Gwamnati za ta fara farautar masu takardun bogi a wajen aiki a wat
Published: 25th, September 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta umarci dukkanin ma’aikatu, hukumomi, sojoji da kuma cibiyoyin kuɗi da ma’aikatu masu zaman kansu da su fara tantance takardun shaidar kammala makaranta na ma’aikatansu daga ranar 6 ga watan Oktoba, 2025.
Wannan mataki ya biyo bayan yawaitar bogi da takardun karatu na bogi a Najeriya.
Za a yi tantancewar ne ta hanyar tsarin amfani da kwamfuta mai suna Nigeria Education Repository and Databank (NERD), wanda aka ƙirƙiro domin adanawa da tabbatar da sahihancin takardun karatun ma’aikata.
A wannan tsari, babu wanda za a ɗauka aiki ko a tabbatar masa da muƙami sai an tabbatar da takardunsa ta hanyar National Credential Verification Service (NCVS).
Kowace takarda da aka tabbatar za a ba ta wata lamba ta musamman mai tsaro.
Jami’ai sun ce wannan mataki zai kare mutuncin ilimi a Najeriya, kodayake masana sun yi gargaɗin cewa wasu za su iya rasa ayyukansu.
A baya, an gano ’yan Najeriya da dama suna amfani da takardun bogi don samun aiki ko ƙarin matsayi a wajen aiki.
A shekarar 2024, gwamnati ta soke takardun shaidar kammala karatu sama da 22,000 daga jami’o’in bogi na Jamhuriyar Benin da Togo.
Haka kuma, gwamnati ta umarci cibiyoyi su riƙa gabatar da rahoton bin doka duk shekara domin tabbatar da tsauraran matakai.
Wannan zai sa ya zama da wuya a riƙa yin amfani da takardun ƙarya ba tare da an gano su ba.
Masana ilimi sun ce idan aka aiwatar da tsarin yadda ya kamata, zai dawo da mutuncin takardun shaidar kammala karatu na Najeriya a idon duniya, tare da bai wa ɗalibai na gari damar samun aiki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Takardun bogi Takardun Shaidar Kammala Karatu Tantancewa da takardun
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi
Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya caccaki matakin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta dauka na fara yajin aiki na tsawon makonni biyu, yana mai bayyana matakin a matsayin wanda bai kamata ba kuma bai dace ba ganin irin kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na biyan kusan dukkanin bukatun kungiyar. Da yake magana a wani shiri na gidan Talabijin na Channels, ‘The Morning Brief’ a ranar Litinin, Alausa ya bayyana rashin jin dadinsa da matakin da ASUU ta dauka na tsunduma yajin aiki duk da kokarin da gwamnatin ke yi akansu. “A cikin shekaru biyun da suka gabata, babu wani batun yajin aikin ASUU, saboda kokarin da gwamnati ke yi akan biyan duk bukatunsu. “A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, ni da mataimakin shugaban kwamitin tattaunawa na gwamnatin tarayya, mun tattauna da ASUU, zan iya gaya muku a yau, a zahiri, an biya kusan dukkan bukatun ASUU, don haka ban ga dalilin da ya sa ASUU ta fara yajin aikin ba.” In ji Ministan ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano October 13, 2025
Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025
Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025