Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Mutane Sun Yaba Da Gina “Tsarin Xinjiang” A Turbar Zamanantarwar Kasar Sin
Published: 25th, September 2025 GMT
Yayin da ake cika shekaru 70 da kafuwar yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa a bana, CGTN ta gudanar da wani bincike na kuri’ar jin ra’ayoyi a duniya a kwanan baya tsakanin mutane 7,446 daga kasashe 38. Sakamakon binciken ya nuna cewa masu bayyana ra’ayoyinsu sun yaba da nasarorin da aka samu a ci gaban tattalin arziki da zamantakewar yankin na Xinjiang.
A cikin binciken kuma, masu bayyana ra’ayoyi sun bayyana kalamai masu dadi game da nasarorin tattalin arziki na Xinjiang, tare da la’akari da manyan nasarori biyar da aka cimma wadanda su ne: ci gaba da inganta kiwon lafiya (da kashi 82.1), da tabbatar da damar samun ilimi ga jama’a (da kashi 81.7), da ci gaba da inganta ayyukan ababen more rayuwa (da kashi 80.8), da kuma samun babban sakamako wajen kare muhalli da gudanar da mulki (da kashi 80.6), kana da karuwar samun kudaden shiga na jama’a (da kashi 80). (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
Kwamitin da ke kula da tsare-tsare da manufofin kuɗi na Babban Bankin Najeriya (CBN) ya zaftare maki 60 daga nauyin kuɗin ruwa da ke kan masu karɓar basussuka.
Wannan dai shi ne karo na farko cikin shekaru biyar da aka samu babban bankin ya yi rangwamin kuɗin ruwa a ƙasar.
CBN ɗin ya ce kwamitin a wannan Talatar ya rage yawan kuɗin ruwan daga kashi 27.5 da yake karɓa a baya zuwa kashi 27 a yanzu.
Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a Taraba An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar FilatoGwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai bayan kammala taron kwamitin karo na 302 da ya gudana a Abuja.
Cardoso, ya bayyana cewa an kuma mayar da buƙatar adana tsabar kuɗi a manyan bankuna zuwa kashi 45 cikin ɗari, yayin da na bankunan ’yan kasuwa aka bar shi a kashi 16 cikin ɗari.
Haka kuma, Babban Bankin ya ƙaddamar da matakin sanya kashi 75 cikin ɗari na tsabar kuɗin da aka adana mallakin ma’aikatu da hukumomin gwamnati da ba sa cikin asusun gwamnati na bai-ɗaya wato TSA.
Cardoso ya bayyana cewa wannan mataki na kwamitin na zuwa ne bayan sauƙin da aka fara gani a farashin kayayyakin a ’yan kwanakin nan.