HausaTv:
2025-11-27@22:01:28 GMT

Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne

Published: 18th, May 2025 GMT

Iran ta yi kakkausan suka game da hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa kan kasar Yemen tana mai danganta su da babban laifin yaki.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa kan ababen more rayuwa na tattalin arzikin kasar Yemen da kuma cibiyoyin jama’a sun zama “laifi na yaki da cin zarafin bil’adama.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Asabar, Esmail Baghai ya yi kakkausar suka kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kaiwa kan manyan tashoshin jiragen ruwa na kasar Yemen.

Ya kara da cewa hare-haren da aka kai a tashar jiragen ruwa ta Hudaydah, Ras Issa da kuma Salif na kasar Yemen, ya zama babban cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya.

Mista Baghai Ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila tana kai irin wadannan hare-hare ne a daidai lokacin da al’ummar kasar Yamen ke fama da matsanancin hali na jin kai.

Kakakin ya jaddada cewa Amurka da Birtaniya da wasu kasashen yammacin duniya suna da hannu a ci gaba da aikata laifukan da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza da kuma ta’addancin da take yi kan kasashen musulmi a yankin.

Ya jaddada cewa goyon bayan da kasashen yammacin duniya ke baiwa Isra’ila, ya kara bai wa gwamnatin Isra’ilar karfin gwiwa wajen aiwatar da hare-haren wuce gona da iri da kisan kiyashin da take yi wa mata da kananan yara na Falastinawa wadanda ba su da kariya, kuma a halin yanzu  ga al’ummar Yemen da ake zalunta.

Jami’in na Iran ya kuma soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da yin shiru a kan hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke yi, Ya kara da cewa: Dole ne al’ummar musulmi su tashi tsaye wajen yakar zaluncin da gwamnatin ke yi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da gwamnatin Isra ila ke hare haren da kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu

Daga Bello Wakili

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi labarin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi cikin alhini da jimami.

Fitaccen malamin da ke Bauchi ya rasu ne a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2026, yana da shekaru 101.

Shugaban Ƙasan ya yi jimamin rasuwar jagoran Darikar Tijjaniyya, yana bayyana shi a matsayin ginshiƙin ɗabi’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa da wa’azi.

Shugaba Tinubu ya ce rashinsa babban rashi ne ba ga iyalansa da dimbin mabiyansa kaɗai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

Shugaban Ƙasa ya tuna da albarka da goyon bayan da ya samu daga marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a lokacin yakin zaɓen 2023.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba, mai cike da natsuwa da hikima. A matsayinaa na mai wa’azi kuma masani kan tafsirin Alƙur’ani Mai Girma, yana da’awar zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga mabiyan Shehun a ci da wajen ƙasa  bisa wannan babban rashi.

Haka kuma ya ja hankalinsu da su girmama sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, ƙarfafa dangantakarsu da Allah, da kuma kasancewa masu taushin zuciya ga jama’a.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Al-Houthi ya yi ta’aziyyar shahadar babban kwamanda na Hizbullah
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin