Leadership News Hausa:
2025-08-17@23:44:20 GMT

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

Published: 18th, May 2025 GMT

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato  An Tsinci Gawarwakin Yara Biyar Cikin Tsohuwar Mota A Nasarawa

Hatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.

Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kafa dokar hana zance tsakanin saurayi da budurwa a Kano

Al’ummar unguwar Sharada da ke Ƙaramar Hukumar Birni a Jihar Kano, sun ƙirƙiro dokoki 29 domin gyara halayyar jama’a da kare lafiyar mutane da dukiyoyinsu.

Daga cikin dokokin akwai hana saurayi da budurwa yin zancen dare, musamman a cikin mota, da kuma hana su wuce ƙarfe 10 na dare suna hira a waje.

Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno — INEC Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano

Mahukuntan yankin sun ce sun ɗauki wannan mataki ne saboda damuwa kan lalacewar tarbiyya, ƙaruwa matsalolin tsaro, da kuma rashin bin al’adun da suka dace musamman a tsakanin matasa.

Wannan ba shi ne karon farko da aka taɓa kafa irin wannan doka ba a jihar.

A baya, unguwanni irin su Fagge, Tudun Yola, Kurna da sauransu sun taɓa kafa irin wannan doka, domin kula da tarbiyyar matasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato
  • Gaza: A cikin sa’o’i 24 Mutane da dama sun yi shahada daruruwa sun jikkata a hare-haren Isra’ila
  • Sudan: An kashe mutane 17 a harin da Dakarun RSF suka kai a  El Fasher
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • An kafa dokar hana zance tsakanin saurayi da budurwa a Kano
  • An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza
  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza Tare Da Rusa Gidajen Mutane A Khan Yunis