DRC: Kungiyar M23 Ta Kori Fararen Hula Zuwa Kasar Rwanda
Published: 18th, May 2025 GMT
Rahotanni daga kasar DRC sun ce a ranar Litinin din da ta gabata kungiyar ‘yan tawaye ta M23 ta kori fararen hula 181 daga garin Goma zuwa kasar Rwanda.
Kungiyar ta zargi fararen hular da ta kora da cewa, ba ‘yan kasa ba ne, asalinsu daga kasar Rwanda ne.
Bugu da kari an gabatar da wasu dubban mutane tare da iyalansu da ake daukar cewa masu laifi ne, da aka zuba su a cikin manyan motoci a yankin Karenga dake yankin Kivu ta arewa.
Mafi yawancin iyalan da aka dauka suna a yankin da yake karkashin ikon kungiyar ‘yan tawaye da Democratic Forces For Liberation of Rwanda ( FDLR).
Gwamnatin Rwanda da kuma kungiyar M23 suna zargin kungiyar FDLR da cewa, tana tafka laifuka a yankin da take rike da shi.
Rahotannin sun ambaci cewa, mafi yawancin wadanda aka kora din suna zaune ne a cikin hemomi na ‘yan hijira dake Sake, da ba shi da nisa sosai daga Goma.
Mai Magana da yawun hukumar ‘yan hijira ta MDD, ( UNHCR) Eujin Byun ta bayyana cewa; an mika mutane 360 zuwa kasar Rwanda a ranar Asabar din da ta gabata.
Ita dai kungiyar M23 wacce ta shimfida ikonta a mafi yawancin yankunan da suke gabashin DRC, tana samun cikakken goyon bayan Rwanda wacce ta aike mata da sojojin da sun kai 4000.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Rwanda
এছাড়াও পড়ুন:
Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
A taron kasashen larabawa karo na 34Th wanda ake gudanarwa a birnin Bagdaza na kasar Iraki, shuwagabannin kasashen larabawa sun bukaci tsagaita wuta a gaza sannan sun yi kira da aka kafa kasar Falasdinu mai zaman kanta.
Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa, shuwagabannin sun bukaci a magance matsalolin da suke faruwa a Siriya Lebanon da kuma sudan. Ana taron shuwagabannin kasashen larabwa a Bagdaza ne a dai dai lokacinda gwamnatin HKI take kara fadada hare-hare a kan zirin Gaza da kuma kashe Falasdinawa maza da mata da yara mutkar abinda zata iya kashewa.
Majiyar kiwon lafiya ta Gaza ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu sojojin HKI sun kashe falasdinawa kimani 53,272 mafi yawansu mata da yara, sannan wasu 120,673 kuma sun ji rauni . Ma’aikatar ta kara da cewa tun watan Marisa bayan da HKI ta sake komawa yaki a gaza ta kashe Falasdinawa 3131 sannan wasu 8,632 suka ji rauni.
A cikin bakin da suka sami halattar taron shuwagabannin kasashen larabawa karo na 34Th akwai babban sakataren MDD Antonio Gotteress kan cewa ana bukatar tsagaita wuta a gaza da gaggawa. Sai kuma Firai ministan kasar Espaniya Pedro Sanchez ya bukaci a takurawa HKI ta dakatar kisan kiyashi a gaza.
Shuwagabannin sun ki amincewa da duk wani shiri na fidda Falasdinawa a gaza ko kuma kasarsu, kamar yadda Trump ya fada a farkon wannan shekarar.
Har’ila yau firai ministan kasar Iraki Muhammad shi’a Assudani, ya ware dalar Amurka miliyon $20 don sake gina Gaza sannan wasu miliyon 20 don sake gina kasar Lebanon. Ministan harkokin wajen kasar Siriya ne ya wakilci kasar a taron na Bagdaza saboda matsin lambar da wasu yan siyasa a kasar Iraki suka yiwa firai ministan kasar kan kada ya bar Ahmes Sharaa ya taka kasar.