Aminiya:
2025-11-27@22:28:47 GMT

Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai

Published: 18th, May 2025 GMT

A farkon wannan sati ne wata takardar neman raba Masarautar Katsina ta bayyana, wadda take neman a ƙirƙiro ƙarin masarautu uku da suka haɗa da ƙarin sarki mai daraja ta ɗaya da mai daraja ta biyu da kuma mai daraja ta uku.

Takardar wadda aka gani da tambarin da ke nuna alamar an miƙa ta ga Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta tayar da ƙura, inda ake ta musayar yawu kan abin da ta ƙunsa da kuma abin da zai iya biyo baya.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Wakilinmu ya gano cewa takardar, wadda kafar yaɗa labarai ta Katsina Times ta fara wallafa wa a kafofin sada zumunta, ta fito ne daga wata ƙungiya mai fadi-tashin ganin an ɗaga darajar wasu garuruwa da hakimansu.

Rashin ganin sunayen waɗanda suka sanya wa takardar hannu shi ma ya sa an yi ta tambayoyi game ainihin manufar waɗanda suka rubuta ta da kuma hakikanin manufarsu.

Dalilin neman raba masarautar Katsina

Masu neman a raba Masarautar Katsina sun kafa hujja ad wasu dalilai na tarihi a matsayin misalan da suke ganin sun wadatar a naɗa sabbin sarakuna masu daraja ta ɗaya da masu daraja ta biyu da masu daraja ta uku, mai maimakon Sarkin Katsina da a halin yanzu shi ne kaɗai sarkin yanak.

Sun kawo misali da yankin Kurfi wanda yanzu karamar hukuma ce amma ba ta da sarki mai daraja ta biyu ko ta uku.

A cewarsu a da can Kurfi kasa ko yanki ne mai zaman kansa da ke karbar umarni daga Shehu Danfodiya.

Kazalika, sun ce, a lokacin turawan mulkin mallaka, Gwamna Lugga ya nada Kaura Amah Sarauta a matsayin mayakin da ya tsare sashen Dankama daga maharan da ke fitowa nan sashen, amma Kaura Amah ya ki amsar tayi ya ce, a bar shi a matsayin shi na mayaki.

Saboda haka suke ganin a sake bayar da wannan sarauta ko da a matsayin mai daraja ta uku ce.

Masu neman sabbin masarautun sun ce, hatta yankin Maska yana buƙatar a yi masa sarki mai daraja ta ɗaya, duba da irin rawar da Sarkin Maska ya taka, wanda ya yi zamani da Sarkin Katsina Muhammadu Korau, wanda shi ne sarki Bahaushe Musulmi na farko da ya yi sarautar ta Katsina.

Ta ci gaba da cewa hatta da Malunfashi da Kafur sun cancanci a ba su sarki mai daraja daya, idan aka yi la’akari da matsayi da kuma tarihin yankunan musamman abubuwan da Malan Dudi Zuri’ar Danejawa ya taka wajen kafa Malumfashi da Kafur.

Ƙungiyar ta kuma waiwayi ita kanta Masarautar Katsina a matsayinta na masarauta tilo da ake da ita mai sarki mai daraja ta ɗaya.

Ta tuno tarihin mutanen nan uku da suka je karbo tuta a hannun Shehu Danfodiyo — Ummarun Dallaje da Malam Na Alhaji da da Ummarun Duniyawa — wadanda a cewar kungiyar, kowanne daga cikinsu yana mulkin yankinsa, kuma suna karbar umarni ne daga wajen shi Shehun Danfodiyo.

Wato, suna mulkin haɗaka wanda daga baya turawan mulkin mallaka suka tilasta masu zama karkashin sarki guda, kamar yadda masu neman wannan bukata suka ce tarihi ya nuna.

Akan haka suke ganin yana da kyau a fitar da sarki mai daraja ta ɗaya a cikinsu yayin da sauran biyun za su zamo sarakuna masu daraja ta biyu, wato, yankin ’Yandakawa da kuma Ummarun Duniyawa wanda ya fara zama a garin Zandam.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu cewa takardar ta fito ne daga wata kungiya da ke da hedikwata a Funtuwa, karkashin jagorancin wani mai suna Salisu Idris Funtuwa.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin kungiyar da ake zargi amma abin ya ci tura.

‘Mun dade muna neman a ba mu masarauta’

Game da yadda jama’ar jihar ke kallon wannan lamari, Malam Ibrahim wani mazaunin garin Funtuwa da wakilinmu ya tuntuba ya ce, “ai mu tuni muka so a yi mana sarki a wannan yanki duba da irin tarihin yankin.

“Mun so a ce an yi mana Sarkin Kudu mai daraja ta daya ko kuma ita wannan hakimci da ake kira da Sarkin Maska ta koma sarki ne mai wukar yanka, ba wannan suna ba hakimi ba.”

Abin da ya faru ya Kano ya ishe mu darasi

Amma Alhaji Usman, ya bayyana cewa “Wannan neman raba kan al’umma ne kawai ba hadin kai ba.

“Su masu wannan tunani ba su duba halin da makwabciyarmu Jihar Kano take ciki a yanzu kan maganar rikicin masarautun?

“A matsayin jiha baki daya fa ke nan da aka samu wannan matsala, to ina ga wani sashe daga cikin jihar?”

Alhaji Usman ya kara da cewa, “idan har suna maganar tarihi ne, sai mu ce a mayar wa da Hausawa sarautarsu domin Hausawa ne suka fara yin sarauta a Katsinar kafin Fulani su shigo.

“Kuma tun wancan lokacin akwai wurare da yawa inda aka haɗe su suka zama daya da kuma inda aka yi musaya.

“Misali, ’Yandoto da Kankara, ai da can ’Yandoto a karkashin Katsina take ita kuma Kankara tana karkashin Zamfara. Lokacin Sarki Dikko aka yi wannan musayar. Su ma sai a ce kowa ya kama gabansa.

“Idan kuma muka koma can Kudancin Katsinar, ita kanta Funtuwar yaya aka same ta? Garin Sabuwa wa ya samar da shi? Sannan mu dawo shiyyar Daura, sai a ce, a mayar da sarautar a garin Zango tunda can ne tushe kuma daga can ake nado sarki,” in ji Alhaji Usman.

Ana zargin gwamnati

Shi kuma wani da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “gaskiya ina zargin akwai wata balulluba daga wasu mukarraban gwamnati ko ita kanta gwamnatin.

“Dalili, wannan batun bai fito ba sai bayan da shugaban kasa ya zo kuma aka samu akasin da aka samu na zuwan sarkin wajen daurin auren ’yar gwamna.

“Kowa ya ga yadda wani ya rubuta takarda yana neman a hukunta sarki saboda karya kofa da dogarawansa suka yi don ya shiga masallacin da ake taron bayan da jami’an tsaron shugaban kasa suka yi yunkurin hana sarki shiga bisa hujjar shugaban kasa ya riga ya shigo masallacin an rufe kofa.

“Sannan akwai batun karin hakimai da gwamnatin jihar za ta yi a masarautun biyu na Katsina da Daura, amma a masarautar ta Katsina suka fi yawa.

“Wadannan duk wasu alamu ne da nake ganin cewa, gwamnati na da sha’awar ganin an farfasa masarautar.

“Wata hujja da muka gani ta cewar, wai sarki tun bayan hawansa bai yi rangadin da sarakunan baya suka rika yi ba, sai ya manta kullum cigaba ake samu.

“Kuma ana sara ana duban bakin gatari. Sarkin nan mutun ne mai tausayin talakawa baya son aza masu wani nauyi.

“Amma duk inda aka yi wani abu muddin aka gaya masa, yana zuwa shi da kansako ya tura wakili.”

Muna bincike kan takardar —Majalisa

Duk da cewa gwamnatin jihar ba ta ce koomai game da wannan batu ba, amma dangane da batun miƙa wannan takadar majalisar dokokin jahar wadda a aka ga tambarinta a kai, mai magana yawun Kakakin majalisar dokokin jihar ta Katsina, Honarabil Nasiru, Aminu Magaji, ya ce, har zuwa lokacin da wakilinmu ya tuntube shi, babu wata takarda mai kama da irin wannan, ba ma ita ba da aka kawo majalisar.

Ya bayyana cewa, majalisar ta kaddamar da binciken yadda aka buga wa takardar da ke yawo a gari tambari da sunanta.

“Yanzu in aka tuna, ana satar sanya hannun mutun a takarda, yin amfani da tambarin karya da sauran irinnsu.

“Sannan a wannan takarda, babu sunan wanda ko wadanda suka rubuta, ta balle sunaye da sa hannu.

“Yadda ka gan ta a soshiyal midiya haka mu ma muka gani,” in ji Aminu Magaji, mai magana da yawon kakakin majalisar dokokin jihar Katsina.

Duk wani kokari na ji daga Masarautar Katsina ya ci tura, kuma har zuwa lokacni da muka kamamla hada wannan labari babu wani abu da ya fito daga gareta a hukumance.

Sai dai wasu na kusa da ita sun ce babu mamakin ji ko ganin irin wannan batu musamman ga masarauta.

“Idan har za a dubi tarihi da kuma yanayi, ai an san Masarautar Katsina haka ya kamace ta ta tsaya. Duk wuraren da ake magana wa ya haifar ko ya raya su?

“Kada mu ɗauka da nisa, abin da Marigayi Sarki Muhammadu Dikko ya yi a wannan masarauta duk arewa babu sarkin da ya yi. Mu kawai dai muna kallon wadanda suke neman kawo wannan matsalar walau sun yi don neman suna ko wani abu can na biyan bukata, musamman a siyasance”, inji wani da ya nemi a sakaya sunansa a yayin da wakilinmu ya tuntube shi a wayar salula

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Masarautar Katsina sarki mai daraja ta ɗaya raba Masarautar Katsina daraja ta biyu masu daraja ta wakilinmu ya wa takardar

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya kafa tarihin zama mutumin da ya fi kowa yawan zuri’ar da ta haddace Alkur’ani a tarihin duniya.

Alkaluma sun nuna cewa shehin malamin, wanda a kwanan nan ya cika shekara 100 a duniya, yana da ’ya’ya da jikoki da ma tattaba-kunne kusan 300 da suka haddace Alkur’ani.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya

A cewar kundin tattara bayanai na Cholan Book Of World Records, wadanda suka karrama malamin da lambar yabo, Sheikh Dahiru Bauchi shi ne mutum na farko da ya taba samun irin wannan baiwar.

Bayanai sun nuna fitaccen malamin yana da ’ya’ya 95 da jikoki 406 da tattaba-kunne 100. Daga cikin wannan adadin, ’ya’yansa 77 da jikoki 199 da kuma tattaba-kunne 12 ne suka haddace Alkur’anin.

A ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamban 2025 ce Allah ya yi wa shehin malamin rasuwa a Bauchi.

Yana daga cikin Halifofin Sheikh Inyass

Sheikh Darihu Bauchi ne daga cikin halifofin Shehu Ibrahim Inyass, Halifan Darikar Tijjaniyya, bayan wanda ya assasa ta, wato Sheikh Ahmadu Tijjani.

Yana daga cikin manyan malaman Musulunci a Najeriya, shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Koli da ke bayar da Fatawar Musulunci a Najeriya sannan babban jigo ne a Darikar Tijjaniya a Najeriya da ma Afirka.

A zantawarsa da ’yan jarida shekarun baya a Bauchi, Sheikh Dahiru ya ba da takaitaccen tarihinsa, inda ya ce, “Tarihina dai ni Bafulatani ne, dukanin kakannina hudu Fulani ne, domin kowane mutum yana da kakanni hudu — ta wajen mahaifinsa biyu, ta wajen mahaifiyarsa biyu.

“To ni dukanin kakannina Fulani ne babu inda muka hadu da wata kabila ta kowace fuska. Mu Fulanin Bauchi ne a lokacin da Jihar Bauchi take hade da Jihar Gombe.

“Bayan da aka raba Jihar Bauchi da Jihar Gombe, sai muka zama mu Fulanin Jihar Bauchi ne, a lokaci guda kuma Fulanin Jihar Gombe ne.

“Ta wajen mahaifina ni Bafulatanin Jihar Bauchi ne, ta wajen mahaifiyata ni Bafulatanin Nafada ne da ke Jihar Gombe.

“An haife ni ne a watan Janairun 1927, wanda ya yi daidai da watan Muharram 1346 Bayan Hijira, a ranar Laraba.”

‘Yadda na mayar da karatun Alkur’ani sana’ata’

Ya ce abin da ya fi ba shi sha’awa a rayuwarsa shi ne irin yadda ya mayar da Alkur’ani sana’arsa da kuma yadda ya rungumi Darikar Tijjaniya ta zama rayuwarsa.

“A duk lokacin da nake hutu ina shagaltuwa ne da karatun Alkur’ani da karanta Salatul Fatihi da tasbihi da istigfari da salatin Annabi (SAW) da sauran zikirori,” in ji shi.

Kwarewar Sheikh Dahiru Bauchi

Da aka tambaye shi kan fannonin ilimin da ya fi kwarewa, shehin malamin ya ce, “Na yi dukkan karatuna na addini a karkashin kulawar mahaifina, har na haddace Alkur’ani kuma ta hannunsa ne na karbi Darikar Tijjaniya.

“Shi mahaifina ya karbi Darikar Tijjaniya ne ta hannun wani mutum mai suna Alhaji Gwani Abba, daga baya sai mahaifina ya ba ni izinin na tafi duk inda nake so domin zurfafa ilimina na addini da haddar Alkur’ani mai girma.

“Bangaren da na fi kwarewa sosai shi ne Alkur’ani, daga nan kuma sai bangaren Tafsiri, a nan malaman Tafsiri sun ce lallai na iya tafsiri inji su.

“Sai kuma bangaren Ma’arifa, ma’anar Ma’arifa shi ne ilimin (gyaran) zuciya wanda ake kiran sa Tlimin Tarbiyya.

“A nan ma masu irin ilimin kan ce ina da sani a fannin. Shehu Ibrahim ya ce lallai na san wannan bangare.

