Aminiya:
2025-11-27@21:48:47 GMT

Siyasa ba ta yiwuwa da rowa — Gwamna Buni

Published: 24th, September 2025 GMT

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya shawarci matasa da ‘yan siyasa masu tasowa da su fahimci cewa siyasa ba ta tafiya da rowa, illa da juriya, sadaukarwa da biyayya.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin rantsar da sabon Alƙalin Alƙalai na jihar (Grand Khadi), tare da wasu mashawartarsa na musamman, mamba na dindindin a hukumar SUBEB da kuma sabbin sakatarorin dindindin guda 13, a wani taro da aka gudanar a babban ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Damaturu.

Za a gudanar da taron kiwon lafiya na farko a Gombe An sake raba Naira biliyan 5 haƙƙoƙin ’yan fansho a Kano

A jawabinsa, Buni ya ce matasa da ‘yan siyasa masu neman makoma a fagen shugabanci dole ne su kasance masu haƙuri, biyayya da ƙwarewa tare da ɗa’a, domin samun ci gaba.

“Siyasa aiki ne na haƙuri, biyayya da sadaukarwa. Ba za a cimma nasara da rowa ko gaggawa ba. Idan matasa suka rungumi juriya, gobe su ma za su zama shugabanni a matakai daban-daban,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa siyasa tana buƙatar haɗin kai, fahimta da tsayin daka wajen bauta wa al’umma, ba don amfanin kai kaɗai ba, lamarin da ya ce shi ne ginshiƙin da ya kamata kowane ɗan siyasa ya ɗora kansa a kai.

Gwamnan ya kuma ja hankalin sabbin jami’an da aka rantsar da su kasance masu gaskiya, nagarta da aiki tuƙuru wajen tabbatar da nagartaccen tsarin mulki a Jihar Yobe.

“Aikin da aka ba ku nauyi ne daga Allah da kuma al’umma. Ku tabbatar da gaskiya, aminci da sadaukarwa, domin idan kuka yi haka, za ku bar tarihi mai kyau a Jihar Yobe,” in ji shi.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, sarakunan gargajiya, malamai da dimbin jama’a daga sassa daban-daban na jihar, inda aka yaba wa Gwamna Buni bisa namijin ƙoƙarinsa na gina al’umma mai dogaro da kai da kuma inganta shugabanci nagari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya ce ko sisi gwamnati ba ta biya waɗanda suka yi garkuwa da ɗalibai mata 25 na sakandaren gwamnati ta Maga da ke jihar ba.

Ya bayyana hakan ne a taron manema labarai da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar a ranar Talata, inda ya tabbatar da kubutar da ɗaliban da aka sace a farkon makon nan.

Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi

Ya ce, “An karɓo ɗalibanmu da aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya ba jami’an tsaro umarni su gano inda yaran suke, kuma su kubutar da su. Muna tabbatar wa iyayen yara da al’ummar Kebbi cewa ’ya’yansu sun dawo lafiya.

“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro, musamman sojoji, ’yan sanda, da Civil Defence da suka yi aiki tukuru har aka kubutar da yaran cikin ƙoshin lafiya,” in ji Gwamnan.

Idris ya jaddada cewa gwamnatin Kebbi ba ta biya kuɗin fansa ba, “Mu, a matsayin gwamnati, ba mu ba da ko sisi ba. A binciken da muka yi, babu wanda ya biya kuɗin fansar yaran.”

A ranar Litinin din da ta gabata ce ’yqn bindiga suka sace ɗaliban su 25 daga makarantar bayan sun kashe mataimakin shugaban makarantar.

Sai dai daga bisani ɗaya daga cikin ɗaliban ta gudo ’yan kwanaki bayan sace su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi