Wata takardar bayani da aka wallafa a yau Lahadi 18 ga watan Mayun shekarar 2024, ta nuna cewa, jimillar kudin da aka samu a masana’antar harkokin sadarwar tauraron dan Adam na kasar Sin ta kai yuan biliyan 575.8, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 79.9, a shekarar 2024, adadin da ya karu da kaso 7.39 cikin dari bisa na makamancin lokacin bara.

Takardar game da bunkasar masana’antar harkokin sadarwar tauraron dan Adam ta kasar Sin, ta yi nuni da cewa, a karshen shekarar 2024, yawan adadin manhajojin fasahar sadarwar tauraron dan Adam a kasar Sin ya zarce 129,000, kuma an sanya wa kusan wayoyin salula miliyan 288 a kasar tsarin da suke iya amfani da sadarwar daga tsarin amfani da tauraron dan Adam na BeiDou.

A matsayin tsarin sadarwa ta tauraron dan Adam na duniya da MDD ta amince da shi, tsarin BeiDou na kasar Sin ya shiga tsarin kungiyoyin kasa da kasa guda 11 ciki har da zirga-zirgar jiragen sama, da jiragen ruwa, da sadarwar wayar salula da sauransu, kana yana ci gaba da fadada yawan kasashe da yankuna masu amfani da shi a duniya.

A halin yanzu, kasashen Afirka fiye da 30 ciki har da Najeriya, da Tunisia, da Senegal da sauransu sun riga sun gina tasoshin CORS masu amfani da tsarin BeiDou.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tauraron dan Adam a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Yau Talata ita ce ranar cika shekaru 104 da kafuwar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS. A cikin lokacin sanyi na shekarar 2012, jama’ar kasar Sin sun wayi gari da ganin motocin gwamnati kalilan ne ke kai-komo a kan tituna, kuma an daina amfani da kudin gwamnati wajen shirya liyafar cin abinci a gidajen cin abinci masu tsada, kana hatta kyautar da ake bayarwa ta kek, watau “Mooncake” lokacin bikin tsakiyar kaka an rage girmanta daga dan karamin akwati zuwa wani karamin kunshi.

Wannan shi ne sauyin da aka samu bayan aiwatar da shahararrun “Ka’idoji Takwas” na jam’iyyar JKS. Matakin da aka dauka na dokoki ya zama tamkar wani magani mai karfi wanda ke warkad da “cututtukan” da suka zama matsaloli kamar “sharholiya da kudin gwamnati” wadanda ake ganin ba su taka-kara-sun karya ba amma kuma sannu a hankali suna zubar da kima da martabar jam’iyya mai mulki ta JKS.

Shekaru 13 bayan haka, a lokacin da aka koyar tare da ilmantar da rassan jam’iyyar a dukkan matakai na kasar Sin game da “Ka’idoji Takwas”, wadannan ka’idojin, wadanda tun farko sun mayar da hankali ne kan “magance cin hanci da rashawa tun daga tushe”. Sun tashi daga zama tsarin gina salon gudanar da aiki zuwa gawurtaccen tsarin tafiyar da shugabanci na jam’iyyar.

A karkashin wannan, babban sirrin JKS wajen samun bunkasa da kuma kiyaye nasarar da ta samu a cikin shekaru fiye da dari a tarihi, shi ne juyin juya halin da take yi wa kanta. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare
  • Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
  • Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce; Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ta Kasar Kan Hukumar IAEA Dole Ne Aiki Da Ita
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar