Leadership News Hausa:
2025-11-14@21:53:30 GMT

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Published: 18th, May 2025 GMT

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Samar da kyakkyawar sadarwa a tsakaninku

Yawan magana da sadarwa mai kyau na hana matsala girma. Idan wani abu ya dame ku, kada ku boye, ku gaya wa juna ta hanya mai dadi da girmamawa.

Gujewa kwatanta rayuwarku da ta wasu

Kowanne aure yana da nasa halin. Kada ku kwatanta rayuwarku da ta wasu, domin hakan yana iya jefa ku cikin damuwa ko rashin godiya.

Hana magulmata samun damar shiga tsakaninku

Magulmata da masu kyashi suna iya haddasa matsala a aure. Kada ku bari mutane su rarrashe ku da magana mara amfani ko su haifar da rashin fahimta.

Bai wa Juna hakkoki

Aure yana da hakkoki. Miji yana da nasa, haka ma mata. Ku rika bai wa juna hakkin da shari’a ta tanada, kamar girmamawa, kulawa, da soyayya.

Mutunta ra’ayin juna idan bai kauce hanya ba

Kowa yana da ra’ayi da tunani. Idan ba saba wa addini ko al’ada ya yi ba, yana da kyau a girmama ra’ayin juna domin samun zaman lafiya.

Rashin boyewa juna sirri

Ma’aurata ya kamata su rika yarda da juna. Idan aka fara boye sirri, hakan yana iya kawo rashin yarda da rashin zaman lafiya. Duk wata matsala, ku tattauna tare.

Allah ya sanya albarka cikin zamantakewar aure.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

An umarci shugaban karamar hukumar da ya mika harkokin majalisar ga mataimakiyarsa, Mrs Victoria Okolo, har sai an kammala binciken.

 

Majalisar ta bai wa kwamitin binciken wata daya don kammala aikinsa tare da bayar da rahoto kan matakin da ya dace.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka November 12, 2025 Manyan Labarai An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano November 12, 2025 Manyan Labarai Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati na jefa makomar ilimi cikin hatsari — ASUU
  • Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
  • ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 
  • Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
  • MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a
  • Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa