Leadership News Hausa:
2025-05-18@21:18:25 GMT

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

Published: 18th, May 2025 GMT

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato  An Tsinci Gawarwakin Yara Biyar Cikin Tsohuwar Mota A Nasarawa

Hatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.

Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Amma mu tambayi kanmu, shin da gaske wannan ita ce hakikanin manufar?

Amma bari mu yi la’akari da wannan hasashen mu gani, ko shi ne ya fusata Amurka ta maka harajin kashi 100 bisa 100 kan fina-finai da ake shigar da su daga kasashen waje ko kuma wadanda aka shirya a ketare?

Akwai wani kirkirarren fim mai suna ‘Ne Zha 2’ da masana’antar shirya fina-finai ta kasar Sin ta shirya a baya-bayan nan. Kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar da rahoton cewa, wannan fim ya zama na farko da ya samar da Dala biliyan 1 a kudin tikitin shiga a kasuwar cikin gida kadai. Bugu da kari, wannan adadi, ya haura sama da Dala biliyan 2 a kudaden shiga a duk duniya. Wannan abin a yaba ne, amma a wani bangare,

Wannan rahoton kadai, zai iya fusata gwamnatin Amurka, ganin cewa, kasar tuni ta yi wa kasar Sin bakin fenti da cewa, ita ce babbar abokiyar hamayyarta a bangaren kasuwanci a duniya.

In ba a manta ba, da ma tun bayan rantsar da gwamnatin Trump, ya sha alwashin kakaba haraji kan duk hajojin da ake shigowa da su Amurka. Hukuncin da gwamnatin ta yanke, lallai ba shakka ba ta canja ra’ayi ba kamar yadda ta yi da sauran sanarwar haraji, wanda hakan ya tabbatar da cewa, yakin cinikayyar duniya har da fina-finai.

Tun ba a yi nisa ba, Amurkawa sun fara dandana kudar yakin cinikayya, inda farashin kayayyaki suka fara tsauri ga ‘yan kasar.

Don haka, akwai yiwuwar Amurkawa za su nisanta daga duk wani fim da aka shirya a ketare da zarar sun ga farashin tikitin ya yi tsada. Shin hakan zai iya zama abin da gwamnatin ke so?

Irin wannan hukunci da Amurka ke dauka, hakan yana da mummunan tasiri akan ‘yan kasarta ko da kuwa lamarin zai shafi sauran ‘yan kasashen waje.

Wai mu tambayi kanmu mana, Amurka ta rasa Dattawa da Masana ne wanda za su ba ta shawara kan harkokin tattalin arziki ne, ko kuwa Gwamnatin ta yi kunnen uwar shegu da shawarwarin su ne?

Masana da dama na ganin cewa, wannan mataki na zabga harajin kashi 100 bisa 100 a fina-finai zai haifar da mummunan sakamako ga masana’antar Hollywood, sannan kuma zai gurgunta kyakkyawar alakarta da takwarorinta na duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  • Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • ‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara
  • Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh                                                                                                              
  • Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba