Gaza: Falasdinawa 150 Ne Su Ka Yi Shahada A Yau Lahadi
Published: 18th, May 2025 GMT
Mai Magana da yawun masu ayyukan ceto a yankin Gaza, ya sanar da cewa; Daga safiyar yau Lahadi zuwa marece adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 150.
Mahmud al-Basal ya fadawa tashar talabijin din ‘almayadin’ cewa; hare-haren na HKI sun fi tsanani ne a arewacin zirin Gaza, kuma kai tsaye suke kai wa sansanonin ‘yan hijira hari.
Da yake Magana akan kayan aikin da suke amfani da su domin ceto, al-Basal ya ce, kaso 75% na kayan aikinsu sun lalace, musamman motoci, kuma rashin makamashi ya sa ba za su iya amfani da su ne.
Haka nan kuma ya yi ishara da amfani da yunwa da HKI take yi akan falasdinawa,sannan ya kara da cewa; Da akwai dubban Falasdinawa da suke yi bacci ba tare sun sami burodin da za su ci ba.
A wurare uku da sojojin mamayar su ka yi wa mutane kisan kiyashi, adadin shahidai ya kai 150,kamar yadda jami’in aikin ceton ya shaidawa tashar almayadin. Daga cikin yankunan da akwai Beit-Lahiya, da Faluja, a arewacin Jabaliya.
Su kuwa Asibitocin yankin na Gaza suna cikin wuraren da sojojin mamayar su ka kai wa hare-hare. Asibiti na karshe da harin sojojin mamayar ya shafa shi ne; Asibitin Indonesia, wanda daga shi, ya zamana babu wani asibiti guda daya da ya saura mai aiki a Arewacin Gaza.
Dama dai sojojin mamayar sun baje asibitin Beit Hanun da kasa, su ka kuma ragargaza asibitin Kamal Adwan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin mamayar
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya
Shugaban kasar Sudan kuma babban kwamandan sojojin kasar Janar Abdulfattah Alburhan, ya yi watsi da shawarar Amurka ta kawo karshen yaki a kasarsa wanda ya lakume rayukan mutane da dama, ya kuma raba kasar gida biyu a cikin watanni kimani 30 da suka gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘AfricaNews’ ya nakalto Burhan yana fadar haka a ranar Lahadi jim kadan bayan ganawarsa da tawagar kasar Amurka wacce ta gabatar masa da shawarar, ya kuma bayyana ta a matsayin mafi munin shawarar tsagaita budewa juna wuta da aka gabatar masa ya zuwa yanzun. Burhan ya zargi Massad Boulos mai bawa shugaban kasar Amurka a kan al-amuran nahiyar Afirka da da kokarin rusa sojojin kasar Sudan da kuma bawa yan tawaye karkashin jagorancin Amity damar ci gaba da iko da wani daga bangaren kasar.
Burhan ya zargi Amurka da goyon bayan yan tawayen a cikin shawarar da ta gabatar, kuma shawarar ba irin zaman lafiyan da mutanen sudan suke so ba. Masana suna ganin gwamnatin Amurka da kawayenta wadanda suke goyon bayan yantawaye a duniya musamman a cikin kasashen Larabawa suna son sake raba kasar Sudan ne, kuma sun gabatar da wannan shawarar ce a dai-dai lokacinda suka fahinci cewa gwamnatin kasar tana samun nasara a kan yan tawaye wadanda suke iko da yankin Darfur na yammacin kasar ta Sudan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji November 24, 2025 Habasha: Bayan Shekaru 10,000 Dutsen Hayli Gubbi Ya Yi Aman Wuta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci