Aminiya:
2025-11-27@21:14:25 GMT

Gwamnati za ta fara farautar masu takardun bogi a wajen aiki a wat

Published: 25th, September 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta umarci dukkanin ma’aikatu, hukumomi, sojoji da kuma cibiyoyin kuɗi da ma’aikatu masu zaman kansu da su fara tantance takardun shaidar kammala makaranta na ma’aikatansu daga ranar 6 ga watan Oktoba, 2025.

Wannan mataki ya biyo bayan yawaitar bogi da takardun karatu na bogi a Najeriya.

Shugaban EFCC ya bayyana a Aso Rock yayin da Tinubu ya gana da Ibas NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Suke Sa Dalibai Cin NECO Fiye da WAEC

Za a yi tantancewar ne ta hanyar tsarin amfani da kwamfuta mai suna Nigeria Education Repository and Databank (NERD), wanda aka ƙirƙiro domin adanawa da tabbatar da sahihancin takardun karatun ma’aikata.

A wannan tsari, babu wanda za a ɗauka aiki ko a tabbatar masa da muƙami sai an tabbatar da takardunsa ta hanyar National Credential Verification Service (NCVS).

Kowace takarda da aka tabbatar za a ba ta wata lamba ta musamman mai tsaro.

Jami’ai sun ce wannan mataki zai kare mutuncin ilimi a Najeriya, kodayake masana sun yi gargaɗin cewa wasu za su iya rasa ayyukansu.

A baya, an gano ’yan Najeriya da dama suna amfani da takardun bogi don samun aiki ko ƙarin matsayi a wajen aiki.

A shekarar 2024, gwamnati ta soke takardun shaidar kammala karatu sama da 22,000 daga jami’o’in bogi na Jamhuriyar Benin da Togo.

Haka kuma, gwamnati ta umarci cibiyoyi su riƙa gabatar da rahoton bin doka duk shekara domin tabbatar da tsauraran matakai.

Wannan zai sa ya zama da wuya a riƙa yin amfani da takardun ƙarya ba tare da an gano su ba.

Masana ilimi sun ce idan aka aiwatar da tsarin yadda ya kamata, zai dawo da mutuncin takardun shaidar kammala karatu na Najeriya a idon duniya, tare da bai wa ɗalibai na gari damar samun aiki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Takardun bogi Takardun Shaidar Kammala Karatu Tantancewa da takardun

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki

Shugaban Iran ya sanar da cewa gwamnati na aiki don inganta juriya da ingancin tattalin arzikin kasar.

Masoud Pezeshkian, Shugaban Iran, ya yi jawabi a taron Kasuwar Jarin Iran na shekara-shekara mai taken “Juriya, Kirkire-kirkire, Ci gaba,” yana mai jaddada gyare-gyaren manufofin tattalin arziki, kula da albarkatu, da kuma tallafawa masu zuba jari. Ya bayyana cewa gwamnati na aiki don rage cikas ga samar da kayayyaki da ciniki.

Pezeshkian ya nuna muhimmancin yin tarurruka na wata-wata tare da masu zuba jari da masu samar da kayayyaki don nemo hanyoyin magance matsalolin da ake fuskanta.

Ya kara da cewa, “Tanadin kashi 10% na iya adana ganga 800,000 zuwa 900,000 na mai a kowace rana.” Ya kuma nuna cewa samar da wutar lantarki daga hanyoyin da ake sabuntawa ya karu sosai kuma ya tabbatar da cewa gwamnati ta shirya tsaf don biyan bukatun makamashi a lokacin hunturu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah November 26, 2025 UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon November 26, 2025 Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta