Aminiya:
2025-10-13@18:09:48 GMT

Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 37 a ƙauyen Gbajibo-Mudi da ke Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara.

Hatsarin wanda ake fargabar ya auku ne a sanadiyar ɗaukar fasinjoji fiye da kima ya faru ne da yammacin ranar Alhamis da ta gabata.

Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027? Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi

Lamarin na zuwa ne watanni bakwai bayan aukuwar makamancinsa wanda ya janyo asarar fiye da mutum 106 a jihar.

A cewar wani mazaunin yankin, kwale-kwalen wanda ya ɗauko fasinjoji kimanin 150 ya kife ne a tsakiyar ruwa.

Bayanai sun ce waɗanda lamarin ya rutsa da su na komawa gida ne bayan cin kasuwa a tsallake kogin.

Sai dai kuma an alaƙanta faruwar lamarin da saukar mamamkon ruwan sama da iska mai ƙarfi da suka sanya kwale-kwalen ya riƙa tangal-tangal ɗauke da fasinjojin da suka haɗa har da mata da ƙananan yara.

Aminiya ta ruwaito cewa an ceto mutane 47, yayin da ragowar da suka iya ruwa suka fidda kansu zuwa gaɓar kogin.

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Kaiama, Saidu Baba ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa sun ziyarci ƙauyen tare da Sarkin Kaiama da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar.

Ya ce mazauna ƙauyukan Tungamaje da Gelewa abin ya fi shafa, yayin da limamin ɗaya ƙauyen Tungamaje ya ce sun yi asarar rayukan mutane 27 da ciki har da mata bakwai da yara biyu.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Kaiama, Abdullahi Danladi, ya ce ba za su zuba ido ba a riƙa samun aukuwar hatsarin kwale-kwale kusan duk shekara.

Ya bayyana cewa sun fara shirin kafa wani kwamiti da zai tilasta ɗauka da kuma tanadar matakan kariya yayin hawa kwale-kwale ciki har da sanya rigar ruwa da kuma haramta tafiyar dare da makamantansu.

Sarkin Kaiama, Alhaji Muazu Umar, ya nanata muhimmancin wayar da kan fasinjoji da masu jiragen ruwa dangane da kiyaye matakan kariya yayin duk wani sufuri da za su yi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kwara Kifewar kwale kwale kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

Shugaban ya ci gaba da cewa, a karkashin shugabancinsa, Hukumar za ta yi namijin kokari wajen bayar da goyon bayanta, wajen fitar da kayan da ba su shafi dangogin Mai ba, zuwa kasar waje, musamman ta hanyar cin giyar albakatun yanayin na Abuja da kuma na bangaren aikin noma, da birnin ke da shi. Ya kara da cewa, ta hanyar wadannan alkatun kasar da birnin ke da su, Hukumar za ta kara bayar da gudunmwarta, wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar nan da kuma kara fitar da kayan da ba su shafi Man ba, zuwa ketare.

 

A cewarsa, domin Hukumar ta tabbatar da na kara mayar da hankalin wajen ganin ana bin ka’ida da kuma tabbatar da ingancin gudanar da ayyukanta, ta kirkiro da tsare-tsare na fasahar zamani na bai daya da ake kira a turance, PCS da kuma NSW.

A cewarsa, wadannan fasahar ta zamani, za su taimaka wajen hada masu ruwa da tsaki a fannin da ke fitar da kaya zuwa ketare tare da kuma rage jinkiri wajen fitar da kayan waje da kuma samar da kyakyawan yanayi ga masu fitar da kayan ketare.Shugaban ya sanar da cewa, Hukumar na alfaharin danganta manta da ayyukan da Cibiyar ta kolin kasuwanci ta Abuja ke ci gaba da gudanarwa musamman a bangaren kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

Dantsoho ya kuma gayyaci masu ruwa da tsaki a fannin kar su bari a barsu a baya, wajen cin gajiyar saukin da Hukumar ta samar na fitar da kaya daga cikin kasar nan, zuwa ketare.

Kazalika, Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar ta kuma samar da tsarin fasahar zamani na fitar da kaya a cikin sauki a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar wato EPT.

Ya kara da cewa, wannan fasahar ta taimaka matuka wajen fitar da kaya waje ba tare da wani tarnaki ba.

Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta kuma fadada fasahar ta EPT, domin samar da saukin fitar da kaya ga kananan da matsakaitan masana’antun kasar suka sarrafa, domin fitar da su ketare.

Hakazalika, Shugaban ya bayyana cewa, domin ayyukan Hukumar su tafi kafada da kafada da kudurin Gwamnatin Tarayya NPA ta saita gudanar da ayyukanta ta hanyar yin amfani da fasahar ta zamani ta PCS.

A cewarsa, wannan zai tabbatar da samar da wani ginshike ga fasahar NSW, inda za a rinka fitar da kayan waje, ba tare da wata matsala ba.

Dantsoho ya yi nuni da cewa, fasahar ta NSW aba ce, da ake yin amfani da da ita, a daukacin fadin duniya, wajen samar da saukin fitar da kaya waje.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Hukumar na daukar Malamai wajen ganin cewa, ayyukanta, sun kai da lungu da sako, da ke da wuyar isa a kasar.

Ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yau, kofar Hukumar a bude take domin yin hadaka da su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi  October 10, 2025 Tattalin Arziki Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi October 10, 2025 Tattalin Arziki Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama October 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano