Yayin da ake cika shekaru 70 da kafuwar yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa a bana, CGTN ta gudanar da wani bincike na kuri’ar jin ra’ayoyi a duniya a kwanan baya tsakanin mutane 7,446 daga kasashe 38. Sakamakon binciken ya nuna cewa masu bayyana ra’ayoyinsu sun yaba da nasarorin da aka samu a ci gaban tattalin arziki da zamantakewar yankin na Xinjiang.

An amince sosai da cewa, tsarin gudanar da mulkin Xinjiang da kasar Sin ta yi amfani da shi ya gano hanyar da ta dace wajen daidaita ci gaba da bangaren tsaro a yankunan kan iyaka, da kara kaimi ga amfani da zamanantarwar kasar Sin a yankin Xinjiang, da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a yankin.

A cikin binciken kuma, masu bayyana ra’ayoyi sun bayyana kalamai masu dadi game da nasarorin tattalin arziki na Xinjiang, tare da la’akari da manyan nasarori biyar da aka cimma wadanda su ne: ci gaba da inganta kiwon lafiya (da kashi 82.1), da tabbatar da damar samun ilimi ga jama’a (da kashi 81.7), da ci gaba da inganta ayyukan ababen more rayuwa (da kashi 80.8), da kuma samun babban sakamako wajen kare muhalli da gudanar da mulki (da kashi 80.6), kana da karuwar samun kudaden shiga na jama’a (da kashi 80). (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100

Kwamitin da ke kula da tsare-tsare da manufofin kuɗi na Babban Bankin Najeriya (CBN) ya zaftare maki 60 daga nauyin kuɗin ruwa da ke kan masu karɓar basussuka. 

Wannan dai shi ne karo na farko cikin shekaru biyar da aka samu babban bankin ya yi rangwamin kuɗin ruwa a ƙasar.

CBN ɗin ya ce kwamitin a wannan Talatar ya rage yawan kuɗin ruwan daga kashi 27.5 da yake karɓa a baya zuwa kashi 27 a yanzu.

Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a Taraba An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

Gwamnan Babban Bankin, Olayemi Cardoso, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai bayan kammala taron kwamitin karo na 302 da ya gudana a Abuja.

Cardoso, ya bayyana cewa an kuma mayar da buƙatar adana tsabar kuɗi a manyan bankuna zuwa kashi 45 cikin ɗari, yayin da na bankunan ’yan kasuwa aka bar shi a kashi 16 cikin ɗari.

Haka kuma, Babban Bankin ya ƙaddamar da matakin sanya kashi 75 cikin ɗari na tsabar kuɗin da aka adana mallakin ma’aikatu da hukumomin gwamnati da ba sa cikin asusun gwamnati na bai-ɗaya wato TSA.

Cardoso ya bayyana cewa wannan mataki na kwamitin na zuwa ne bayan sauƙin da aka fara gani a farashin kayayyakin a ’yan kwanakin nan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Batun Gina Yankin Xinjiang Na Zamani Mai Ra’ayin Gurguzu
  • Xinjiang A Shekaru 70: Yadda Yankin Ya Habaka Da Aikin Noma
  • Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995