Aminiya:
2025-08-17@11:18:44 GMT

Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai

Published: 18th, May 2025 GMT

A farkon wannan sati ne wata takardar neman raba Masarautar Katsina ta bayyana, wadda take neman a ƙirƙiro ƙarin masarautu uku da suka haɗa da ƙarin sarki mai daraja ta ɗaya da mai daraja ta biyu da kuma mai daraja ta uku.

Takardar wadda aka gani da tambarin da ke nuna alamar an miƙa ta ga Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta tayar da ƙura, inda ake ta musayar yawu kan abin da ta ƙunsa da kuma abin da zai iya biyo baya.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Wakilinmu ya gano cewa takardar, wadda kafar yaɗa labarai ta Katsina Times ta fara wallafa wa a kafofin sada zumunta, ta fito ne daga wata ƙungiya mai fadi-tashin ganin an ɗaga darajar wasu garuruwa da hakimansu.

Rashin ganin sunayen waɗanda suka sanya wa takardar hannu shi ma ya sa an yi ta tambayoyi game ainihin manufar waɗanda suka rubuta ta da kuma hakikanin manufarsu.

Dalilin neman raba masarautar Katsina

Masu neman a raba Masarautar Katsina sun kafa hujja ad wasu dalilai na tarihi a matsayin misalan da suke ganin sun wadatar a naɗa sabbin sarakuna masu daraja ta ɗaya da masu daraja ta biyu da masu daraja ta uku, mai maimakon Sarkin Katsina da a halin yanzu shi ne kaɗai sarkin yanak.

Sun kawo misali da yankin Kurfi wanda yanzu karamar hukuma ce amma ba ta da sarki mai daraja ta biyu ko ta uku.

A cewarsu a da can Kurfi kasa ko yanki ne mai zaman kansa da ke karbar umarni daga Shehu Danfodiya.

Kazalika, sun ce, a lokacin turawan mulkin mallaka, Gwamna Lugga ya nada Kaura Amah Sarauta a matsayin mayakin da ya tsare sashen Dankama daga maharan da ke fitowa nan sashen, amma Kaura Amah ya ki amsar tayi ya ce, a bar shi a matsayin shi na mayaki.

Saboda haka suke ganin a sake bayar da wannan sarauta ko da a matsayin mai daraja ta uku ce.

Masu neman sabbin masarautun sun ce, hatta yankin Maska yana buƙatar a yi masa sarki mai daraja ta ɗaya, duba da irin rawar da Sarkin Maska ya taka, wanda ya yi zamani da Sarkin Katsina Muhammadu Korau, wanda shi ne sarki Bahaushe Musulmi na farko da ya yi sarautar ta Katsina.

Ta ci gaba da cewa hatta da Malunfashi da Kafur sun cancanci a ba su sarki mai daraja daya, idan aka yi la’akari da matsayi da kuma tarihin yankunan musamman abubuwan da Malan Dudi Zuri’ar Danejawa ya taka wajen kafa Malumfashi da Kafur.

Ƙungiyar ta kuma waiwayi ita kanta Masarautar Katsina a matsayinta na masarauta tilo da ake da ita mai sarki mai daraja ta ɗaya.

Ta tuno tarihin mutanen nan uku da suka je karbo tuta a hannun Shehu Danfodiyo — Ummarun Dallaje da Malam Na Alhaji da da Ummarun Duniyawa — wadanda a cewar kungiyar, kowanne daga cikinsu yana mulkin yankinsa, kuma suna karbar umarni ne daga wajen shi Shehun Danfodiyo.

Wato, suna mulkin haɗaka wanda daga baya turawan mulkin mallaka suka tilasta masu zama karkashin sarki guda, kamar yadda masu neman wannan bukata suka ce tarihi ya nuna.

Akan haka suke ganin yana da kyau a fitar da sarki mai daraja ta ɗaya a cikinsu yayin da sauran biyun za su zamo sarakuna masu daraja ta biyu, wato, yankin ’Yandakawa da kuma Ummarun Duniyawa wanda ya fara zama a garin Zandam.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu cewa takardar ta fito ne daga wata kungiya da ke da hedikwata a Funtuwa, karkashin jagorancin wani mai suna Salisu Idris Funtuwa.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin kungiyar da ake zargi amma abin ya ci tura.

‘Mun dade muna neman a ba mu masarauta’

Game da yadda jama’ar jihar ke kallon wannan lamari, Malam Ibrahim wani mazaunin garin Funtuwa da wakilinmu ya tuntuba ya ce, “ai mu tuni muka so a yi mana sarki a wannan yanki duba da irin tarihin yankin.

“Mun so a ce an yi mana Sarkin Kudu mai daraja ta daya ko kuma ita wannan hakimci da ake kira da Sarkin Maska ta koma sarki ne mai wukar yanka, ba wannan suna ba hakimi ba.”

Abin da ya faru ya Kano ya ishe mu darasi

Amma Alhaji Usman, ya bayyana cewa “Wannan neman raba kan al’umma ne kawai ba hadin kai ba.

“Su masu wannan tunani ba su duba halin da makwabciyarmu Jihar Kano take ciki a yanzu kan maganar rikicin masarautun?

“A matsayin jiha baki daya fa ke nan da aka samu wannan matsala, to ina ga wani sashe daga cikin jihar?”

Alhaji Usman ya kara da cewa, “idan har suna maganar tarihi ne, sai mu ce a mayar wa da Hausawa sarautarsu domin Hausawa ne suka fara yin sarauta a Katsinar kafin Fulani su shigo.

“Kuma tun wancan lokacin akwai wurare da yawa inda aka haɗe su suka zama daya da kuma inda aka yi musaya.

“Misali, ’Yandoto da Kankara, ai da can ’Yandoto a karkashin Katsina take ita kuma Kankara tana karkashin Zamfara. Lokacin Sarki Dikko aka yi wannan musayar. Su ma sai a ce kowa ya kama gabansa.

“Idan kuma muka koma can Kudancin Katsinar, ita kanta Funtuwar yaya aka same ta? Garin Sabuwa wa ya samar da shi? Sannan mu dawo shiyyar Daura, sai a ce, a mayar da sarautar a garin Zango tunda can ne tushe kuma daga can ake nado sarki,” in ji Alhaji Usman.

Ana zargin gwamnati

Shi kuma wani da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “gaskiya ina zargin akwai wata balulluba daga wasu mukarraban gwamnati ko ita kanta gwamnatin.

“Dalili, wannan batun bai fito ba sai bayan da shugaban kasa ya zo kuma aka samu akasin da aka samu na zuwan sarkin wajen daurin auren ’yar gwamna.

“Kowa ya ga yadda wani ya rubuta takarda yana neman a hukunta sarki saboda karya kofa da dogarawansa suka yi don ya shiga masallacin da ake taron bayan da jami’an tsaron shugaban kasa suka yi yunkurin hana sarki shiga bisa hujjar shugaban kasa ya riga ya shigo masallacin an rufe kofa.

“Sannan akwai batun karin hakimai da gwamnatin jihar za ta yi a masarautun biyu na Katsina da Daura, amma a masarautar ta Katsina suka fi yawa.

“Wadannan duk wasu alamu ne da nake ganin cewa, gwamnati na da sha’awar ganin an farfasa masarautar.

“Wata hujja da muka gani ta cewar, wai sarki tun bayan hawansa bai yi rangadin da sarakunan baya suka rika yi ba, sai ya manta kullum cigaba ake samu.

“Kuma ana sara ana duban bakin gatari. Sarkin nan mutun ne mai tausayin talakawa baya son aza masu wani nauyi.

“Amma duk inda aka yi wani abu muddin aka gaya masa, yana zuwa shi da kansako ya tura wakili.”

Muna bincike kan takardar —Majalisa

Duk da cewa gwamnatin jihar ba ta ce koomai game da wannan batu ba, amma dangane da batun miƙa wannan takadar majalisar dokokin jahar wadda a aka ga tambarinta a kai, mai magana yawun Kakakin majalisar dokokin jihar ta Katsina, Honarabil Nasiru, Aminu Magaji, ya ce, har zuwa lokacin da wakilinmu ya tuntube shi, babu wata takarda mai kama da irin wannan, ba ma ita ba da aka kawo majalisar.

Ya bayyana cewa, majalisar ta kaddamar da binciken yadda aka buga wa takardar da ke yawo a gari tambari da sunanta.

“Yanzu in aka tuna, ana satar sanya hannun mutun a takarda, yin amfani da tambarin karya da sauran irinnsu.

“Sannan a wannan takarda, babu sunan wanda ko wadanda suka rubuta, ta balle sunaye da sa hannu.

“Yadda ka gan ta a soshiyal midiya haka mu ma muka gani,” in ji Aminu Magaji, mai magana da yawon kakakin majalisar dokokin jihar Katsina.

Duk wani kokari na ji daga Masarautar Katsina ya ci tura, kuma har zuwa lokacni da muka kamamla hada wannan labari babu wani abu da ya fito daga gareta a hukumance.

Sai dai wasu na kusa da ita sun ce babu mamakin ji ko ganin irin wannan batu musamman ga masarauta.

“Idan har za a dubi tarihi da kuma yanayi, ai an san Masarautar Katsina haka ya kamace ta ta tsaya. Duk wuraren da ake magana wa ya haifar ko ya raya su?

“Kada mu ɗauka da nisa, abin da Marigayi Sarki Muhammadu Dikko ya yi a wannan masarauta duk arewa babu sarkin da ya yi. Mu kawai dai muna kallon wadanda suke neman kawo wannan matsalar walau sun yi don neman suna ko wani abu can na biyan bukata, musamman a siyasance”, inji wani da ya nemi a sakaya sunansa a yayin da wakilinmu ya tuntube shi a wayar salula

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Masarautar Katsina sarki mai daraja ta ɗaya raba Masarautar Katsina daraja ta biyu masu daraja ta wakilinmu ya wa takardar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Akwai wasu tsaffin ‘yan siyasa daga yankin Arewacin Najeriya,wadanda ke ci da gumin ‘yan Arewa. Wadannan tsaffin ‘yan siyasa, yanzu alkadarinsu ya riga ya karye, ba su da wani abu da ya rage illa su rungumi siyasar kabilanci da bangaranci.

Ba tsaffin ‘yan siyasa kawai ba ne. Gungu-gungu ne. Wasun su, tsaffin ‘yan boko ne. Wasu ‘yan Kasuwa. Wasu ma ba wata sana’a ko wani aiki da suka taba yi a rayuwarsu da ya wuce ci da gumin Arewa . Wani abu da ya hade su shi ne, mafi yawansu sun samu damar da za su taimaki Arewa ko mutanen Arewa, amma suka ki. Misali, a cikin irin wadannan mutane, babu maras sa kunya,irin wadanda suka rike mukamai a gwamnatin marigayi Shugaba Buhari. Ire-iren wadannan mutanen har suna da bakin magana? Yanzu har wani wanda ya taba rike mukamin minista a gwamnatin Buhari na da bakin magana cewa an ki kammala hanyar Abuja zuwa Kano? Me yana su gama ta lokacin da sunan mulki? Me ya hana su gama aikin hanyar Kano zuwa Katsina ko Kano zuwa Kongolam? Me ya hana su gama hanyoyi da yawa a Arewa?

Abin takaici shugabannin wadannan kungiyoyi na dattawan Arewa, babu damar da ba su samu ba. Amma Fisabilillahi in da sun yi amfani da damar da suka samu, da yanzu za ai magana akwai marabarata a Arewa ko matasa masu bangar siyasa? Wasu gwamnoni cikin su. Yanzu misali, in banda me tsohon gwamnan Kano Ibrahim Shekaru zai yi a kungiya? Wanda yai gwamna shekara 8, yai minista, yai sanata, kuma maida kan shi baya ya dawo kungiya? Kuma kungiya ba irin ta su tsohon shugaban kasar Amurka Jimmy Carter ba. Ai a duniya, wadanda suka taba rike mukaman siyasa na kafa gidauniya amma ba kungiyar siyasa ba. Ba kungiyar neman abinci ba da tattaunawa kan mukaman siyasa. Gidauniya aka sani mai yaki da cututuuka,ko mai bunkasa ilmin mata da yara da sauran matsaloli ba kungiyar assasa kabilanci ba da siyasar ci da ceto

Wadannan mutanen ta kare masu ne kawai. Ba su da abin fada shi ne suka dawo suka dauki kahon tsana suka kafa ma gwamnatin Shugaba Tinubu. Babu wani kishin Arewa a tare da su.

 

Wadanne Ayyuka Tinubu Ya Gudanar A Arewa?

Tunda aka kirkiri Nijeriya,ba ai shugaban da ya dauko hanyar ‘yantar da Arewacin Nijeriya ba, kamar shugaba Tinubu. Misali, su wa za su fi cin gajiyar hukumar kiwo? Arewa an santa da noma da kiwo. Tinubu ya kirkiri hukumar kiwo ya dauko minista daga Arewa Mukhtar Idi Maiha ya damka amanar wurin. Ya dauko mutane masu daraja kamar Farfesa Attahiru Jega ya sanya a wurin domin a zamanantar da kiwo, a kawo karshen fadace fadace tsakanin manoma da makiyaya, sannan Nijeriya ta samu karuwar kudaden kasashen waje. A gabanka, lokacin babbar Sallah, shugaban mulkin sojar janhoriyar Nijar ya hana a shigo da dabbobi a Nijeriya. Wannan babban sako ne cewa mu tashi mu farka. Kuma Arewacin Nijeriya za mu dogaro da kanmu harma mu ciyar da Nijeriya da nama da madara idan muka ci gaba da ba gwamnatin Tinubu goyan baya.

