Gwamnati Za Ta Ci Gaba Da Inganta Lafiya A Jihar Sakkwato
Published: 25th, September 2025 GMT
Gwamnatin jihar Sokoto ta ce za ta ci gaba da jajircewa wajen inganta fannin kiwon lafiya a jihar.
Mataimakin gwamnan jihar Alhaji Idris Mohamed Gobir ya bayyana cewa yayin da ya karbi bakuncin sabuwar wakiliyar Unicef ta kasa Mrs Wafaa Sa’eed da ta kai ziyarar fahimtar da jihar.
Alhaji Idris Gobir ya ce a kan haka ne bangaren ke samun mafi yawan kasafin kudi tun hawan gwamnatin mai ci.
A wata sanarwa da Daraktan hulda da manema labarai (Mataimakin Gwamnan) Garba Muhammed ya raba wa manema labarai, Mataimakin Gwamnan ya ce manufar ita ce a tabbatar da cewa mutane suna samun ayyukan kiwon lafiya cikin sauki.
Ya kuma nuna jin dadinsa da tallafin daban-daban da gwamnatin jihar ke samu daga Unicef domin inganta fannin lafiya.
Alhaji Idris Gobir ya bada tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da bayar da duk wani goyon bayan da Unicef ke bukata domin gudanar da ayyukansu cikin kwanciyar hankali a jihar.
Tun da farko, sabuwar wakiliyar kasar Misis Wafaa Sa’eed ta ce ayyukan Unicef sun shafi jin dadin mutane musamman yara a duniya.
Misis Wafaa Sa’eed ta sanar da cewa Unicef za ta taimaka wa yara marasa galihu 18,000 a shirin inshorar lafiya a jihar.
Ta ci gaba da cewa Asusun ya samar da wayoyin hannu guda 200 da kuma abin caji wato Power Bank da kuma Kwamfutar laptop 3 na rijistar zamantakewa a jihar.
Wakilin Unicef na kasa tare da rakiyar sabon mataimakin wakilin kasar mai kula da ayyuka Mista Charles Opikoli Lolika ya bayyana jin dadinsa tare da hadin gwiwar da asusun ke samu daga gwamnatin jihar tare da fatan za a dore.
REL/MUSTAPHA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato gwamnatin jihar
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya ASUU a ranar Lahadi ta sanar da shiga yajin aiki na makonni biyu, wanda zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, a duka jami’o’in gwamnati na ƙasar.
Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.
Asuu ta ce yajin aikin na gargaɗi ne bayan cikar wa’adin da suka bai wa gwamnatin Najeriya a watan Satumban da ya gabata.
“Yajin aikin gargadin zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, kamar yadda aka amince a taron NEC na ƙarshe,” kamar yadda Piwuna ya bayyana.
RN