Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
Published: 18th, May 2025 GMT
Iran ta yi kira da a kawo karshen neman shafe wata al’umma daga kan doron kasa tare da kawo karshen rashin hukunta shugabannin ‘yan sahayoniyya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan hare-hare da laifukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya take ci gaba da yi a cikin ‘yan kwanakin nan a zirin Gaza, yana mai kira da a kawo karshen kisan kiyashi da rashin hukunta shugabannin gwamnatin ‘yan shayoniyya da kuma gurfanar da su a gaban kuliya don hukunta su.
Baqa’i ya yi ishara da laifuffukan da ba a taba ganin irinsa ba da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta yi kan al’ummar Falastinu da ba su da kariya a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, ya kuma yi kakkausar suka kan munanan hare-haren da aka kai kan matsugunan ‘yan gudun hijira na wucin gadi da cibiyoyin kiwon lafiya a Gaza, wanda ya yi sanadin shahada da jikkata daruruwan mutane a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata. Ya yi nuni da alhakin kai tsaye da ke wuyan masu kare gwamnatin ‘yan mamaya da magoya musu baya a fagen soja da na siyasa, musamman Amurka da Birtaniya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce: “A halin da ake ciki, bayan gaza cimma matsaya a yunkurin masu shiga tsakani na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ‘yan mamaya sun kara zafafa kai hare-haren ta’addanci da nufin gabatar da wasu bukatu da ba su dace ba, da kuma raba mazauna yankin Zirin Gaza da muhallinsu, wanda tabbas hakan zai fuskanci turjiya daga al’ummar Falasdinu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.
Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA