Aminiya:
2025-05-18@13:50:35 GMT

Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 37 a ƙauyen Gbajibo-Mudi da ke Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara.

Hatsarin wanda ake fargabar ya auku ne a sanadiyar ɗaukar fasinjoji fiye da kima ya faru ne da yammacin ranar Alhamis da ta gabata.

Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027? Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi

Lamarin na zuwa ne watanni bakwai bayan aukuwar makamancinsa wanda ya janyo asarar fiye da mutum 106 a jihar.

A cewar wani mazaunin yankin, kwale-kwalen wanda ya ɗauko fasinjoji kimanin 150 ya kife ne a tsakiyar ruwa.

Bayanai sun ce waɗanda lamarin ya rutsa da su na komawa gida ne bayan cin kasuwa a tsallake kogin.

Sai dai kuma an alaƙanta faruwar lamarin da saukar mamamkon ruwan sama da iska mai ƙarfi da suka sanya kwale-kwalen ya riƙa tangal-tangal ɗauke da fasinjojin da suka haɗa har da mata da ƙananan yara.

Aminiya ta ruwaito cewa an ceto mutane 47, yayin da ragowar da suka iya ruwa suka fidda kansu zuwa gaɓar kogin.

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Kaiama, Saidu Baba ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa sun ziyarci ƙauyen tare da Sarkin Kaiama da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar.

Ya ce mazauna ƙauyukan Tungamaje da Gelewa abin ya fi shafa, yayin da limamin ɗaya ƙauyen Tungamaje ya ce sun yi asarar rayukan mutane 27 da ciki har da mata bakwai da yara biyu.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Kaiama, Abdullahi Danladi, ya ce ba za su zuba ido ba a riƙa samun aukuwar hatsarin kwale-kwale kusan duk shekara.

Ya bayyana cewa sun fara shirin kafa wani kwamiti da zai tilasta ɗauka da kuma tanadar matakan kariya yayin hawa kwale-kwale ciki har da sanya rigar ruwa da kuma haramta tafiyar dare da makamantansu.

Sarkin Kaiama, Alhaji Muazu Umar, ya nanata muhimmancin wayar da kan fasinjoji da masu jiragen ruwa dangane da kiyaye matakan kariya yayin duk wani sufuri da za su yi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kwara Kifewar kwale kwale kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 3 sun mutu, 21 sun jikkata a turmutsitsin karɓar kuɗin tallafi a Borno

An tabbatar da mutuwar mutum uku tare da jikkatar wasu da dama sakamakon turmutsutsu a yayin wani taron rabon kuɗaɗen tallafi a garin Bama da ke jihar Borno.

Wasu bayanai sun bayyana cewa ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Najeriya da UNICEF suka shirya rabon tallafin.

Shaidun gani da ido sun ce, turmutsitsin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin karfe 8:00 na safe a makarantar firamare ta Kasugula, daya daga cikin cibiyoyin bayar da tallafi da aka kebe a garin Bama.

Rahoton na nuni da cewar waɗanda suka ci gajiyar shirin sun taru ne domin karɓar tallafin kuɗi na naira 28,500 kowannensu.

Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta da cizo a Ribas Budurwa ta guntule mazakutar saurayinta da cizo a Ribas

Turmutsitsin ya faru ne a daidai lokacin da jama’a suka yi cincirundo a bakin  kofar makarantar, lamarin da ya haifar da turereniya.

 

Wani dan shekara 60 mazaunin Mazaɓar Bukar Tela, wanda lamarin ya ritsa da shi ya rasu ne a lokacin da aka isa babban asibitin garin Bama. Daga baya wasu mutane biyu da suka jikkata sun mutu yayin da ake jinya a asibiti.

Majiyar ta ce, waɗanda suka samu raunukan sun hada da mata da maza, kuma an tura karin sojoji wurin da lamarin ya faru domin dawo da zaman lafiya tare da saukaka kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Daga bisani aka bayar da gawarwakin mamatan ga iyalansu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Kungiyar ta ICRC_Africa ta ce ba ta da hannu a aikin rarraba kudaden a Bama wanda ya haifar da wannan turmutsitsin da ya kai ga asarar rayuka, kamar yadda aka gabatar a cikin rahoton farko.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara
  • Hukumar KNARDA Ta Ƙudiri Aniyar Yashe Madatsun Ruwa A Kano 
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Mutum 3 sun mutu, 21 sun jikkata a turmutsitsin karɓar kuɗin tallafi a Borno
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato