Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@18:01:45 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Published: 18th, May 2025 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Shugaban Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya karɓi tawagar jami’an Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) tare da kamfanin Max Air domin duba kayayyakin aikin hukumar.

 

A jawabinsa, mataimakin mai kula da ofishin hukumar da ke Kano, Mista Barnabas Anderson, ya ce manufar wannan ziyarar ita ce don yin binciken gaggawa da tabbatar da ingancin kayan aikin hukumar kula da alhazai ta jihar.

 

Ya ƙara da cewa, tawagar ta tantance kayan aiki, shirin jigilar maniyyata na jihar, takardun tafiya, fasfo da kuma kayan aikin sansanin Alhazai.

 

Ya bayyana cewa, za a yi jigilar rukuni na farko na maniyyata 550 daga jihar Jigawa zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayun 2025, yayin da rukuni na biyu za su tashi ranar 21 ga watan Mayun.

Mista Anderson ya nuna gamsuwarsa da yadda hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da aikin hajjin bana.

 

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Janar na Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya jaddada cewa an samu nasarori da dama a shirye-shiryen aikin hajjin 2025 a jihar.

Ya sake jaddada kudirin gwamnatin jihar wajen tabbatar da jin daɗin maniyyata daga Jigawa, a gida Najeriya da kuma ƙasar Saudiyya.

 

Labbo ya yaba wa NAHCON bisa goyon baya da haɗin kai da take bai wa hukumar domin nasarar aikin hajjin bana.

 

Tawagar ta ziyarci sansanin horaswar matasa masu yi wa kasa hidima NYSC na Yakubu Gowon da ke Fanisau, inda nan ne sansanin Alhazai na wucin gadi da kuma Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa Muhammadu Sunusi.

 

Radio Nigeria ya ruwaito cewa, Daraktan Janar din ya kuma kaddamar da tawagar ‘yan jarida na aikin hajjin 2025 a ofishinsa.

 

Ya yi kira ga ‘yan jaridar da aka zaɓa da su tabbatar da kiyaye dokoki da ka’idojin aikin jarida yayin da suke a Ƙasa Mai Tsarki.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa wannan titin ba na yankin Arewa kadai ba ne, ya bayyana shi a matsayin jijiyar ƙasa da ƙasa ne wadda ke haɗa yankuna daban-daban tare da ƙarfafa haɗin kai da bunƙasar tattalin arziki.

 

Ya kara da cewa titin Abuja- Kaduna da Kano na ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ƙarƙashin Manufar Sabon Fata na (Renewed Hope Agenda), wadda ke nufin sabunta manyan gine-ginen ƙasa da inganta tattalin arziki.

 

Yace “Wannan titi ba hanya ce kawai ba inda yace wata hanya ce ta tattalin arziki wadda ke haɗa mutane, kasuwanni, da dama a fadin Arewacin Nijeriya da ma bayan haka,”

 

A nasa jawabin, Sanata Umahi ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake kaiwa da komowa domin kare muradun al’ummar Kaduna, tare da tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar kammala aikin cikin lokaci. Ya bayyana cewa an umarci kamfanonin da ke aikin da su rika aiki sau biyu a rana domin hanzarta cigaba ba tare da rage inganci ba.

 

Ministan ya kara da cewa amfani da fasahar siminti mai ɗorewa wanda zai tabbatar da cewa titin zai dawwama tare da rage kudin gyara nan gaba.

 

Kamfanonin da ke aikin sun yi alkawarin ƙara gaggautawa musamman a yankin Jere dake jihar Kaduna, inda ake sa ido sosai kan ci gaban aiki. Gwamnatin Jihar Kaduna ta kuma tabbatar da ci gaba da haɗin kai da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya domin magance ƙalubalen da ke iya janyo tsaiko.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari October 11, 2025 Manyan Labarai Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP October 11, 2025 Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano