Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso
Published: 18th, May 2025 GMT
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin dakatar da wani hadiminsa, Ibrahim Rabi’u nan take daga muƙaminsa.
Abba ya dakatar da hadimin ne wanda yake ɗauko masa rahoto a ma’aikatar sufuri, saboda wasu kalamai da ya furta kan tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo AwoniyiHakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Asabar, 17 ga watan Mayun 2025.
Dawakin Tofa ya ce Sakataren Gwamnatin Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ne ya fitar da sanarwar dakatarwar, wadda ta fara aiki nan take.
Baya ga haka, gwamnatin ta umarci a rubuta takardar neman bahasi daga hadimin da aka dakatar, bisa kalamansa masu tsauri da suka shafi raɗe-raɗin shirin sauya sheƙa da ake zargin Kwankwaso zai yi.
Gwamnatin ta kuma ja kunnen dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da kada su riƙa fitar da bayanai ba tare da izini ba, tana mai jaddada cewa duk wata sanarwa daga gwamnati sai an tabbatar da ita kafin a bayyana ta ga jama’a.
Gwamnatin ta bayyana cewa ba ta da hannu cikin kalaman da Rabi’u Ibrahim ya fitar, tana mai cewa wannan magana tasa ce kawai, kuma ra’ayinsa ne shi kaɗai, bisa wasu dalilai da shi kaɗai ya bar wa kansa sani.
Sanarwar ta kuma tunatar da al’umma cewa, Kwamishinan Yaɗa labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Wayya, shi ne kaɗai ke da hurumin yin magana a madadin gwamnatin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ibrahim Rabi u Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
“Abin takaici ne ace Nijeriya tana karancin Mlaman makaranta da suka kai 194,876 a makarantun gwamnati a fadin tarayyar Nijeriya. Halin da makarantunmu na Sakandare suke ciki shi ma lamarin bata canza zane ba. Rashin isassun Malamai shi ma lamarin abin damuwa ne domin kuwa sannu a hankali hakan zai iya shafi samar da ingantaccen ilimi a makarantunmu kamar yadda sakamakon hakan ba zai haifar da da mai ido ba cewar, Amba”.
Don haka ya ja kunnen Nijeriya cewa rashin isassun Malaman zai iya kawo cikas wajen kokarin da Nijeriya ta ke yi na cimma muradin ci gaba na 4 (SDG 4) da ya kunshi ingantaccen ilimi ba tare da wani bambanci ba, tsakanin gwamnatoci uku ba tare da wani bata lokaci ba a dauki mataki wanda ya dace.
Ya ci gaba da bayanin“Mu ma mun sa bakinmu wajen kira da babbar murya domin aikin koyarwa ya kasance abinda kowa yake sha’awar yi ne ga matasa masu tasowa. Dole ne gwamnati ta dauki yawan Malaman da suka kamata a dauka tare da yin la’akari da ingancinsu, domin a ci gaba da samar da ingantaccen ilimi a tsarin tafiyar da makarantunmu,”.
Duk alkawarin da aka yi na jin dadin Malaman makaranta ba a cika shi
Amba har ila yau nya nuna rashin jin sadinsa kan yadda aka kasa cika alkawuran jin dadin da aka yi wa Malaman makaranta’, duk kua da yake an yi alkawarin tun, a shekarar 2020. Yana iya tunawa zamanini mulkin tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya amince da wasu abubuwan da za su taimaka wadanda suka hada da tsarin albashi na musamman, da kuma irin lokacin da za su yi ritaya, da gidaje masu saukin kama haya a kauyuka amma suma ba a kai ga yinsu ba.
“Abin takaici ne cewar bayan lamarin shekarun da za’ayi ritaya daga aiki idan an kai an gabatar dasu, 65, abinda Jihohi 22 da Babban Birnin Tarayya Abuja, yawancin duk abubuwan da aka amince za ayi masu har yanzu ba a cika alkawarin ba. Muna kiran gwamnatin tarayya da Jihohi su cika dukkan aalkawuran za aka yi na game da jin dadin Malaman makarabta kamar yadda suke, saboda a samu damar dawo da irin martabar da aka san aikin koyarwa yana da ita kamar yadda ya ce,”.
Game da aiwatar da dolar mafi karancin albashi na kasa kamar yadda aka amince a shekarar 2024, Shugaban kungiyar Malamai ta kasa yace Jihohi goma basu cika ka’idar ba kamar yadda take ba, ta aiyatar da mafi karancin albashi, yayin da Jihohi hudu ma basu fara biya ba.
Kungiyar Malaman ta yi magana kan rashin ba shi bangaren ilimi kuaddaen da suka dace a bashi, inda suka ce Nijeriya ta ci gaba da kasancewa a baya kan yadda mizani na kasa da kasa wato shawarar da aka yanke na kason da aka amincewa bangaren ilimi, inda aka ce a rika ware ma shi bangaren kashi 4–6 na kudaden da suk shigo ma kasa a duk shekara GDP oko kuma 15–20 na gaba dayan kasafin kudin zuwa ga bangaren ilimi.
Amba ya ce ya zuwa wayan Maris na shekarar 2024, kamar Naira biliyan 54 da aka ware ma bangaren ilimin bai daya (UBE) har yanzu ba a samu amsar ko kwabo ba saboda rashin bada kaso da akace a rika badawa wato Jihohi da Babban Birnin Tarayya Abuja.
“Rashin yadda Jihohi suka ki biyan kason na sun a kudi kaman a kai ga basu tallafin na UBEC, hakan ya kara gurgunta rashin bunkasa ilimin na bai daya, da kuma taimakawa tsare= tsaren da za su jawo hankalin Malamai ya raja’a kan aikin koyarwa kamar yadda ya ce,”.
Hakanan ma kungiyar bata ji dadin da wani kokarin na gwamnatin Jihar Edo ban a ta mika wasu makarantun gwamnati ga Hukumomi da ba nata ba, da kuma kungoyoyi masu zaman kansu, abinda ta kalla a matsayin wasu matakai ne da za su kawo cikas wajen cimma burin samar da ilimi kyauta.
Kungiyar ta ce wadannan matakan suna kawo barazana wajen samar da adalci, musamman ma ga irin wadanda basu da halin ba ‘ya’yan nasu ilimi, kamar ‘yanmata, yara masu kulawa ta musamman, da kuma wadanda suke can kauyuka.
Ta yi kira da gwamnatin Jihar Edo ta daukai matakan da suka kamata kamar yadda tsarin mulki ya tanadar wajen samar da ilimi kamar yadda lamarin yake yadda doka ta tanadar.
Kungiyar ta yi magana ne kan muhimmancin kulawa jin dadin Malamai,inda ta yi tunatarwa da rahoton shekarar 2008 kan kungiyar ma’aikata ta duniya da kuma hukumar ILO/UNESCO, in da aka yi bayanai kan muhimmancin jin dadin Malamai ’ a matsayin irin abubuwan da suke jan mutane na sha’awar aikin koyarwa da kuma ci gaba da zaman kwararrun a makarantu.
Mr. Bobby Winful na Kwalejin gwamnatrin tarayya ta maza da je Abuja Abuja, ya dora alhakin rashin Malamai kan wadansu abubuwa, da suka hada da rashin kulawa dajin dadin Malamai, da kuma karancin Malaman d aka amince da su masu lasin na aikin koyarwa.
“Muna karancin Malamai ne saboda yadda ba a kulawa da hakkin Malamai bare jin dadinsu abin ba wani abin azo a gani bane. Sau da yawa wasu wuraren ba ma a biyan albashin. Abin mamaki ace wai wasu Malaman suna zuwa aiki har tsawon shekara uku ba tare da albashi ba. Hakan shi yasa ake samun raguwar Malamai masu takardar shedar da aka amince sun cancanta su koyar, saboda yawancin dalibai a Jami’a basu sha’wara karanta darasin ilimi, duk wannan ba domin komai ba saboda babu wasu abubuwan da za su ja hankali a sharuddana aikin nasu, ba wata maganar jin dadinsu da kuma ,aganar albashi kamar yadda ya yi karin bayani,”.
Shugabar makarantun Chalcedony, Dakta. Mary Chinwuba, ta bayyana babban dalilin da ya kawo karancin Malamai a Nijeriya saboda babu wasu abubuwan jan hankali daga cikin sharuddan aikinsu ba, don haka ta yi kiran da ayi gaggawar inganta sharuddan aikinsu da kuma jin dadinsu.
Gwamnati ta yi kira ga Malaman makaranta da su hada kansu
A na shi jawabin Minisatan ilim, Dakta. Maruf Olatunji Alausa, ya kara jaddada manufar gwamnati ta sanin cewa Malamiai sune babban tubali wajen gina kasa da ci gabantar.
Ya yi karin haske “Malamai sune ginshikin ci gaban al’umma hakanan kuma babbar hanyar bi zuwa wajen bunkasa al’umma da kuma kasa.Don haka idan an yiwa Malamai wani ihisani hakan baya nuna ta hakan ne aka san da su ba, manufa kuwa sun kasance tamkar zuba jari ne domin samun ingantaccen ilimi, karuwar da dalibi zai yi, da kuma yadda kasa za ta kasance cewar Dakta Alausa.
Dakta Alausa ya bayyana hanyoyi masu yawa domin inganta shi aikin koyarwar wadanda suka hada da, tsarin ilimin Malami na kasa, tsarin sa ido na hukumar al’amuran Malamai, ci gaban bunkasa kwarewar aikin Malamta na NTI, da kuma irin yadda hukumar ilimin bai daya take taimakawa shi bangaren na ilimi.
An karrama Gwamnoni hudu saboda inganta jin dadin Malaman makaranta’
An karrama gwamnoni hudu saboda yadda suke taimakawa harkar ilimi ya wuce duk irin tunanin da mutum zai yi, saboda bunkasa jin dadin Malamai da yadda lkamarin ilimi yake a Jihohin nasu.
An yi bikin karramar ne, a Eagle Skuare, Abuja, gwamnonin da aka karrama sun hada da Katsina, Adamawa, Kogi, da kuma Delta saboda tsare-tsaren da suka bullo da su wadanda za su karawa Malamai kwarin ne su rungumi aikin nasu da gaskiya, da kuma gyara hanyoyin da ake amfani da su wajen koyarwa ko kuma a takaice yanayin da yafi dacewa da koyarwa da koyo.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA