HausaTv:
2025-07-03@10:36:44 GMT

MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024

Published: 18th, May 2025 GMT

A wani rahoton da MDD ta fitar a cikin kwanakin nan, ya bayyana cewa, tun daga 2024 ne yunwar da ake fuskanta a duniya ta kara tsanani domin ta shafi mutanen da sun kai miliyan 295.

Rahoton  ya kara da cewa; wannan adadin na mutanen dake fama da yunwa mai tsanani suna warwatse a cikin kasashe 53 na duniya.

A  Juma’ar da ta gabata aka fitar da wannan rahoton. Haka nan kuma an bayyana cewa idan aka kwatanta da yunwar da aka yi fama da ita a shekarar 2023, to da aka shiga 2024 an sami karuwar masu fama da matsananciyar yunwar da adadinsu ya karu da  miliyan 13.7. Shekaru shida kenan a jere da ake samun karuwar yawan mutanen da suke fama da yunwa.

An kaddamar da wannan rahoton ne a karkashin kawancen kasa da kasa na fada da karancin abinci a duniya wanda ake kira da ( GNAFC) wanda ya kunshi hukumar Abinci ta duniya ( FAO), da kuma ( WFP) da sauran kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya bayyana alkaluman da aka fitar na adadin masu fama da matsananciyar yuwa da cewa; Wani adadi ne wanda bai girgiza duniya ba, domin tana tafiya ne a karkace.”

Wani sashe na rahoton ya yi ishara da cewa da akwai dalilai masu yawa da su ka haddasa  karancin abinci; sun kuwa hada da talauci, koma bayan tattalin arziki, sauyin yanayi mai tsanani, sai dai kuma duk da haka rikice-rikice da fadace-fadace a cikin wasu yankuna, su ne ummul-haba’isin karancin abincin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su

Shugaban hukumar kula da makarantun kiwon lafiya da bada lasisi ga likitoci kula da lafiya a matakin farko ta kasa Alhaji Dr Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya hori ma’aikatan kiwon lafiya a matakin farko da dukkannin masu ruwa da tsaki a bangaren lafiya su rubanya kokari fuskar tabbatar da kwarewa domin inganta ayyukan kula da lafiya a Nijeriya.

Dr. Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya yi wannan kiran ne a Katsina lokacin bukin rufe taron karawa juna sani na tsawon kwanaki uku na wannan shekarar wanda aka shiryawa Malaman koyar da darusan kiwon lafiya a matakin farko.

Taron wanda ya samu halartan jami’an kiwon lafiya daga dukkannin jihohin yankin arewa maso yamma, yana da nufin ilimintar dasu ne kan yadda za su rungumi sabbin dabarun aiki irin na zamani dai dai da tsarin dokokin hukumar kula da makarantun kiwon lafiya da bada lasisi ga likitocin kula da lafiya a matakin farko ta Naheriya.

Dr. Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya bayyana cewa wajibi ne dukkannin ma’aikatan hukumar da sauran masu ruwa da tsaki a bangaren lafiya a matakin farko su kara zama masu kwazo tare da yin aiki da sauran dokokin aiki na fasahohin zamani domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Don haka shugaban hukumar ya sake yin kira ga malarta taron su yi amfani da abubuwan da suka koya yadda suka dace domin bunkasa harkokin kiwon lafiya a Naheriya.

Maryam Idris

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149
  • Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19