Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara
Published: 18th, May 2025 GMT
Wani hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 37 a ƙauyen Gbajibo-Mudi da ke Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara.
Hatsarin wanda ake fargabar ya auku ne a sanadiyar ɗaukar fasinjoji fiye da kima ya faru ne da yammacin ranar Alhamis da ta gabata.
Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027? Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo AwoniyiLamarin na zuwa ne watanni bakwai bayan aukuwar makamancinsa wanda ya janyo asarar fiye da mutum 106 a jihar.
A cewar wani mazaunin yankin, kwale-kwalen wanda ya ɗauko fasinjoji kimanin 150 ya kife ne a tsakiyar ruwa.
Bayanai sun ce waɗanda lamarin ya rutsa da su na komawa gida ne bayan cin kasuwa a tsallake kogin.
Sai dai kuma an alaƙanta faruwar lamarin da saukar mamamkon ruwan sama da iska mai ƙarfi da suka sanya kwale-kwalen ya riƙa tangal-tangal ɗauke da fasinjojin da suka haɗa har da mata da ƙananan yara.
Aminiya ta ruwaito cewa an ceto mutane 47, yayin da ragowar da suka iya ruwa suka fidda kansu zuwa gaɓar kogin.
Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Kaiama, Saidu Baba ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa sun ziyarci ƙauyen tare da Sarkin Kaiama da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar.
Ya ce mazauna ƙauyukan Tungamaje da Gelewa abin ya fi shafa, yayin da limamin ɗaya ƙauyen Tungamaje ya ce sun yi asarar rayukan mutane 27 da ciki har da mata bakwai da yara biyu.
Da yake nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Kaiama, Abdullahi Danladi, ya ce ba za su zuba ido ba a riƙa samun aukuwar hatsarin kwale-kwale kusan duk shekara.
Ya bayyana cewa sun fara shirin kafa wani kwamiti da zai tilasta ɗauka da kuma tanadar matakan kariya yayin hawa kwale-kwale ciki har da sanya rigar ruwa da kuma haramta tafiyar dare da makamantansu.
Sarkin Kaiama, Alhaji Muazu Umar, ya nanata muhimmancin wayar da kan fasinjoji da masu jiragen ruwa dangane da kiyaye matakan kariya yayin duk wani sufuri da za su yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kwara Kifewar kwale kwale kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
Wata tankar mai ta yi gobara a wani gudan mai a yankin Tungan-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Rijau a Jihar Neja, lamarin da ya janyo ƙonewar gidaje da kadarori da masu yawa.
Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne a lokacin da tankar take shirin sauke mai a ranar Litinin da yamma, inda wutar ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.
Duk da cewa babu wanda ya rasa ransa, lamarin ya haifar da firgici inda mazauna yankin suka yi ta tserewa suka bar gidajensu yayin da tankar ke ci da wuta.
Tankar mai ta yi hatsari a hanyar Lapai-Agaie Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a BornoA wani lamari ba daban, wata tankar mai ta kife a kan hanyar Lapai zuwa Agaie, lamarin da ya toshe hanya tare da haddasa cunkoson ababen hawa.
Shaidu sun ce tankar, wadda ke ɗauke da fetur daga Legas zuwa Gombe, ta kife ne da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin bayan jikinta ya rabu da kan motar, ya ƙetare hanya, abin da ya tayar da hankalin jama’a.
Wani mazaunin yankin, Malam Mahmud Abubakar, ya ce jami’an tsaro sun garzaya wajen domin tsare yankin, sannan aka tura ma’aikatan kashe gobara don kauce wa tashin wuta.
Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne a yankin Efu-Nda-Egbo na Ƙaramar Hukumar Lapai, inda ya haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani.
Kokarin tuntuɓar Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, bai yi nasara ba, domin bai amsa kiran wayar da wakilinmu ya yi masa ba.