Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@17:53:39 GMT

Jigawa Za Ta Kafa Kananan Bankuna 5 A Wasu Sassan Jihar

Published: 25th, September 2025 GMT

Jigawa Za Ta Kafa Kananan Bankuna 5 A Wasu Sassan Jihar

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce ta amince da fara shirin karbar lasisin aiki don kafa sabbin Kananan bankunan guda 5 a wasu wurare da aka zaba a fadin jihar.

 

Kwamishinan yada labarai na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

 

A cewarsa, shirin wani bangare ne na dabarun gwamnatin jihar na fadada hanyoyin samar da kudade da zurfafa shiga harkokin tattalin arziki a yankunan karkara da marasa galihu.

 

Ya bayyana cewa, za a kafa bankunan masu karamin karfi a kananan hukumomin Birniwa, Gujungu – Taura, Guri, Gwaram da Kaugama.

 

Ya ce, shawarar da majalisar ta yanke ya nuna irin sadaukarwar da gwamnatin Gwamna Umar Namadi ta yi na bunkasa hada-hadar kudi a matsayin wani makami na rage radadin talauci, bunkasa sana’o’in cikin gida, da karfafa tattalin arziki daga tushe.

 

Sagir ya ci gaba da cewa, sabon tallafin kudi na da nufin karawa kananan bankunan jihar tallafi, da samar da ayyuka na kudi kamar tanadi, bashi, da tallafin kananan ‘yan kasuwa ga daidaikun jama’a da al’ummomin da a al’adance ke cire su daga tsarin banki na zamani.

 

Ya kuma bayyana cewa, majalisar ta kuma amince da bayar da kwangilar samar da lantarki ta amfani da hasken rana a muhimman cibiyoyin zamantakewar al’umma a jihar.

 

Ya ce, darajar kwangilar ta kai sama da naira miliyan 733, inda ya kara da cewa amincewar ya yi daidai da manufofin shirin samar da hanyoyin samar da hasken rana na jihar, wanda aka tsara shi don fadada wutar lantarki zuwa sassa masu muhimmanci kamar ilimi, kiwon lafiya, da sauran muhimman ababen more rayuwa a fadin Najeriya.

 

Kwamishinan ya ce, tsarin tantancewar fasaha da tsare-tsare zai samar da cikakken tantance bukatun makamashi, dacewa da kayayyakin more rayuwa, da kuma tsare-tsaren aiwatar da aikin shimfida tsarin hasken rana a zababbun makarantu, cibiyoyin kiwon lafiya, da sauran muhimman cibiyoyin gwamnati a fadin jihar Jigawa.

 

Ya kara da cewa, aikin na nuni da yadda gwamnatin Namadi ta kuduri aniyar samar da hanyoyin samar da makamashi mai dorewa, da samar da ababen more rayuwa masu jure yanayi, da kuma inganta ayyukan hidima a sassa masu muhimmanci.

 

KARSHE/USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu ma’aurata da wasu mutane biyar bisa zarginsu da gudanar da ɗaurin aure ba tare da izinin iyayensu ba ko kuma bin tsarin addinin Musulunci a unguwar Nasarawa da ke cikin birnin Kano. Wadanda ake zargin sun hada da ango mai suna Aminu mai shekaru 23 da amaryarsa Sadiya mai shekaru 22. Sauran wadanda aka kama su ne Umar mai shekaru 24 wanda ya kasance wakilin ango; Abubakar, mai shekaru 23, wanda ya kasance waliyyin amarya; Usaina, mai shekaru 21; da kuma wasu ‘yan mata guda biyu wadanda suka kasance shaidu a yayin ɗaurin auren. Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya Rahotanni sun bayyana cewa, an ɗaura auren ne akan sadaki Naira 10,000, ba tare da amincewar iyayen ma’auratan ba. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, mataimakin babban kwamandan hukumar ta Hisbah, Dr. Mujaheeddeen Aminuddeen, ya ce an kama wadanda ake zargin ne biyo bayan korafe-korafen da ‘yan unguwar suka kai wa hukumar. Ya bayyana cewa, matakin da wadanda ake zargin suka ɗauka ya saɓawa koyarwar addinin Musulunci da kuma dokokin aure na jihar, yana mai jaddada cewa, hukumar ta Hisbah ba za ta amince da duk wani abu da ya saɓawa tsarin addini da na shari’a a jihar Kano ba. Dr. Aminudeen ya kara da cewa, a halin yanzu wadanda aka kama suna hannun Hisbah domin ci gaba da bincike. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025 Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025 Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara