Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya
Published: 17th, May 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Katsina ta sanar cewa, za a fara jigilar maniyyatan jihar a ranar Lahadi 18 ga wannan wata na Mayu, 2025, zuwa Ƙasa Mai Tsarki.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Alhaji Badaru Bello Karofi, ya shaida wa wakilinmu, cewa maniyyatan da suka fito daga Malunfashi da Bakori, Ƙanƙara, Dandume, Ƙafur da Ɗanja sune rukunin farko da ake sa ran za su tashi daga filin sauka da tashin jiragen sama na Umaru Musa da ke cikin babban birnin jihar.
Tun farko sai da jagoran mahajjatan jahar, wanda kuma shi ne mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruk Joɓe ya bayyana cewar, gwamnatin jihar ta ɗauki duk wasu matakan da suka wajaba tun daga gida har zuwa Ƙasa Mai Tsarki domin ganin cewa mahajjatan jihar sun samu duk wata kulawa a hukumance don gudanar da aikin ibadar cikin jin daɗi da walwala.
Sai dai Amirul Hajjin ya ja hankalin maniyatan da su kiyaye duk wata doka, tun daga nan gida har a can Saudiyya inda suke ɗaukar hukunci mai tsanani ga wanda ya saɓa, musamman shiga da duk wani nau’in abin da zai sa maye da sauransu.
Gwamnatin Kano ta haramta ‘Ƙauyawa Day’ a lokacin bikin aure ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Bornoউৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙasa Mai Tsarki maniyyata Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Kasar Sin ta kawo karshen aikin bayar da agajin gaggawa mafi girma a gundumar Rongjiang da ke lardin Guizhou, a yankin kudu maso yammacin kasar da misalin karfe 10 na safiyar ranar Lahadi, yayin da aka kammala ruwan saman da aka tafka kamar da bakin kwarya kamar yadda mahukuntan yankin suka bayyana.
Lardin Guizhou da wasu larduna masu iyaka da shi da ke kudu maso yammacin kasar Sin sun fuskanci mamakon ruwan sama tun daga ranar 18 ga watan Yuni, lamarin da ya haifar da mummunar ambaliyar ruwa, inda lamarin ya fi muni a yankin Rongjiang.
Mahukuntan yankin sun raba yankin zuwa kashi bakwai a matsayin wadanda ambaliyar ta fi shafa tare da kwashe mazauna zuwa wasu manyan wurare masu tudu. An kwashe fiye da mutane 40,000 zuwa wurare masu aminci tun karfe 6 na yammacin ranar Asabar saboda rigakafin hadarin ambaliyar.
Kasar Sin ta ware karin kudi yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.96 daga cikin kasafin kudin gwamnatin tsakiya don tallafa wa ayyukan ba da agajin gaggawa da farfado da lardin Guizhou da ambaliyar ruwan ta shafa, inda hakan ya kara adadin kudin da aka ware zuwa yuan miliyan 200, kamar yadda hukumar raya kasa da gudanar da gyare-gyare ta kasar ta bayyana. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp