‘Yan Sandan Kano Sun Kama Mutane 78 Da Ake Zargi Da Safarar Miyagun Kwayoyi
Published: 25th, September 2025 GMT
A wani samame na kwanaki hudu na hadin gwiwa na yakar shaye-shayen miyagun kwayoyi da tashe-tashen hankula a kan tituna, rundunar hadin guiwa mai wanzar da zaman lafiya da farfado da matasa ta jihar Kano, ta kama wasu mutane 78 da ake zargi a manyan wuraren da ke jihar.
A wata sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na hukumar NDLEA a Kano Sadiq Mohammad Maigatari ya fitar, ya ce rundunar ta yi aiki tare da hadin gwiwar hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA da kuma rundunar ‘yan sandan Najeriya.
Wannan farmakin dai ya shafi fitattun wuraren da ake aikata miyagun laifuka da suka hada da Mariri Yan’itace, Fagge, Badawa, Masallacin Idi, da Kofar Mata. Sauran wurare kamar su Kwalejin Rumfa, Makabartar Dan’agundi, da Kofar Wambai an kai sumame. Jami’ai sun tabbatar da cewa 60 daga cikin wadanda aka kama suna da alaka kai tsaye da laifukan da suka shafi muggan kwayoyi ko ayyukan ‘yan daba.
Sanarwar ta yi bayanin cewa an gano wasu haramtattun abubuwa yayin da ake share su, wadanda suka hada da wiwi, Diazepam, Exol-5, Pregabalin, maganin roba, da cakudar titinan gida da ake kira “Suck and Die.” Mahukunta sun ce kamun ya nuna yadda ake samun karuwar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasan Kano.
Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata wanda ya jagoranci aikin, ya ce gwamnati na ci gaba da jajircewa wajen ganin ta kawar da shaye-shayen miyagun kwayoyi da tashe-tashen hankula tsakanin matasa. “Za mu ci gaba da aiki don ganin an gurfanar da wadanda ke da hannu a gaban shari’a tare da magance tushen abubuwan ta hanyar gyarawa da ilimi.”
Kwamandan NDLEA ACGN A.I. Ahmad ya yaba da kokarin da aka yi tare kuma ya bukaci jama’a da su goyi bayan kokarin aiwatar da ayyukan da ake yi.
Ya kuma jaddada mahimmancin shigar da al’umma domin samar da jihar Kano mai zaman lafiya, ba ta da miyagun kwayoyi.
Abdullahi Jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: miyagun kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
Aƙalla mutane biyu ne suka mutu a rikicin da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a unguwar Dambo, wani kauye da ke da tazarar ’yan kilomita daga Birnin Kebbi, babban birnin Jihar Kebbi.
Wani mazaunin yankin mai suna Ɗanladi Usman ya ce rikicin ya fara ne bayan an kashe wani mutum mai suna Sule yayin da yake aiki a gonarsa.
“Kashe Sule ya tayar da hankulan al’umma, inda manoma suka ɗauki fansa suka kashe wani makiyayi da har yanzu ba a gano sunansa ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa makiyayan sun sha faɗa da manoma a kwanakin baya bayan sun aike musu da sako cewa su hanzarta girbe amfanin gonakinsu domin za su riƙa wucewa da shanunsu ta gonakin nan ba da daɗewa ba.
An yi jana’izar sojojin da ’yan bindiga suka kashe a Kebbi Rashin wutar lantarki ya rusa harkoki a Kaduna, Kano da Katsina“A lokacin da wasu manoma suka je gonakinsu domin yin aiki, sai makiyaya suka kai musu hari, daga nan ne aka shiga tashin hankali,” in ji shi.
Wani mazaunin yankin, Abubakar Aliyu, ya roƙi gwamnati da ta kawo ƙarshen wannan rikici na dogon lokaci tsakanin manoma da makiyaya.
“Wannan matsala ba sabuwa ba ce, kuma sarakunan gargajiya sun san da ita. Muna fatan a samu adalci ga waɗanda abin ya shafa, kuma gwamnati ta kawo ƙarshen wannan rikici,” in ji shi.
Rundunar ’yan sanda a jihar ba ta tabbatar da faruwar lamarin ba domin jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Nafiu Abubakar, ba a iya samun sa a waya ba lokacin da ake haɗa wannan rahoto.