Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne
Published: 18th, May 2025 GMT
Iran ta yi kakkausan suka game da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa kan kasar Yemen tana mai danganta su da babban laifin yaki.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa kan ababen more rayuwa na tattalin arzikin kasar Yemen da kuma cibiyoyin jama’a sun zama “laifi na yaki da cin zarafin bil’adama.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Asabar, Esmail Baghai ya yi kakkausar suka kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kaiwa kan manyan tashoshin jiragen ruwa na kasar Yemen.
Ya kara da cewa hare-haren da aka kai a tashar jiragen ruwa ta Hudaydah, Ras Issa da kuma Salif na kasar Yemen, ya zama babban cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.
Mista Baghai Ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila tana kai irin wadannan hare-hare ne a daidai lokacin da al’ummar kasar Yamen ke fama da matsanancin hali na jin kai.
Kakakin ya jaddada cewa Amurka da Birtaniya da wasu kasashen yammacin duniya suna da hannu a ci gaba da aikata laifukan da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza da kuma ta’addancin da take yi kan kasashen musulmi a yankin.
Ya jaddada cewa goyon bayan da kasashen yammacin duniya ke baiwa Isra’ila, ya kara bai wa gwamnatin Isra’ilar karfin gwiwa wajen aiwatar da hare-haren wuce gona da iri da kisan kiyashin da take yi wa mata da kananan yara na Falastinawa wadanda ba su da kariya, kuma a halin yanzu ga al’ummar Yemen da ake zalunta.
Jami’in na Iran ya kuma soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da yin shiru a kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke yi, Ya kara da cewa: Dole ne al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen yakar zaluncin da gwamnatin ke yi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da gwamnatin Isra ila ke hare haren da kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya
Magajin garin birnin Tehran ya bayyana cewa: Karyar ‘yan sahayoniyya ya tonu na cewa ba su kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran ba
Magajin garin birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ali-Ridha Zakani ya tabbatar da cewa: Karairayi da ‘yan sahayoniyya suke yadawa dangane da rashin kai hare-hare kan fararen hula a yakin da suka kaddamar kan Iran a fili yake karara. Yana mai nuni da cewa akwai kwarararn dalilai da ake da su wadanda suke fallasa karyar wadannan ikirari.
A cikin bayanansa, Zakani ya ce: Dalilai kan wadannan karairayi su ne kaburbura gawawwaki da suka hada da fili mai lamba ta 42 a makabartar Al-Jannar – Zahra da ke babban birnin Tehran. Ya bayyana cewa, duk wanda ya ga jerin sunayen wadanda suka yi shahada a lokacin yakin zai iya ganin karara irin karyar da ‘yan sahayoniyya suka shirga, kamar yadda kowa zai iya ganin gine-ginen da aka kai musu hare-hare a birnin Tehran.
Zakani ya kuma yi ishara da hare-haren baya- bayan nan da yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya suka kai kan wuraren fararen hula da suka hada da cibiyoyin kiwon lafiya, inda ya kara da cewa, gwamnatin ‘yan sahayoniyya sun kai hare-hare kan motocin daukar marasa lafiya da asibitoci da ba su bukatar wata shaida wajen tabbatar da karairayin ‘yan sahayoniyya.