“Sauran ilimomi kuma ina tattabawa, su Hadisi da Lugga da Li’irabi da Tasrifi da Fikihu, duk ina tattabawa,” inji shi.

‘Dalilin da nake buga misali kan duk tambayar da aka yi min’

Da aka tambayarsa cewa jama’a na mamakin yadda idan aka yi masa tambaya sai ya ba da misali kafin ya bayar da gundarin amsar, sai ya ce, “Wato shi buga misali wata runduna ce ta Allah mai shigar da ilimi cikin kawunan mutane.

“Idan ka kawo amsar magana sai ka buga misalin da za ta hau kan mutane domin fahimtar da su.

“Shi buga misali yana jawo hankali a fahimci mene ne aka fada. Misali na da matukar muhimmaci wajen ba da amsa.”

Shehin malamin ya zama masanin Tafsirin Alkur’ani Mai Girma wanda ya samu lambobin yabo a wannan bangaren.

Ya kuma samu digirin girmamawa a bangarori daban-daban a Najeriya da ma kasashen waje.

Jami’ar Tarayya da ke Lafiya a Jihar Nasarawa ta ba shi lambar yabo ta Digirin girmamawa, sannan Gwamnatin Tarayya ta ba shi lambar girmamawa ta kasa ta OFR.

Nasarorin Sheikh Dahiru Bauchi

Ga wasu daga cikin nasarorin da Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya samu a tsawon shekarunsa:

Ya musuluntar da dubban mutane A duk lokaci bayan lokaci yakan karanta Alkur’ani kuma yana yin saukar Alkur’ani a kwana biyu Ya ba da lazumin Darikar Tijjaniyya wa dubban mutane da dama a fadin duniya Ya kafa makarantun haddar Alkur’ani sama da 1500 a Najeriya da sassan Afirka Sama da mutum 140,924 sun haddace Alkur’ani a makarantunsa a fadin Najeriya Karkashin gidauniyasa, an gina dakunan karatu guda 133,060 a Arewacin Najeriya Mutum ne mai kishin kasarsa Najeriya wanda aduk lokacin da ya bude baki zai yi addu’a sai ya roki Allah Ya ba kasar zaman lafiya da kwanciyar hankali

Bugu da kari, malamin yana cikin wadanda suka fi kowa dadewa suna tafisirin Alkur’ani da watan azumin Ramadan.

Masallacin da yake tafsirin da ke unguwar Tudun Wada a Kaduna, na daya daga cikin manyan masallatan da ke cikin garin, kuma za a iya cewa a tsawon shekaru, malamin yakan zauna a garin kusan fiye da a ko ina.

Wani bincike da wani wanda yayi Nazari kan rayuwar malamin ya kuma rubuta littafi a kansa mai suna Shehu Dahiru Bauchi Ginin Allah, shekaru uku da suka wuce, Farfesa Khalid Abdullahi Zaria, ya ce

Daya daga cikin almajiran shehin, Mallam Ahmad Tijjani Kolo, ya ce a yanzu an sami karin mahaddata a cikin zuri’arsa, inda yanzu suka doshi 300. Ya ce da wahala a sami mai irin wannan a tarihi.

Shugaban Kungiyar Daliban Sheikh Dahiru Bauchi, Mallam Ibrahim Imam Ismaila, ya ce a tarihi babu wanda ya taba samun irin baiwarsa.

‘Rayuwarsa gaba daya makaranta ce’

Shi kuwa Daraktan  Wakafi a Hukumar Shari’a na Jihar Bauchi, Mallam Ahmad Tijjani Sa’id, ya ce rayuwar shehun malamin gaba dayanta makaranta ce.

Ya kuma ce malamin ya yi tafiya daga Arewa har kasashen Kudu a kan jaki da doki don yada addinin.

Sannan ya yi tafiya a kan keke zuwa kauyuka da dama kamar Tafawa Balewa da yankunan Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Yamma don yada addinin Musulunci.

‘Gidajensa 1,000 da ake zama kyauta’

Malam Ahmad Tijjani Sa’id ya ci gaba da cewa babu abin mamaki cikin sha’anin malamin kamar yadda yake daukar nauyi ba tare da jin tsoron hidima ba.

“Yana da gidaje fiye da dubu daya a fadin kasar nan, amma ba inda ake haya, bayin Allah masu neman ilimi yake zubawa a ciki kyauta.

“Jama’ar da yake ciyarwa Allah kadai Ya san adadinsu. A kullum idan Shehi zai fito zai sallami baki fiye da 3,000 da suka zo ziyarar sa daga ciki da wajen Najeriya, kuma za ka samu dalibansa ya yi musu auren fari ya musu suna kuma bai gaji ba.

“Ya maka mace ta biyu ya dauki nauyinku. Ire-iren wadannan halaye na Shehi da wuya ka samu wanda zai iya yin haka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza