Aminiya:
2025-11-09@04:27:15 GMT

Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe

Published: 24th, September 2025 GMT

An kammala shirin gudanar da taron lafiya karo na farko a tarihin Jihar Gombe, wanda za a fara a ranar 2 ga Oktoba.

Da yake zantawa da manema labarai wannan Larabar a Gombe, Kwamishinan Lafiya, Dakta Habu Dahiru, ya bayyana cewa, za a gudanar da taron na tsawon kwanaki biyu domin tattauna matsalolin bangaren lafiya da zummar samo mafita.

An sake raba Naira biliyan 5 haƙƙoƙin ’yan fansho a Kano Komawar Natasha majalisa ya nuna haɗin kai zai iya yaƙar rashin adalci — Atiku

Ya ce, taron zai samu halartar manyan baki ciki har da Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu; Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Hajiya Amina Mohammed; Ministan Lafiya, Farfesa Ali Pate; tare da wasu abokan hulda, ‘yan majalisar tarayya, masana harkar lafiya, kungiyoyin farar hula da kuma kafafen yaɗa labarai.

Dakta Dahiru ya ƙara da cewa, a yayin taron, gwamnati za ta ƙaddamar da cibiyar kiran gaggawa ta lafiya da kuma tura motocin daukar marasa lafiya (ambulance), domin ba da agaji cikin gaggawa a dukkan sassan jihar.

A cewarsa, wannan sabon tsarin zai bai wa jama’a damar kiran hukumomin lafiya cikin sauri domin daukar marasa lafiya zuwa asibiti ba tare da bata lokaci ba.

“Wannan shiri zai sauya tsarin ba da agajin gaggawa a Gombe, kuma taron alama ce ta sabon babi a yunƙurin gwamnati na inganta harkokin lafiya a jihar,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Ali Pate jihar Gombe Kiwon Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

Kwamishinan lafiya na Jihar Adamawa, Dokta Felix Tangwami ya bayyana cewa, cutar kwalara a Ƙaramar hukumar Mubi ta yi sanadin mutuwar mutane 10, inda ya buƙaci mazauna yankin da su kula da tsaftar jikinsu.

Da yake yi wa Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) bayani a Yola ranar Laraba, Tangwami ya ce marasa lafiyan sun mutu ne a gida maimakon a cibiyoyin lafiya.

Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita

Ya ƙara da cewa, gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumar lafiya ta duniya (WHO) sun ɗauki matakin gaggawa don daƙile ɓarkewar cutar.

“Tun daga farko, mun ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin, kasancewar mu a can, kuma ba za a iya musanta hakan ba,” in ji shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, waɗanda suka ziyarci cibiyoyin kiwon lafiya sun samu kulawa, inda aka kwantar da majinyata 25 a ranar Talata 4 ga watan Nuwamba, yayin da wasu da dama kuma an sallame su tare da wayar da su kan harkokin tsafta.

Ya bayyana cewa, an tura jami’an kula da cututtuka na jihar, da Daraktan kula da cututtuka a Hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko, da masu aikin sa-kai zuwa Mubi domin gudanar da ayyuka da kuma wayar da kan jama’a.

Sun kuma gano waɗanda abin ya shafa a cikin unguwanni don tabbatar da sun samu kulawar lafiya.

Tangwami ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya da su goyi bayan ƙoƙarin gwamnati ta hanyar ƙarfafa gwiwar mazauna yankin da su gaggauta neman magani a cibiyoyin lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Genoa ta naɗa Daniele De Rossi sabon kociya
  • Ajax ta kori kocinta John Heitinga
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa