Aminiya:
2025-09-24@21:46:44 GMT

Siyasa ba ta yiwuwa da rowa — Gwamna Buni

Published: 24th, September 2025 GMT

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya shawarci matasa da ‘yan siyasa masu tasowa da su fahimci cewa siyasa ba ta tafiya da rowa, illa da juriya, sadaukarwa da biyayya.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin rantsar da sabon Alƙalin Alƙalai na jihar (Grand Khadi), tare da wasu mashawartarsa na musamman, mamba na dindindin a hukumar SUBEB da kuma sabbin sakatarorin dindindin guda 13, a wani taro da aka gudanar a babban ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Damaturu.

Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe An sake raba Naira biliyan 5 haƙƙoƙin ’yan fansho a Kano

A jawabinsa, Buni ya ce matasa da ‘yan siyasa masu neman makoma a fagen shugabanci dole ne su kasance masu haƙuri, biyayya da ƙwarewa tare da ɗa’a, domin samun ci gaba.

“Siyasa aiki ne na haƙuri, biyayya da sadaukarwa. Ba za a cimma nasara da rowa ko gaggawa ba. Idan matasa suka rungumi juriya, gobe su ma za su zama shugabanni a matakai daban-daban,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa siyasa tana buƙatar haɗin kai, fahimta da tsayin daka wajen bauta wa al’umma, ba don amfanin kai kaɗai ba, lamarin da ya ce shi ne ginshiƙin da ya kamata kowane ɗan siyasa ya ɗora kansa a kai.

Gwamnan ya kuma ja hankalin sabbin jami’an da aka rantsar da su kasance masu gaskiya, nagarta da aiki tuƙuru wajen tabbatar da nagartaccen tsarin mulki a Jihar Yobe.

“Aikin da aka ba ku nauyi ne daga Allah da kuma al’umma. Ku tabbatar da gaskiya, aminci da sadaukarwa, domin idan kuka yi haka, za ku bar tarihi mai kyau a Jihar Yobe,” in ji shi.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, malamai da dimbin jama’a daga sassa daban-daban na jihar, inda aka yaba wa Gwamna Buni bisa namijin ƙoƙarinsa na gina al’umma mai dogaro da kai da kuma inganta shugabanci nagari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta ce a karon farko za ta shirya taron zuba jari da samar da masana’antu na Arewacin Najeriya, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 29 da 30 ga watan Satumba a Abuja.

Taron wanda aka shirya tare da hadin gwiwar jihohin arewa 19 da kuma kamfanin raya yankin – NNDC, na da nufin mayar da yankin a matsayin wata cibiya ta samun bunkasar tattalin arziki da habaka masana’antu.

An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI

Da yake magana a taron manema labarai da aka gudanar ranar Litinin a Abuja, kakakin kungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya bayyana taron a matsayin “kira domin zaburar da tattalin arziki da kuma tsare-tsare na cika alkawarin Arewacin Najeriya.”

Ya ce an tsara taron ne a cikin watanni 18 da suka gabata domin kaddamar da wani shiri na kishin kasa wanda zai karfafa ayyukan ci gaba da bude sabbin kafofin damammanki ga yankin, Najeriya da abokan huldar kasa da kasa.

“Wannan taron ba na siyasa ba ne, yana mai da hankali kan tattalin arziki, kan damammaki, da kuma samar da wadata. Yana da zimmar nuna karfin Arewacin Najeriya da kuma gabatar da hangen nesa na ci gaba, kirkire-kirkire, da haɗin gwiwa. Daga yau, za mu bude sabon babi,” in ji Jiddere.

Da yake yin la’akari da irin gudunmawar da yankin ya bayar a tarihi, ya tuna cewa a shekarun 1960 zuwa farkon 1980, Arewacin Nijeriya ya ba da karfin tattalin arzikin kasa ta hanyar noma, masana’antu, da kasuwanci. “Dalarmu na gyada ya kai sararin sama; auduga, fatu, dabbobi, da ma’adanai masu ƙarfi suna tallafawa masana’antu,” in ji shi.

Duk da haka, ya ce rashin tsaro da rashin zuba jari sun rage ci gaban yankin, wanda ya haifar da rikice-rikice na albarkatu masu yawa da kuma abubuwan da ba a san su ba, “Wannan taron yana manufa juya akalar rikicin zuwa ga damammaki da kuma tabbatar da cewa Arewacin Najeriya ya samu kwarin gwiwa zuwa wani sabon zamani na ci gaba,” in ji shi.

Jiddere ya zayyana ginshiƙai masu mahimmanci guda biyar da yankin yake tutiya da su kamar albarkar ƙasa da noma, manyan ma’adanai, albarkatun ɗan adam, ababen more rayuwa, da masana’antu, waɗanda ke samun tallafi kamar ilimi, kiwon lafiya, gidaje, da fasaha.

Ya nanata cewa Arewacin Najeriya “yana da alaƙa da kasa-wata babbar hanyar shiga Nijar, Chadi, Kamaru, Benin, Mali, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.”

Ya ƙalubalanci masu ruwa da tsaki da su yi nazari a kan abubuwan da ba za a iya amfani da su a yankin ba, yana mai tambaya, “Ta yaya yankin da ya samar da shugabanni da masu ƙirkire-ƙirkire a duniya, ’yan ƙato da gora irin su Alhaji Aliko Dangote da Amina Mohammed, har yanzu bai nuna cikakken ƙarfin tattalin arzikinsa ba?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC