Leadership News Hausa:
2025-05-18@16:53:28 GMT

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Published: 18th, May 2025 GMT

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Samar da kyakkyawar sadarwa a tsakaninku

Yawan magana da sadarwa mai kyau na hana matsala girma. Idan wani abu ya dame ku, kada ku boye, ku gaya wa juna ta hanya mai dadi da girmamawa.

Gujewa kwatanta rayuwarku da ta wasu

Kowanne aure yana da nasa halin. Kada ku kwatanta rayuwarku da ta wasu, domin hakan yana iya jefa ku cikin damuwa ko rashin godiya.

Hana magulmata samun damar shiga tsakaninku

Magulmata da masu kyashi suna iya haddasa matsala a aure. Kada ku bari mutane su rarrashe ku da magana mara amfani ko su haifar da rashin fahimta.

Bai wa Juna hakkoki

Aure yana da hakkoki. Miji yana da nasa, haka ma mata. Ku rika bai wa juna hakkin da shari’a ta tanada, kamar girmamawa, kulawa, da soyayya.

Mutunta ra’ayin juna idan bai kauce hanya ba

Kowa yana da ra’ayi da tunani. Idan ba saba wa addini ko al’ada ya yi ba, yana da kyau a girmama ra’ayin juna domin samun zaman lafiya.

Rashin boyewa juna sirri

Ma’aurata ya kamata su rika yarda da juna. Idan aka fara boye sirri, hakan yana iya kawo rashin yarda da rashin zaman lafiya. Duk wata matsala, ku tattauna tare.

Allah ya sanya albarka cikin zamantakewar aure.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu

An samu bullar rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a dangantaka tsakanin Aljeriya da Faransa

Rikicin ma’aikatan harkokin diflomasiyya tsakanin Aljeriya da Faransa ya dawo kan gaba a fagen dakaddamar da ke tsakaninsu.

Rikici dai na kara kamari ne tsakanin Aljeriya da Faransa, tun daga rikicin korar ‘yan kasar Aljeriya daga Faransa zuwa rikicin korar ma’aikatan diflomasiyyar Faransa daga Aljeriya. Kasashen biyu sun tsaya a gaban nauyin tarihin mulkin mallaka ba tare da shawo kan shi ba. Aljeriya ta gayyaci mukaddashin jakadan Faransa domin sanar da shi aniyarta ta korar karin jami’an Faransa da ke aikin taimakon wucin gadi daga kasarta.

Wannan kiran ya biyo bayan maimaita cin zarafi mai tsanani da bangaren Faransa ya yi ne, yana wakiltar keta doka da aka kafa da kuma keta tsarin al’ada don nada ma’aikata a ofisoshin diflomasiyya da na ofishin jakadancin Faransa da aka amince da su a Aljeriya.

Akalla ma’aikatan Faransa 15 ne aka nada don gudanar da ayyukan diflomasiyya ko na ofishin jakadancin a kasar Aljeriya, ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba, gami da sanarwa a hukumance ko kuma ba da izini, kamar yadda ka’idoji da yarjejeniyoyin kasa da kasa suka bukata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso
  • Gidauniyar Mangal Ta Dauki Nauyin Yi Wa Mutum 12,300 Masu Cutar Kaba Aiki A Katsina
  • Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta
  • Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani
  • Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure
  • Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
  • Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista
  • Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci