Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
Published: 17th, May 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Katsina ta sanar cewa, za a fara jigilar maniyyatan jihar a ranar Lahadi 18 ga wannan wata na Mayu, 2025, zuwa Ƙasa Mai Tsarki.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Badaru Bello Karofi, ya shaida wa wakilinmu, cewa maniyyatan da suka fito daga Malunfashi da Bakori, Ƙanƙara, Dandume, Ƙafur da Ɗanja sune rukunin farko da ake sa ran za su tashi daga filin sauka da tashin jiragen sama na Umaru Musa da ke cikin babban birnin jihar.
Tun farko sai da jagoran mahajjatan jahar, wanda kuma shi ne mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Joɓe ya bayyana cewar, gwamnatin jihar ta ɗauki duk wasu matakan da suka wajaba tun daga gida har zuwa Ƙasa Mai Tsarki domin ganin cewa mahajjatan jihar sun samu duk wata kulawa a hukumance don gudanar da aikin ibadar cikin jin daɗi da walwala.
Sai dai Amirul Hajjin ya ja hankalin maniyatan da su kiyaye duk wata doka, tun daga nan gida har a can Saudiyya inda suke ɗaukar hukunci mai tsanani ga wanda ya saɓa, musamman shiga da duk wani nau’in abin da zai sa maye da sauransu.
Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Bornoউৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙasa Mai Tsarki maniyyata Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin shahidai a yakin Gaza ya kai 53,119 tun daga Oktoba 2023
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda suka yi shahada a yakin da Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza ya kai 53,119 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Adadin ya karu ne sakamakon wasu hare-haren Isra’ila na baya baya nan wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 93 wayewar safiyar Juma’a.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ma’aikatar ta ce an kuma mika wasu mutane fiye da 200 da suka jikkata zuwa asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya a zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da sojojin Isra’ila suka kai a yankuna da dama.
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an sami rahoton mutuwar mutane 109 da jikkata 216, a cewar hukumomin lafiya.
Tun bayan da Isra’ila ta sake koma kai hare-haren a ranar 18 ga Maris, adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa shahidai 2,985 da kuma jikkata 8,137.
A dunkule, tun fara harin Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023, adadin wadanda suka mutu a yanzu ya kai 53,119 da 120,214 da suka jikkata.
Kafofin yada labaran Falasdinu sun rawaito cewa sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa sama da 250 a fadin zirin Gaza musamman a yankin Beit Lahia da ke arewacin zirin Gaza cikin sa’o’i 36 kacal.