Aminiya:
2025-07-03@02:24:40 GMT

Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso

Published: 18th, May 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin dakatar da wani hadiminsa, Ibrahim Rabi’u nan take daga muƙaminsa. 

Abba ya dakatar da hadimin ne wanda yake ɗauko masa rahoto a ma’aikatar sufuri, saboda wasu kalamai da ya furta kan tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Kwale-kwale ya nutse da mutum 37 a Kwara Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Asabar, 17 ga watan Mayun 2025.

Dawakin Tofa ya ce Sakataren Gwamnatin Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ne ya fitar da sanarwar dakatarwar, wadda ta fara aiki nan take.

Baya ga haka, gwamnatin ta umarci a rubuta takardar neman bahasi daga hadimin da aka dakatar, bisa kalamansa masu tsauri da suka shafi raɗe-raɗin shirin sauya sheƙa da ake zargin Kwankwaso zai yi.

Gwamnatin ta kuma ja kunnen dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da kada su riƙa fitar da bayanai ba tare da izini ba, tana mai jaddada cewa duk wata sanarwa daga gwamnati sai an tabbatar da ita kafin a bayyana ta ga jama’a.

Gwamnatin ta bayyana cewa ba ta da hannu cikin kalaman da Rabi’u Ibrahim ya fitar, tana mai cewa wannan magana tasa ce kawai, kuma ra’ayinsa ne shi kaɗai, bisa wasu dalilai da shi kaɗai ya bar wa kansa sani.

Sanarwar ta kuma tunatar da al’umma cewa, Kwamishinan Yaɗa labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Wayya, shi ne kaɗai ke da hurumin yin magana a madadin gwamnatin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ibrahim Rabi u Jihar Kano Rabi u Musa Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina

Bayanai daga makusantan fitaccen attajirin nan da ya riga mu gidan gaskiya, Alhaji Aminu Ɗantata sun nuna cewa an ɗage jana’izarsa da aka shirya gudanarwa bayan sallar La’asar a ranar Talata.

Yanzu an mayar da jana’izar zuwa bayan Magariba a haramin birnin Madina.

Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu

A wata zantawa da ya yi da BBC, Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya bayyana cewa tuni gawar Alhaji Aminu ta isa birnin na Madina.

“Alhamdu lilLah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince,” in ji Mustapha Junaid.

Wannan dai shi ne karo na biyu da ake sauya lokacin jana’izar mamacin wanda da farko aka ruwaito cewa za a gudanar a ranar Litinin kamar yadda Ministan Labarai, Mohammed Idris ya tabbatar.

A karon na farko dai, Ministan ya ce an ɗage jana’izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madina.

A cewarsa, “akwai ƙa’idoji da Gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan yadda za a shigar da gawa domin yi mata jana’iza a ƙasar.

“Saboda haka yanzu ana nan ana ta cike-ciken takardu tsakanin Gwamnatin Saudiyya da iyalan mamacin,” in ji Ministan.

Mohammed Idris ya ce idan an kammala za a ɗauko gawar daga Hadaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Saudiyya.

Ya ƙara da cewa tuni ofishin jakadancin Nijeriya a Saudiyya da iyalan mamacin suka kammala shirye-shiryen jana’izar.

Alhaji Aminu Ɗantata yana da burin binne shi a birnin Madina, inda kuma ’yan uwansa suka nemi amincewar hukumomin Saudiyya game da buƙatar kuma aka sahale musu.

Tun da safiyar Litinin ce tawagogin Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin Kano suka tafi Saudiyyar domin halartar jana’izar da aka shiryi yi a ranar Litinin din.

Daga cikin tawagogin akwai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Gwamnan Jigawa, Umar Namadi da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

Haka kuma, akwai tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da kuma malamai irinsu Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da Dakta Bashir Aliyu.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Asabar da ta gabata ce dai bajimin ɗan kasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
  • Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
  • Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  • Jana’izar Aminu Ɗantata: Abba da Sarki Sanusi sun tafi Saudiyya