Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso
Published: 18th, May 2025 GMT
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin dakatar da wani hadiminsa, Ibrahim Rabi’u nan take daga muƙaminsa.
Abba ya dakatar da hadimin ne wanda yake ɗauko masa rahoto a ma’aikatar sufuri, saboda wasu kalamai da ya furta kan tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo AwoniyiHakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Asabar, 17 ga watan Mayun 2025.
Dawakin Tofa ya ce Sakataren Gwamnatin Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ne ya fitar da sanarwar dakatarwar, wadda ta fara aiki nan take.
Baya ga haka, gwamnatin ta umarci a rubuta takardar neman bahasi daga hadimin da aka dakatar, bisa kalamansa masu tsauri da suka shafi raɗe-raɗin shirin sauya sheƙa da ake zargin Kwankwaso zai yi.
Gwamnatin ta kuma ja kunnen dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da kada su riƙa fitar da bayanai ba tare da izini ba, tana mai jaddada cewa duk wata sanarwa daga gwamnati sai an tabbatar da ita kafin a bayyana ta ga jama’a.
Gwamnatin ta bayyana cewa ba ta da hannu cikin kalaman da Rabi’u Ibrahim ya fitar, tana mai cewa wannan magana tasa ce kawai, kuma ra’ayinsa ne shi kaɗai, bisa wasu dalilai da shi kaɗai ya bar wa kansa sani.
Sanarwar ta kuma tunatar da al’umma cewa, Kwamishinan Yaɗa labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Wayya, shi ne kaɗai ke da hurumin yin magana a madadin gwamnatin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ibrahim Rabi u Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
Ana zargin wata amarya da yi wa angonta yankan rago kwana uku bayan ɗaurin aurensu a Jihar Katsina.
Angon mai suna Abubakar Abdulkarim da aka fi sani da Dan Gaske, ana zargin ya rasa ransa bayan da amaryar ta yi amfani da wuƙa wajen halaka shi.
Shaidu sun ce ta yi masa mummunan rauni a wuya wanda ya yi sanadiyyar mutuwarsa.
Angon da amaryarsa suka daura aure ne a ranar Alhamis, 18 ga Nuwamba, 2025, amma farin cikin aure ya rikide zuwa makoki a ranar Lahadi da rana lokacin da lamarin ya faru.
Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaWani ɗan uwansa mai suna Aminu Danladi ya ce cewa sun yi taro da marigayin da safiyar ranar, suna shirya ziyarar ’yan uwansu da za a kai da yamma.
Ya ce daga baya ango ya koma gida domin shiri, sai kuma aka ji labarin an same shi kwance a cikin jini babu rai.
Aminu ya kuma ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa auren dole ne aka yi wa ma’auratan, inda ya tabbatar da cewa dangantakarsu ta kasance lafiya kafin aure.
Majiyoyi sun ce matar, ’yar asalin Katsina, ta taɓa yin aure a baya, abin da ake zargin dangin mijin ba su sani ba.
An ce bayan faruwar lamarin amaryar ta ruɗe inda ta je gidan maƙwabta tana neman abinci. Wannan hali ya sa tsofaffin mata zargin akwai matsala, suka bi ta gida inda suka tarar da gawar mijin, suka kuma sanar da jami’an tsaro.
Rundunar ’Yan Sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara gudanar da bincike a kai.
Kakakin ’yan sanda na jihar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargi da hannu a lamarin, kuma bincike na ci gaba.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Katsina, CP Bello Shehu, ya tabbatar da cewa za a gudanar da bincike mai zurfi, tare da kira ga jama’a da su bayar da bayanai masu amfani.