Aminiya:
2025-09-24@21:14:49 GMT

Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe

Published: 24th, September 2025 GMT

An kammala shirin gudanar da taron lafiya karo na farko a tarihin Jihar Gombe, wanda za a fara a ranar 2 ga Oktoba.

Da yake zantawa da manema labarai wannan Larabar a Gombe, Kwamishinan Lafiya, Dakta Habu Dahiru, ya bayyana cewa, za a gudanar da taron na tsawon kwanaki biyu domin tattauna matsalolin bangaren lafiya da zummar samo mafita.

An sake raba Naira biliyan 5 haƙƙoƙin ’yan fansho a Kano Komawar Natasha majalisa ya nuna haɗin kai zai iya yaƙar rashin adalci — Atiku

Ya ce, taron zai samu halartar manyan baki ciki har da Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu; Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Hajiya Amina Mohammed; Ministan Lafiya, Farfesa Ali Pate; tare da wasu abokan hulda, ‘yan majalisar tarayya, masana harkar lafiya, kungiyoyin farar hula da kuma kafafen yaɗa labarai.

Dakta Dahiru ya ƙara da cewa, a yayin taron, gwamnati za ta ƙaddamar da cibiyar kiran gaggawa ta lafiya da kuma tura motocin daukar marasa lafiya (ambulance), domin ba da agaji cikin gaggawa a dukkan sassan jihar.

A cewarsa, wannan sabon tsarin zai bai wa jama’a damar kiran hukumomin lafiya cikin sauri domin daukar marasa lafiya zuwa asibiti ba tare da bata lokaci ba.

“Wannan shiri zai sauya tsarin ba da agajin gaggawa a Gombe, kuma taron alama ce ta sabon babi a yunƙurin gwamnati na inganta harkokin lafiya a jihar,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Ali Pate jihar Gombe Kiwon Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja

Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa a yayin da take guje wa harin ’yan bindiga a kauyen Allawa da ke Karamar Hukumar Shiroro a Jihar Neja.

Sarkin yankin Bassa, Bagudu Amos, ne ya bayyana hakan a lokacin taron tattaunawa da mata kan zaman lafiya da kare su daga cin zarafi, mai taken: “Ƙarfafa kariya daga cin zarafin jima’i da na jinsi a Jihar Neja.”

Kungiyar Tunani Initiative, tare da goyon bayan Dorothy Njemanze Foundation da Ford Foundation, ce ta shirya taron domin ƙarfafa mata wajen yaki da cin zarafi da ke ƙara ta’azzara a sakamakon rashin tsaro.

Bagudu Amos ya bayyana cewa mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa a kafa da jaririn a bayanta domin tserewa daga harin ’yan bindiga, amma daga bisani ta gano cewa jaririn ya riga ya mutu a bayanta.

Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Ya ce lamarin da ya faru a shekarar 2023, na ɗaya daga cikin dimbin abubuwan firgici da mata ’yan gudun hijira ke fuskanta a kullum, inda mafi yawansu ba su da isasshen tallafi ko ƙarfafa gwiwa wajen yaki da cin zarafin jinsi da ke biyo bayan matsalar tsaro.

Shugabar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta nuna damuwarta kan yadda ba a ba wa mata muhimmanci da ya dace wajen shiga cikin harkar sasanta rikice-rikice da zaman lafiya a Jihar Neja. Ta yi kira ga mata da su haɗa kai domin karya shingayen da ke hana su shiga harkokin warware rikice-rikice.

“A Jihar Neja, kamar yadda ake gani a wasu wuraren da ke fama da rashin tsaro, mata su ne mafiya fuskantar ƙuncin hare-haren ’yan bindiga. Idan an kai hari, mafi yawanci maza ake kashewa, sai a bar mata da nauyin sake gina iyali daga farko. Wannan rawar da mata ke takawa ba a ba shi muhimmancin da ya kamata. Wannan shi ne dalilin da ya sa taron ya mayar da hankali kan ƙara bayyana muhimmancin mata a harkar zaman lafiya da kuma yaki da cin zarafi,” in ji ta.

Daraktan Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam a Jihar Neja, Ambasada Nuhu Muhammad, ya jaddada muhimmancin samun karin mata a majalisar dokokin jiha da ma ta ƙasa domin samar da dokoki da manufofi da za su amfanar da su.

Mata da suka halarci taron sun yi kira da a tsaurara hukunci kan masu yi wa mata fyade, tare da kira da a haɗa ƙarfi da ƙarfafa juna wajen shawo kan yawaitar cin zarafi musamman a ƙauyuka.

Mahalarta sun kuma jaddada muhimmancin kafa ƙungiyar mata mai ƙarfi guda ɗaya domin tunkarar matsalar cin zarafin mata a Jihar Neja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Li Qiang: Sin Ba Za Ta Nemi Sabon Matsayi Ko Fifiko A Yayin Tattaunawa Karkashin WTO Ba
  • Saudiyya Ta Naɗa Sabon Mufti
  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80