Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Published: 18th, May 2025 GMT
Samar da kyakkyawar sadarwa a tsakaninku
Yawan magana da sadarwa mai kyau na hana matsala girma. Idan wani abu ya dame ku, kada ku boye, ku gaya wa juna ta hanya mai dadi da girmamawa.
Gujewa kwatanta rayuwarku da ta wasuKowanne aure yana da nasa halin. Kada ku kwatanta rayuwarku da ta wasu, domin hakan yana iya jefa ku cikin damuwa ko rashin godiya.
Magulmata da masu kyashi suna iya haddasa matsala a aure. Kada ku bari mutane su rarrashe ku da magana mara amfani ko su haifar da rashin fahimta.
Bai wa Juna hakkokiAure yana da hakkoki. Miji yana da nasa, haka ma mata. Ku rika bai wa juna hakkin da shari’a ta tanada, kamar girmamawa, kulawa, da soyayya.
Mutunta ra’ayin juna idan bai kauce hanya baKowa yana da ra’ayi da tunani. Idan ba saba wa addini ko al’ada ya yi ba, yana da kyau a girmama ra’ayin juna domin samun zaman lafiya.
Rashin boyewa juna sirriMa’aurata ya kamata su rika yarda da juna. Idan aka fara boye sirri, hakan yana iya kawo rashin yarda da rashin zaman lafiya. Duk wata matsala, ku tattauna tare.
Allah ya sanya albarka cikin zamantakewar aure.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
An sake tabbatar wa ma’aikatan Gwamnatin Tarayya FG da suka yi ritaya cewa za a biya su wani bangare na kudaden ariyas a cikin wannan watan, kamar yadda hukumomin da abin ya shafa suka yi alkawari.
Mataimakin Sakataren ƙungiyar masu karɓar fansho ta ƙasa, Alhaji Ahmed Gazali, ya bayar da wannan tabbaci yayin da ake tattaunawa da shi ta wayar tarho daga Abuja.
Alh. Ahmed Gazali, ya yi bayanin cewas daraktan dake kula da kudade na ofishin akanta janar na tarayya ya tabbatar da daukan matakin hakan na biyan kudaden.
Ya bayyana fatan ganin kudirin FG na gaggauta biyan kudade, domin dakatar da duk wata zanga zanga wanda hakan bai dace ba ga ma’aikatan da suka yi ritaya domin bata martaban kasan nan.
Hakan kuma masu karban fensho a Radion Tarayya na kasa FRCN da Gidan talabijin na kasa NTA dake Kaduna sun nuna damuwarsu game da zargin da ake yi cewa ana kokarin wulakanta shugabannin kungiyar ma’aikatan da suka yi ritaya karkashin jagorancin kwamaret Munkaila Ogunbote.
DAGA SULEIMAN KAURA