Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-03@07:35:07 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Published: 18th, May 2025 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Shugaban Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya karɓi tawagar jami’an Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) tare da kamfanin Max Air domin duba kayayyakin aikin hukumar.

 

A jawabinsa, mataimakin mai kula da ofishin hukumar da ke Kano, Mista Barnabas Anderson, ya ce manufar wannan ziyarar ita ce don yin binciken gaggawa da tabbatar da ingancin kayan aikin hukumar kula da alhazai ta jihar.

 

Ya ƙara da cewa, tawagar ta tantance kayan aiki, shirin jigilar maniyyata na jihar, takardun tafiya, fasfo da kuma kayan aikin sansanin Alhazai.

 

Ya bayyana cewa, za a yi jigilar rukuni na farko na maniyyata 550 daga jihar Jigawa zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayun 2025, yayin da rukuni na biyu za su tashi ranar 21 ga watan Mayun.

Mista Anderson ya nuna gamsuwarsa da yadda hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da aikin hajjin bana.

 

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Janar na Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya jaddada cewa an samu nasarori da dama a shirye-shiryen aikin hajjin 2025 a jihar.

Ya sake jaddada kudirin gwamnatin jihar wajen tabbatar da jin daɗin maniyyata daga Jigawa, a gida Najeriya da kuma ƙasar Saudiyya.

 

Labbo ya yaba wa NAHCON bisa goyon baya da haɗin kai da take bai wa hukumar domin nasarar aikin hajjin bana.

 

Tawagar ta ziyarci sansanin horaswar matasa masu yi wa kasa hidima NYSC na Yakubu Gowon da ke Fanisau, inda nan ne sansanin Alhazai na wucin gadi da kuma Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa Muhammadu Sunusi.

 

Radio Nigeria ya ruwaito cewa, Daraktan Janar din ya kuma kaddamar da tawagar ‘yan jarida na aikin hajjin 2025 a ofishinsa.

 

Ya yi kira ga ‘yan jaridar da aka zaɓa da su tabbatar da kiyaye dokoki da ka’idojin aikin jarida yayin da suke a Ƙasa Mai Tsarki.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Ta ce, yayin ziyarar, firaministan kasar Sin Li Qiang, zai zurfafa musayar ra’ayoyi tare da jagororin kasar Masar, game da ciyar da alakar sassan biyu gaba, da zurfafa hadin gwiwa mai samar da gajiya, da batutuwan dake jan hankulan sassan biyu.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwalejin Koyar Da Aikin Jinya Ta Jigawa Za Ta Fara Bada Shaidar Babbar Difiloma
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
  • Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata