ƙarya, musamman a ƙasashen da ke da raunin tsarin dimokuraɗiyya.
Ya buƙaci a samar da matakan kariya da za su tabbatar da gaskiya da amincewa a duniyar fasaha.
Kira kan samar da kotun kuɗi ta duniyaNajeriya ta buƙaci a kafa kotun duniya da za ta rika duba harkokin kuɗi da warware rikice-rikice a tsakanin ƙasashe.
Wannan, a cewar Shettima, zai ƙara gaskiya da bin doka a harkokin kuɗi na duniya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya ya buƙaci a haɗin gwiwa Ya buƙaci a Najeriya ta Shettima ya
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Ta wadanne hanyoyi cutar Kansa ke farawa?
Kowace kwayar halitta ta jikin mutum akwai aikin da take yi, asalin kwayar halittar ta kan kasu kashi-kashi; suna mutuwa idan aka fitar da su ko kuma suka lalace, sai wata kwayar ta maye gurbinsu. A irin wannan lokaci ne, Kansar ke samun gurin zama sai ta zuba tata kwayar halittar ta kori asalin kwayar halittar da ke jikin Dan’adam, wanda hakan ke jawo matsaloli a sassan jikin da Kansar ta kama.
Saboda haka, kwayar cutar Kansa; ta kan watsu a sauran sassan jiki, misali Kansar huhu ta kan tafi cikin kasusuwa ta girma, a yayin da kwayar ta yadu; ana kiranta da suna ‘meh-TAS-tuh-sis’, ita kuma Kansar huhu idan ta tafi cikin kasusuwa; ana kiran ta da suna ‘Lung Cancer’ a turance. A bangaren likitoci, kwayar cutar Kansar da ta shiga cikin kashi; daidai ta ke da ta huhu, sai dai idan ta yadu a cikin kashin.
Banbance-banbancen cutar Kansa:
Wata Kansar ta kan yadu ne cikin gaggawa, yayin da kuma wata ta ke yaduwa a hankali a hankali, sannan kowacce ana iya yin maganinta ta hanyoyi daban-daban, wata ta hanyar tiyata kadai za a iya samun waraka; wata kuma ta hanyar shan magani.
Idan mutum yana dauke da Kansa, likita ya kan yi kokari wajen gano irin Kansar da yake dauke da ita. Mutanen da ke da cutar Kansa, ana yi musu magani ne gwargwadon irin yanayin wadda suke dauke da ita.
Wane matsayi cutar Kansa ta taka?
Duk wanda ke dauke da wannan cuta ta Kansa, likita zai so sanin matakin da ta kai, daga inda ta fara ana kiran sa a turance ‘Cancer Stage’, sannan matsayin da Kansar ta ke shi ne zai taimaka wajen sanin maganin da za a dora mai dauke da lalurar a kai.
Kowace irin Kansa, akwai gwajin da ake yi domin gano matasayin da ta kai. A dokar gwajin matakinta na farko da kuma mataki na biyu, na nuna Kansar ba ta yi karfi sosai ba. Mataki na uku da na hudu kuma yana nuna ta yadu sosai. Mataki na hudu shi ne makura wajen yaduwar ta.
Alamomin 20 Na Kamuwa Da Cutar Kansa:
1- Shashsheka da karancin numfashi
2- Tari da ciwon kirji, alama ce ta Kansar huhu ko ta bargo ciwon kirjin kan kasance daga kirjin zuwa kafada, sannan ya sauko zuwa hannu
3- Zazzabi da saurin kamuwa da ciwo, hakan na faruwa ne dalilin asalin kwayar halittar jinin mutum ta tabu
4- Fama wajen hadiye abu, wannan na nuni da an kamu da wannan cuta
5- Futowar kurji me ruwa a wuya, hammata da kuma gwiwa
6- Yawan zubda jini
7- Kasala da yawan gajiya
8- Kumburin ciki
9- Rashin sha’awar abu da kuma daukewar dandano
10- Ciwon ciki da mara
11- Fitar jini daga dubura
12- Rama lokaci guda
13- Yawan ciwon ciki
14- Nono ya yi ja ya kumbura alama ce ta ‘breast cancer’
15- Canjawar kan nono
16- Nauyi da kuma ciwo na fitar hankali a lokacin al’ada, wannan ita ma alama ce ta ‘uterus cancer’, ana bukatar yin hoto (transbiginal)
17- Kumburin fuska
18- Canjawar farce, zai iya kasancewa ‘lung cancer’, idan kuma ya kode ya yi fari to ‘liber cancer’ ne
19- Ciwon baya a bangaren dama, yana nuni da ‘liber cancer’ ko ‘breast cancer’
20-Fesowar kuraje a jikin mutum
Amma sai an je asibiti an ga likita kafin a tabbatar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA