Aminiya:
2025-08-17@16:31:55 GMT

Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi

Published: 18th, May 2025 GMT

An yi wa ɗan wasan gaba na ƙungiyar Nottingham Forest, Taiwo Awoniyi allurar barci mai nauyi domin taimaka masa murmurwa daga tiyatar da aka yi masa.

Bayanai sun tabbatar cewa an garzaya da ɗan wasan ɗan asalin Nijeriya asibiti ne domin yi masa tiyata a ranar Litinin, bayan ya samu mummunan rauni a cikinsa a wasan da suka tashi canjaras, 2-2 da Leicester a Gasar Premier ta Ingila.

Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?

Alamu sun nuna cewa rayuwar ɗan wasan mai shekara 27 ba ta cikin haɗari, kuma allurar barcin da aka yi masa za ta taimaka ne wajen tsagaita ayyukan zuciya da jikinsa wanda hakan zai taimaka wajen hanzarta samun sauƙi.

Awoniyi ya yi karo ne da ƙarfen raga sa’ilin da yake ƙoƙarin cin ƙwallo mintuna kaɗan gabanin tashi daga karawar tasu da Leicester.

Likitoci sun kwashe tsawon mintuna suna kula da shi kafin barin sa ya ci gaba da wasa, duk da raɗaɗin da yake ji, kamar yadda aka gani baro-baro, kasancewar a lokacin Forest ta ƙarar da yawan ’yan wasa da za ta iya canzawa.

A ranar Litinin aka kara tabbatar da munin raunin da ya samu bayan likitocin ƙungiyarsa sun kara duba shi, aka garzaya da shi asibiti domin yi masa tiyata.

Amma ranar Talata, Nottingham Forest ta fitar da sanarwa cewa “Awoniyi na samun sauki”.

A yayin wasan nasu an ga yadda aka samu wata ’yar rashin jituwa tsakanin mamallakin ƙungiyar Evangelos Marinakis da mai horas da ita Nuno Espirito Santo a cikin filin wasa jim kaɗan bayan kammala wasan a ranar Lahadi.

Bayan sukar abin da mamallakin ƙungiyar ya yi, Forest ta ce lamarin ya faru ne kasancewar Marinaki bai ji daɗin yadda Awoniyi ya ci gaba da wasa ba duk kuwa da raunin da ya samu.

Sanarwar ƙungiyar ta ce “Evangelo Marinakis bai ɗauki Nottingham a matsayin ƙungiyar ƙwallon ƙafa kawai ba, ya ɗauke ta a amatsayin wani ɓangare na iyalinsa — kuma yana ƙoƙarin ganin kowa ya yi amanna da hakan.

“Shi ya sanya bai ji daɗin abin da ya faru ba a filin wasa na Leicester City a ranar Lahadi.

“Matakin da ya ɗauka ya kasance na nuna tsantsar kulawa da tallafa wa daya daga cikin waɗanda ya ɗauka a matsayin nasa.”

Wane ne Taiwo Awoniyi?

Awoniyi ɗan asalin Najeriya ne mai shekaru 27 da ke taka leda a ƙungiyar Nottingham Forest da ke Birtaniya.

Ya tafi ƙungiyar ne a watan Yunin 2022 daga ƙungiyar Union Berlin da ke Jamus, kuma ya fara wasan ƙwallon ƙafa ka’in da na’in ne a ƙungiyar Liverpool a shekara ta 2015 kafin ya tafi wasu ƙungiyoyi a Jamus da Holland da kuma Belgium a matsayin aro.

Ɗan wasan na gaba ya taka wa Nijeriya a gasanni daban-daban a matakai daban-daban kafin buga wa ƙasar a babbar ƙungiyarta ta Super Eagles.

Yana daga cikin tawagar Nijeriya da ta yi nasara kan Libya a wasan neman gurbin gasar Kofin nahiyar Afirka ta 2025. Dan wasan na da aure da ɗa ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya a ƙungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi

Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO), Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana cewa Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin ƙasar nan da yake ci gaba da yi. 

Okonjo-Iweala ta shaida wa manema labarai hakan ne ranar Alhamis bayan ta gana da shugaban ƙasar a Abuja.

Motar tifa ta murƙushe ɗalibai biyu har lahira a Bayelsa Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar

“Shugaban ƙasa [Tinubu] da muƙarrabansa sun yi ƙoƙari sosai wajen daidaita tattalin arzikin Nijeriya.

“Wannan namijin ƙoƙarin na Tinubu abu ne da ya zama dole a yaba masa da ba kowa zai iya yi ba.

Tsohuwar Ministar Kuɗin ta Nijeriyar ta ƙara da cewa, yanzu aikin da ke gaban shugaban shi ne ya haɓaka tattalin arzikin ta yadda kowane ɗan ƙasa zai samu na kansa cikin sauƙi.

Ngozi ta yi kira ga gwamnatin Nijeriyar ta tanadi hanyoyi da dabarun sauƙaƙa wa talakawan ƙasar da ke fama da raɗaɗin tsare-tsaren tattalin arziƙi da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa.

Duk da ta yaba wa shugaban ƙasar kan tsare-tsarensa na tattalin arziki da suka haɗa da cire tallafin man fetur, tsohuwar Ministar Kuɗin ta ce dole ne gwamnatin ta tallafa wa ’yan ƙasar.

Iweala ta ce “muna ganin shugaban ƙasar da gwamnatinsa sun daidaita tattalin arzikin Najeriya, amma duk da haka sai sun tabbatar da ɗorewar sauyin mai kyau da aka samu zuwa yanzu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025)
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
  • Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi