Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-18@01:56:17 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Published: 18th, May 2025 GMT

Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa

Shugaban Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya karɓi tawagar jami’an Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) tare da kamfanin Max Air domin duba kayayyakin aikin hukumar.

 

A jawabinsa, mataimakin mai kula da ofishin hukumar da ke Kano, Mista Barnabas Anderson, ya ce manufar wannan ziyarar ita ce don yin binciken gaggawa da tabbatar da ingancin kayan aikin hukumar kula da alhazai ta jihar.

 

Ya ƙara da cewa, tawagar ta tantance kayan aiki, shirin jigilar maniyyata na jihar, takardun tafiya, fasfo da kuma kayan aikin sansanin Alhazai.

 

Ya bayyana cewa, za a yi jigilar rukuni na farko na maniyyata 550 daga jihar Jigawa zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayun 2025, yayin da rukuni na biyu za su tashi ranar 21 ga watan Mayun.

Mista Anderson ya nuna gamsuwarsa da yadda hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da aikin hajjin bana.

 

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Janar na Hukumar Kula da Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya jaddada cewa an samu nasarori da dama a shirye-shiryen aikin hajjin 2025 a jihar.

Ya sake jaddada kudirin gwamnatin jihar wajen tabbatar da jin daɗin maniyyata daga Jigawa, a gida Najeriya da kuma ƙasar Saudiyya.

 

Labbo ya yaba wa NAHCON bisa goyon baya da haɗin kai da take bai wa hukumar domin nasarar aikin hajjin bana.

 

Tawagar ta ziyarci sansanin horaswar matasa masu yi wa kasa hidima NYSC na Yakubu Gowon da ke Fanisau, inda nan ne sansanin Alhazai na wucin gadi da kuma Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa Muhammadu Sunusi.

 

Radio Nigeria ya ruwaito cewa, Daraktan Janar din ya kuma kaddamar da tawagar ‘yan jarida na aikin hajjin 2025 a ofishinsa.

 

Ya yi kira ga ‘yan jaridar da aka zaɓa da su tabbatar da kiyaye dokoki da ka’idojin aikin jarida yayin da suke a Ƙasa Mai Tsarki.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya

Kashi na biyu na maniyyata 415 daga jihar Kwara sun tashi zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

 

Da yake jawabi ga maniyyatan jihar kafin tafiyarsu, Amirul-Hajj na Jiha, Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahaya- Alebiosu ya shawarce su da su kasance jakadu nagari na jihar yayin da suke kasar Saudiyya.

 

Oba Yahaya- Alebiosu ya ce gwamnatin jihar ta samar da matakai daban-daban don tabbatar da annashuwa da kare lafiyar alhazai a tafiyar da suke yi a kasa mai tsarki.

 

Mai baiwa gwamnan jihar Kwara shawara ta musamman kan harkokin addini, Alhaji Ibrahim Dan-Maigoro ya jagoranci tawagar maniyyata guda 415 zuwa kasar Saudiyya.

 

An dauke Mahajjatan ne a jirgin Max Airline daga filin jirgin sama na Babatunde Idi-Agbon dake Ilorin.

 

Ya zuwa yanzu dai an jigilar alhazai 975 daga jihar Kwara zuwa kasar Saudiyya.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa
  • Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa
  • Kashi Na Biyu Na Maniyyata 415 Daga Jihar Kwara Sun Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko
  • Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kudirin Dokar Hukumar Kula Da Manyan Makarantun Sakandire