Shugaba Tinubu ya bude iyakokin da Buhari ya kulle, abinci ya karu a kasa. Shugaba Tinubu ya ba da ayyukan hanyoyin da gwamnatin Buhari ta watsar kamar layin dogo daga Kano zuwa Maradi, hanyar Sokoto zuwa Badagary, Akwanga zuwa Gombe, Kafur Marabar Kankara zuwa Gidan Mutum Daya, Kano zuwa Kongolom da sauran su. Ana ci gaba da aikin bututun iskar gas daga Ajakuta zuwa Kano, ana ci gaba da aikin hako mai a Kolmani. Shugaba Tinubu ya ba Arewa mukaman da sune gwamnati. Ministan tsaro guda biyu duk Arewa ne. Mai ba shugaban kasa akan tsaro dan Arewa ne. Kuma ba wanda aka hana yai aikin shi. Misali, ko Hasidin Iza Hassada ba zai ce kashe ‘yan ta’adda dubu goma sha uku ba komi bane. Ko ‘yanto mutanen da akai garkuwa da su sama dubu sha daya ba daidai ba ne.

An ba mu mukamin ministan kiwon lafiya da walwala, Muhammad Ali Pante da duniya ke alfahari da shi saboda an tabbatar da kwarewarsa. Misali, cikin shekaru 2 kawai, an gyara kananan asibitocin guda 500 a jihohin Arewa. An sakar fannin kiwon lafiya matakin farko kudi Naira Biliyan 20 a Arewa domin rage mutuwar mata masu haihuwa da yara kanana. An yi ma mata dubu 4 fidar haihuwa (CS) kyauta. An yi miliyoyin yara allurar rigafin kyanda,zazzabin cizon sauro da farar masassara. Mutane miliyan daya da dubu dari tara masu dauke da kwayar cuta mai karya garkuwar jiki na ci gaba da samun magani duk da datse tallafi da gwamnatin Amurka ta yi. da sauran su.

Tinubu ya ba mu karamar ministan Ilmi, Suwaiba. A shekarar 2024, gwamnatin shugaba Tinubu ta ba kowace jihar Naira Miliyan 598 ta horas da malamai, ta gina makarantu na zamanin na firamare 37 da sauran su. Hukumar TETFUND baki daya hannun ‘yan Arewa take. Babban Sakataren hukumar Sonny Echono da shugaban Board din Aminu Bello Masari duk ‘yan Arewa ne,kuma dubi irin aikin da ake a wurin?

Batun ba dalibai lamani,abi ne mai kyau da zai amfani ‘ya’yan talakawa su sami ilmi mai inganci domin fita daga kangin talauci. Tsaffin Arewa masu ci da gumin Arewa ba su damu da ilmin ‘yan uwansu ba. Sun fi kyautata ma kawalai, karuwai da ‘yan bangar siyasa.

Idan ka koma bangaren aikon gona, Abubakar Kyari da ayyukan da ake. Takin kawai a shekarar 2024 karkashin tsarin AgriPocket sun ba manoma miliyan 2 a kan rangwamen farashin kashi hamsin. Babban Bankin Nijeriya, ya rama manoma da ba na boge ba buhun taki miliyan biyu da dubu dari biyu.

Saboda haka farfaganda ce ta siyasa masu fadar ba a yi da Arewa. Kamata yai su fito fili su ce ba a yi da su kawai.

 

Kiranka ga al’ummar Arewa?

To ni kirana ga matasan Arewa, shi ne, kada su bari masu ci da ceto su maida su makaman siyasa. Tinubu ya ce kowa zai iya zama mai ilmi. Ko farfesa kake so, ga kofa an bude. Saboda zabi ya gare ka ka bi hanyoyin da aka tanada domin amfana da tsare-tsaren gwamnati, kamar NELFUND da sauran su.

Mutanen Arewa mu sani zaman lafiya da hadin kan Nijeriya ya fi burin wani dan siyasa. Maganar kabilanci da bangaranci mu barta, saboda kasashe da yawa sun tarwatse,an yi yake yake a kasashen Afirika da dama saboda wasu ‘yan siyasa sun fito da batun kabilanci.

Rwanda, Saliyo, Liberia, Ibory Coast da sauran su duk sun danin sakamakon siyasar banza ta kabilanci. Mulki zai dawo a 2031 ba 2027 ba, kuma shugaba Tinubu ne yakamata a sake zabe saboda shi ya gano matsalar Najeriya,kuma ya dauki hanyar magance ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara