MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024
Published: 18th, May 2025 GMT
A wani rahoton da MDD ta fitar a cikin kwanakin nan, ya bayyana cewa, tun daga 2024 ne yunwar da ake fuskanta a duniya ta kara tsanani domin ta shafi mutanen da sun kai miliyan 295.
Rahoton ya kara da cewa; wannan adadin na mutanen dake fama da yunwa mai tsanani suna warwatse a cikin kasashe 53 na duniya.
A Juma’ar da ta gabata aka fitar da wannan rahoton. Haka nan kuma an bayyana cewa idan aka kwatanta da yunwar da aka yi fama da ita a shekarar 2023, to da aka shiga 2024 an sami karuwar masu fama da matsananciyar yunwar da adadinsu ya karu da miliyan 13.7. Shekaru shida kenan a jere da ake samun karuwar yawan mutanen da suke fama da yunwa.
An kaddamar da wannan rahoton ne a karkashin kawancen kasa da kasa na fada da karancin abinci a duniya wanda ake kira da ( GNAFC) wanda ya kunshi hukumar Abinci ta duniya ( FAO), da kuma ( WFP) da sauran kungiyoyin da ba na gwamnati ba.
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya bayyana alkaluman da aka fitar na adadin masu fama da matsananciyar yuwa da cewa; Wani adadi ne wanda bai girgiza duniya ba, domin tana tafiya ne a karkace.”
Wani sashe na rahoton ya yi ishara da cewa da akwai dalilai masu yawa da su ka haddasa karancin abinci; sun kuwa hada da talauci, koma bayan tattalin arziki, sauyin yanayi mai tsanani, sai dai kuma duk da haka rikice-rikice da fadace-fadace a cikin wasu yankuna, su ne ummul-haba’isin karancin abincin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025)
Sarkin Zuru, Alhaji Mohammed Sani Sami Gomo II, ya rasu a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, a wani asibiti da ke birnin London bayan gajeruwar rashin lafiya. Ya rasu yana da shekaru 82.
A cewar majiyoyin danginsa, ana sa ran za a kawo gawarsa daga London zuwa Najeriya nan da gobe (Litinin), domin gudanar da jana’iza.
Marigayin ya bar mata hudu, ’ya’ya bakwai da jikoki biyu.
Daya daga cikin masu rike da sarautar gargajiya a Zuru, Muhammed Abba Zuru, ya bayyana cewa iyalan marigayin na jiran isowar gawarsa daga London kafin a kammala shirye-shiryen jana’iza.
An haifi Mohammed Sani Sami a Zuru, Jihar Kebbi, a ranar 24 ga Oktoba, 1943. Ya shiga Rundunar Sojin Najeriya a ranar 10 ga Disamba, 1962, inda ya samu horo tare da Ibrahim Babangida.
Daga bisani ya halarci Mons Officer Cadet School da ke Aldershot, Ingila, inda ya zama hafsan soji a ranar 25 ga Yuli, 1963.
Ya halarci yakin basasa na Najeriya, kuma ya jagoranci dakarun da suka fatattaki sojojin Chadi da suka kutsa Jihar Borno.
A watan Yuli 1975, Janar Murtala Mohammed ya naɗa shi kwamandan Brigade of Guards a matsayin Lieutenant Colonel.
Bayan juyin mulkin 31 ga Disamba, 1983 wanda ya kawo Janar Muhammadu Buhari kan mulki, an naɗa Sani Sami a matsayin Gwamnan Soja na Jihar Bauchi.
Ya riƙe wannan muƙamin har zuwa watan Agusta 1985 lokacin da Janar Ibrahim Babangida ya karɓi mulki daga hannun Buhari.
A lokacin mulkinsa a Bauchi, ya inganta cibiyoyin lafiya tare da kaddamar da babban shirin noma mai taken “Back to Land.”
Haka kuma ya jagoranci shirya gasar cin kofin duniya ta wasan handball a jihar.
A watan Oktoba 1984, lokacin da ake fuskantar ƙaruwa na matsalolin addini, Sani Sami ya jaddada haramcin wa’azin addini a fili.
Ya kuma bayyana cewa rushe wasu coci-coci domin gina sabon ring road ba ya nufin hari ne kan addinin Kirista, tare da ƙara da cewa gwamnati ta ware fili domin Katolika su gina sabon coci.
Ya yi ritaya daga rundunar soji a matsayin Manjo Janar a ranar 3 ga Satumba, 1990. A shekarar 1995, aka naɗa shi Sarkin Zuru na 11, mukamin da ya riƙe har zuwa rasuwarsa.
Kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu na Jihar Kebbi, Alhaji Garba Umar-Dutsinmari, ya mika ta’aziyyar gwamnatin jihar ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Zuru, al’ummar Zuru da Jihar Kebbi baki ɗaya.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayin da Aljannah Firdausi, tare da bai wa iyalansa haƙuri da juriyar rashin.
Sanarwar ta ƙara da cewa ana ci gaba da shirye-shiryen jana’iza yayin da ake jiran isowar gawarsa daga London.