Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi
Published: 18th, May 2025 GMT
An yi wa ɗan wasan gaba na ƙungiyar Nottingham Forest, Taiwo Awoniyi allurar barci mai nauyi domin taimaka masa murmurwa daga tiyatar da aka yi masa.
Bayanai sun tabbatar cewa an garzaya da ɗan wasan ɗan asalin Nijeriya asibiti ne domin yi masa tiyata a ranar Litinin, bayan ya samu mummunan rauni a cikinsa a wasan da suka tashi canjaras, 2-2 da Leicester a Gasar Premier ta Ingila.
Alamu sun nuna cewa rayuwar ɗan wasan mai shekara 27 ba ta cikin haɗari, kuma allurar barcin da aka yi masa za ta taimaka ne wajen tsagaita ayyukan zuciya da jikinsa wanda hakan zai taimaka wajen hanzarta samun sauƙi.
Awoniyi ya yi karo ne da ƙarfen raga sa’ilin da yake ƙoƙarin cin ƙwallo mintuna kaɗan gabanin tashi daga karawar tasu da Leicester.
Likitoci sun kwashe tsawon mintuna suna kula da shi kafin barin sa ya ci gaba da wasa, duk da raɗaɗin da yake ji, kamar yadda aka gani baro-baro, kasancewar a lokacin Forest ta ƙarar da yawan ’yan wasa da za ta iya canzawa.
A ranar Litinin aka kara tabbatar da munin raunin da ya samu bayan likitocin ƙungiyarsa sun kara duba shi, aka garzaya da shi asibiti domin yi masa tiyata.
Amma ranar Talata, Nottingham Forest ta fitar da sanarwa cewa “Awoniyi na samun sauki”.
A yayin wasan nasu an ga yadda aka samu wata ’yar rashin jituwa tsakanin mamallakin ƙungiyar Evangelos Marinakis da mai horas da ita Nuno Espirito Santo a cikin filin wasa jim kaɗan bayan kammala wasan a ranar Lahadi.
Bayan sukar abin da mamallakin ƙungiyar ya yi, Forest ta ce lamarin ya faru ne kasancewar Marinaki bai ji daɗin yadda Awoniyi ya ci gaba da wasa ba duk kuwa da raunin da ya samu.
Sanarwar ƙungiyar ta ce “Evangelo Marinakis bai ɗauki Nottingham a matsayin ƙungiyar ƙwallon ƙafa kawai ba, ya ɗauke ta a amatsayin wani ɓangare na iyalinsa — kuma yana ƙoƙarin ganin kowa ya yi amanna da hakan.
“Shi ya sanya bai ji daɗin abin da ya faru ba a filin wasa na Leicester City a ranar Lahadi.
“Matakin da ya ɗauka ya kasance na nuna tsantsar kulawa da tallafa wa daya daga cikin waɗanda ya ɗauka a matsayin nasa.”
Wane ne Taiwo Awoniyi?Awoniyi ɗan asalin Najeriya ne mai shekaru 27 da ke taka leda a ƙungiyar Nottingham Forest da ke Birtaniya.
Ya tafi ƙungiyar ne a watan Yunin 2022 daga ƙungiyar Union Berlin da ke Jamus, kuma ya fara wasan ƙwallon ƙafa ka’in da na’in ne a ƙungiyar Liverpool a shekara ta 2015 kafin ya tafi wasu ƙungiyoyi a Jamus da Holland da kuma Belgium a matsayin aro.
Ɗan wasan na gaba ya taka wa Nijeriya a gasanni daban-daban a matakai daban-daban kafin buga wa ƙasar a babbar ƙungiyarta ta Super Eagles.
Yana daga cikin tawagar Nijeriya da ta yi nasara kan Libya a wasan neman gurbin gasar Kofin nahiyar Afirka ta 2025. Dan wasan na da aure da ɗa ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya a ƙungiyar
এছাড়াও পড়ুন:
Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Katsina ta sanar cewa, za a fara jigilar maniyyatan jihar a ranar Lahadi 18 ga wannan wata na Mayu, 2025, zuwa Ƙasa Mai Tsarki.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Badaru Bello Karofi, ya shaida wa wakilinmu, cewa maniyyatan da suka fito daga Malunfashi da Bakori, Ƙanƙara, Dandume, Ƙafur da Ɗanja sune rukunin farko da ake sa ran za su tashi daga filin sauka da tashin jiragen sama na Umaru Musa da ke cikin babban birnin jihar.
Tun farko sai da jagoran mahajjatan jahar, wanda kuma shi ne mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Joɓe ya bayyana cewar, gwamnatin jihar ta ɗauki duk wasu matakan da suka wajaba tun daga gida har zuwa Ƙasa Mai Tsarki domin ganin cewa mahajjatan jihar sun samu duk wata kulawa a hukumance don gudanar da aikin ibadar cikin jin daɗi da walwala.
Sai dai Amirul Hajjin ya ja hankalin maniyatan da su kiyaye duk wata doka, tun daga nan gida har a can Saudiyya inda suke ɗaukar hukunci mai tsanani ga wanda ya saɓa, musamman shiga da duk wani nau’in abin da zai sa maye da sauransu.
Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Borno