Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
Published: 18th, May 2025 GMT
Iran ta yi kira da a kawo karshen neman shafe wata al’umma daga kan doron kasa tare da kawo karshen rashin hukunta shugabannin ‘yan sahayoniyya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan hare-hare da laifukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya take ci gaba da yi a cikin ‘yan kwanakin nan a zirin Gaza, yana mai kira da a kawo karshen kisan kiyashi da rashin hukunta shugabannin gwamnatin ‘yan shayoniyya da kuma gurfanar da su a gaban kuliya don hukunta su.
Baqa’i ya yi ishara da laifuffukan da ba a taba ganin irinsa ba da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta yi kan al’ummar Falastinu da ba su da kariya a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, ya kuma yi kakkausar suka kan munanan hare-haren da aka kai kan matsugunan ‘yan gudun hijira na wucin gadi da cibiyoyin kiwon lafiya a Gaza, wanda ya yi sanadin shahada da jikkata daruruwan mutane a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata. Ya yi nuni da alhakin kai tsaye da ke wuyan masu kare gwamnatin ‘yan mamaya da magoya musu baya a fagen soja da na siyasa, musamman Amurka da Birtaniya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce: “A halin da ake ciki, bayan gaza cimma matsaya a yunkurin masu shiga tsakani na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ‘yan mamaya sun kara zafafa kai hare-haren ta’addanci da nufin gabatar da wasu bukatu da ba su dace ba, da kuma raba mazauna yankin Zirin Gaza da muhallinsu, wanda tabbas hakan zai fuskanci turjiya daga al’ummar Falasdinu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Amurka Ya Zanta Ta Wayar tarho Da Benyamin Natanyahu Dangane Da Iran Da Gaza
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya zanta ta wayar tarho da firay ministan HKI Benyamin Natanyahu kan kasar Iran da kuma yakin Gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa majiyar ofishin Natanyahu ta bayyana cewa tattaunawar tana zuwa ne a dai-dai lokacinda rikici da yaki yake ci gaba a gaza, da kuma tattaunawa kan shirin Nuclear kasar Iran ke ci gaba.
Labarin ya kara da cewa shugaban kasar Amurka na jirin jawabin da kasar Iran zata mayar masa dangane da shawarar da ya gabatar na warware matsalar tashe makamancin Yuranium a Iran.
Har’ila yau ya na jiran jawabin da kungiyar Hamas za ta bayar kan yarjeniyar dakatar da yaki a Gaza.
Shugaban dai yana cikin matsin lamba don ganin an warware wadannan al-amura guda biyu na gabas ta tsakiya.
Tattaunawar wanda bai fi mintoci 40 ba, ya bukaci gwamnatin Natanyaho ta shirya daukar matakan gaggawa bayan da shugaban ya sami wadannan sakonnin da yake jira.
Don haka ne ake saran Natanyanhu zai gudanar da taron gaggawa tare da manya manyan jami’an gwamnatinsa a ma’aikatar tsaro ko yakin na kasar, don tattauna wadannan al-amura.