A taron kasashen larabawa karo na 34Th wanda ake gudanarwa a birnin Bagdaza na kasar Iraki, shuwagabannin kasashen larabawa sun bukaci tsagaita wuta a gaza sannan sun yi kira da aka kafa kasar Falasdinu mai zaman kanta.

Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa, shuwagabannin sun bukaci a magance matsalolin da suke faruwa a Siriya Lebanon da kuma sudan.

Ana taron shuwagabannin kasashen larabwa a Bagdaza ne a dai dai lokacinda gwamnatin HKI take kara fadada hare-hare a kan zirin Gaza da kuma kashe Falasdinawa maza da mata da yara mutkar abinda zata iya kashewa.

Majiyar kiwon lafiya ta Gaza ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu sojojin HKI sun kashe falasdinawa kimani 53,272 mafi yawansu mata da yara, sannan wasu 120,673 kuma sun ji rauni . Ma’aikatar ta kara da cewa tun watan Marisa bayan da HKI ta sake komawa yaki a gaza ta kashe Falasdinawa 3131 sannan wasu 8,632 suka ji rauni.

A cikin bakin da suka sami halattar taron shuwagabannin kasashen larabawa karo na 34Th akwai babban sakataren MDD Antonio Gotteress kan cewa ana bukatar tsagaita wuta a gaza da gaggawa.  Sai kuma Firai ministan kasar Espaniya Pedro Sanchez ya bukaci a takurawa HKI ta dakatar kisan kiyashi a gaza.

Shuwagabannin sun ki amincewa da duk wani shiri na fidda Falasdinawa a gaza ko kuma kasarsu, kamar yadda Trump ya fada a farkon wannan shekarar.

Har’ila yau firai ministan kasar Iraki Muhammad shi’a Assudani, ya ware dalar Amurka miliyon $20 don sake gina Gaza sannan wasu miliyon 20 don sake gina kasar Lebanon. Ministan harkokin wajen kasar Siriya ne ya wakilci kasar a taron na Bagdaza saboda matsin lambar da wasu yan siyasa a kasar Iraki suka yiwa firai ministan kasar kan kada ya bar Ahmes Sharaa ya taka kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza

Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Amurka tana da hannu dumu-dumu a muggan ayyukan da gwamnatin ‘yan shayoniyya suka aikata nakisan kare dangi a Gaza

Jakada kuma wakilin dindindin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya yi nuni da ire-iren laifuffukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya suke ci gaba da aikatawa kan al’ummar Falastinu, yana mai bayyana wadannan laifuka a matsayin wani misali karara na kisan kiyashi yana kuma daukar Amurka a matsayin babbar kawa a aikata wadannan muggan laifuka.

A yayin zama na musamman a Majalisar Dinkin Duniya a yammacin jiya Alhamis kan batun boren Falasdinawa “Ankaba” na musamman ya bayyana cewa: Gwamnatin yahudawan sahayoniyya tana so da cikakken goyon baya da taimakon Amurka ta hanyar kaddamar da harte-haren wuce gona da iri da gangan ta rusa asibitoci, makarantu, kashe mata da yara, kaiwatar da kisan gilla kan ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya da ‘yan jarida da sauransu, lamarin da a halin yanzu ya yi sanadin shahadar mutane kusan 60,000 da jikkata wasu da kuma bacewar wasu da dama.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Munanan laifukan da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta aikata, ba za a iya musantawa ba, kuma kungiyoyin duniya, kotun duniya da sauran hukumomin shari’a na da masaniya kan irin girman wadannan munanan ayyukan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa
  • Jagora: Jawaban Trump A Ziyar Da Ya Kai Wasu Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Abin Kunya Ne Gare Shi Ga Kuma Amurkawa
  • Hamas Ta Ce An Fara Tattaunawa Tare Da HKI Kan Tsakana Wuta A Doha A Yau Asabar
  • Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza
  • Qalibaf : Dole ne Iran da Aljeriya su hada kai don saukaka kai kayan agaji zuwa Gaza
  • Fiye Da Falasdinawa 80 Ne Su Ka Yi Shahada Daga Safiyar Yau Alhamis
  • Jagora: Yin Shirun da  Kasashen Duniya Sun Yi Kan ABinda Yake Faruwa A Gaza Abun Mamaki Ne