Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
Published: 18th, May 2025 GMT
Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.
Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.
Hatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.
Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kafa dokar hana zance tsakanin saurayi da budurwa a Kano
Al’ummar unguwar Sharada da ke Ƙaramar Hukumar Birni a Jihar Kano, sun ƙirƙiro dokoki 29 domin gyara halayyar jama’a da kare lafiyar mutane da dukiyoyinsu.
Daga cikin dokokin akwai hana saurayi da budurwa yin zancen dare, musamman a cikin mota, da kuma hana su wuce ƙarfe 10 na dare suna hira a waje.
Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno — INEC Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a KanoMahukuntan yankin sun ce sun ɗauki wannan mataki ne saboda damuwa kan lalacewar tarbiyya, ƙaruwa matsalolin tsaro, da kuma rashin bin al’adun da suka dace musamman a tsakanin matasa.
Wannan ba shi ne karon farko da aka taɓa kafa irin wannan doka ba a jihar.
A baya, unguwanni irin su Fagge, Tudun Yola, Kurna da sauransu sun taɓa kafa irin wannan doka, domin kula da tarbiyyar matasa.