Leadership News Hausa:
2025-09-24@23:58:53 GMT

Xi Ya Jaddada Batun Gina Yankin Xinjiang Na Zamani Mai Ra’ayin Gurguzu

Published: 25th, September 2025 GMT

Xi Ya Jaddada Batun Gina Yankin Xinjiang Na Zamani Mai Ra’ayin Gurguzu

A yau Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bukaci yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa da ya yi hobbasar gina Xinjiang na zamani mai ra’ayin gurguzu da ke kunshe da hadin kai, da kwanciyar hankali, da samun wadata, da arziki mai albarka, da raya al’adu da kyautata muhallin halittu, inda jama’a za su ci gaba da rayuwa da aiki cikin zaman lafiya da samun wadata.

Yayin da yake sauraren rahoton ayyukan kwamitin jam’iyyar JKS a yankin Xinjiang da gwamnatin yankin a yau 24 ga wata, shugaba Xi ya jaddada cewa, wajibi ne a kafa tubalin samar da albarkatu da masana’antu, da yin nazari sosai a game da turbar samar da ci gaba mai inganci da ta dace da sigogin yankin na Xinjiang.

Shugaban ya kara da cewa, ya kamata a bunkasa hade kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da kirkire-kirkiren masana’antu, da habaka sabbin ginshikan ayyuka masu fa’ida daidai da yanayin cikin gida. Kazalika, wajibi ne a karfafa hade sha’anin al’adu da yawon bude ido tare da inganta ci gaban masana’antar yawon shakatawa na bangaren al’adu. Kuma ya kamata a karfafa ba da kariya da maido da muhallin halittu da karfafa cikakkun sauye-sauyen samar da ci gaba mara gurbata muhalli da habaka tattalin arziki da zamantakewa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko su waye ba sun sace Hakimin Birbyang, Alhaji Zubairu Garba, tare da wasu mata biyu a daren Lahadi a ƙaramar hukumar Kanam ta Jihar Filato. Rahotanni sun ce ƴan bindigar sun shigo ƙauyen ne da tsakar dare, suna harbi a iska kafin daga bisani su yi awon gaba da mutanen. Matar hakimin, wadda aka yi garkuwa da ita a farkon harin, ta samu damar tserewa daga hannun masu garkuwa.

Wannan lamari na baya-bayan nan ya biyo bayan sace-shi-da-kashe wa da aka yi wa Dagacin Shuwaka a yankin Kyaram, wanda shi ma ke cikin ƙaramar hukumar Kanam, mako guda kacal da ya gabata. Hakan ya ƙara tayar da hankali a tsakanin al’ummar yankin kan yawaitar hare-haren ƴan bindiga.

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ƙungiyar Cigaban Kanam (KADA), ta bakin shugaban ta Shehu Kanam da sakataren ta, Barista Garba Aliyu, ta tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ta fitar ga manema labarai a Jos. Sun ce harin ya auku ne misalin ƙarfe 1 na dare, inda ƴan bindigar suka yi awon gaba da hakimin zuwa wani wuri da ba a sani ba. Sun kuma yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta ceto waɗanda aka sace tare da dawo da zaman lafiya a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa garkuwa da mutane da hare-haren ƴan bindiga sun zama ruwan dare a yankin Kanam, inda mafi yawan waɗanda aka sace ake neman kuɗin fansa, yayin da wasu kuma ake hallaka su. Sai dai Daily Trust ya rawaito cewa, kakakin rundunar ƴan sandan jihar Filato, DSP Alabo Alfred, bai amsa tambayar wakilinta ba a lokacin da ake rubuta wannan rahoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Mutane Sun Yaba Da Gina “Tsarin Xinjiang” A Turbar Zamanantarwar Kasar Sin 
  • Xinjiang A Shekaru 70: Yadda Yankin Ya Habaka Da Aikin Noma
  • Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Babban Taro Kan Shawarar Samar Da Ci Gaban Duniya
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Iran Da Rasha Zasu Rattaba Hannun Kan Batun Gina Wasu Tashoshin Nukiliya.
  • He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato