HausaTv:
2025-10-13@17:49:56 GMT

MDD: Yunwa Ta Kara Tsanani A Duniya Daga Shekarar 2024

Published: 18th, May 2025 GMT

A wani rahoton da MDD ta fitar a cikin kwanakin nan, ya bayyana cewa, tun daga 2024 ne yunwar da ake fuskanta a duniya ta kara tsanani domin ta shafi mutanen da sun kai miliyan 295.

Rahoton  ya kara da cewa; wannan adadin na mutanen dake fama da yunwa mai tsanani suna warwatse a cikin kasashe 53 na duniya.

A  Juma’ar da ta gabata aka fitar da wannan rahoton. Haka nan kuma an bayyana cewa idan aka kwatanta da yunwar da aka yi fama da ita a shekarar 2023, to da aka shiga 2024 an sami karuwar masu fama da matsananciyar yunwar da adadinsu ya karu da  miliyan 13.7. Shekaru shida kenan a jere da ake samun karuwar yawan mutanen da suke fama da yunwa.

An kaddamar da wannan rahoton ne a karkashin kawancen kasa da kasa na fada da karancin abinci a duniya wanda ake kira da ( GNAFC) wanda ya kunshi hukumar Abinci ta duniya ( FAO), da kuma ( WFP) da sauran kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya bayyana alkaluman da aka fitar na adadin masu fama da matsananciyar yuwa da cewa; Wani adadi ne wanda bai girgiza duniya ba, domin tana tafiya ne a karkace.”

Wani sashe na rahoton ya yi ishara da cewa da akwai dalilai masu yawa da su ka haddasa  karancin abinci; sun kuwa hada da talauci, koma bayan tattalin arziki, sauyin yanayi mai tsanani, sai dai kuma duk da haka rikice-rikice da fadace-fadace a cikin wasu yankuna, su ne ummul-haba’isin karancin abincin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugabannin masana’antu sun kuma yi kira ga gwamnati da ta daidaita tattalin arziki, inganta saukin gudanar da harkokin kasuwanci, da aiwatar da shirye-shiryen tallafi ga masana’antu na cikin gida.

 

Bugu da kari, masana sun nuna cewa rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi su ne manyan matsaloli ga kamfanoni masu zaman kansu daga kasashen waje, inda kalubalen samun damar mayar da ribar kamfani zuwa kasashen waje da samun kudin waje ke rage amincewar masu zuba jari sosai kuma yana karfafa su su bar kasar.

 

Binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya nuna cewa yanayin tattalin arzikin Nijeriya ya sha wahala tun daga shekarar 2020, inda wasu kamfanoni suka rufe ayyukansu, ko suka yi kaura, ko kuma suka rage yawan ayyukansu a kasar.

 

Ana danganta wannan yanayi da wahalhalun tattalin arziki, canje-canjen kimar kudi, da tsadar gudanar da ayyuka, wanda hakan ya haifar da asarar ayyukan yi da kuma rashin daidaiton tattalin arziki mai yawa.

 

Wasu daga cikin manyan kamfanonin da suka bar Nijeriya sun hada da Standard Biscuits Nigeria Limited, NASCO Fiber Product Limited, Union Trading Company Nigeria Plc, da Deli Foods Nigeria Limited.

 

Ficewar wadannan kamfanonin daga kasuwar Nijeriya ya samo asali ne daga tasirin rashin daidaiton tattalin arziki da sauran kalubalen gudanarwa.

 

Yawancin kamfanonin sun bayyana cewa matsalolin tattalin arziki masu tsanani, canje-canjen kimar kudi marasa tabbas, da hauhawar farashin gudanar da ayyuka su ne manyan dalilan da suka sa suka yanke wannan shawara.

 

“Nijeriya dole ne ta samar da tsarin da zai ja hankalin wadanda za su zuba jari a masana’antu, hakar ma’adanai, wadanda za su sarrafa albarkatun kasa da kayan albarkatun da ake da su, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai hadin kai,” in ji shi.

 

Haka kuma, shugaban Kungiyar Masu Kananan Harkokin Kasuwanci na Nijeriya (ASBON), Dakta Femi Egbesola, ya bayyana cewa ficewar kamfanoni masu zaman kansu na kasashen waje ya shafi yawancin Kananan da Matsakaitan Harkokin Kasuwanci (SMEs) da kamfanoni na cikin gida da ke aiki a kasar, tare da karawa da cewa gwamnati dole ne ta dauki matakan gaggawa don hana ficewar kamfanonin ketare.

 

A yayin da yake magana da daya daga cikin wakilanmu, Daraktan Gudanarwa na Cowry Asset Management Company, Johnson Chukwu, ya bayyana cewa haduwar rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi ya yi tasiri mara kyau ga ra’ayin masu zuba jari na kasashen waje wajen ci gaba da shiga harkokin zuba jari na kamfanoni masu zaman kansu a kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki October 11, 2025 Manyan Labarai Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce October 4, 2025 Rahotonni Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya October 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho