A taron kasashen larabawa karo na 34Th wanda ake gudanarwa a birnin Bagdaza na kasar Iraki, shuwagabannin kasashen larabawa sun bukaci tsagaita wuta a gaza sannan sun yi kira da aka kafa kasar Falasdinu mai zaman kanta.

Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa, shuwagabannin sun bukaci a magance matsalolin da suke faruwa a Siriya Lebanon da kuma sudan.

Ana taron shuwagabannin kasashen larabwa a Bagdaza ne a dai dai lokacinda gwamnatin HKI take kara fadada hare-hare a kan zirin Gaza da kuma kashe Falasdinawa maza da mata da yara mutkar abinda zata iya kashewa.

Majiyar kiwon lafiya ta Gaza ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu sojojin HKI sun kashe falasdinawa kimani 53,272 mafi yawansu mata da yara, sannan wasu 120,673 kuma sun ji rauni . Ma’aikatar ta kara da cewa tun watan Marisa bayan da HKI ta sake komawa yaki a gaza ta kashe Falasdinawa 3131 sannan wasu 8,632 suka ji rauni.

A cikin bakin da suka sami halattar taron shuwagabannin kasashen larabawa karo na 34Th akwai babban sakataren MDD Antonio Gotteress kan cewa ana bukatar tsagaita wuta a gaza da gaggawa.  Sai kuma Firai ministan kasar Espaniya Pedro Sanchez ya bukaci a takurawa HKI ta dakatar kisan kiyashi a gaza.

Shuwagabannin sun ki amincewa da duk wani shiri na fidda Falasdinawa a gaza ko kuma kasarsu, kamar yadda Trump ya fada a farkon wannan shekarar.

Har’ila yau firai ministan kasar Iraki Muhammad shi’a Assudani, ya ware dalar Amurka miliyon $20 don sake gina Gaza sannan wasu miliyon 20 don sake gina kasar Lebanon. Ministan harkokin wajen kasar Siriya ne ya wakilci kasar a taron na Bagdaza saboda matsin lambar da wasu yan siyasa a kasar Iraki suka yiwa firai ministan kasar kan kada ya bar Ahmes Sharaa ya taka kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas aragchi da tokwransa na kasar Masar Badr Abdullati da kuma tokwaransu na kasar Omman Badr ben Hamad Al-Busaidi sun tattauna a tsakaninsu a birnin Oslo inda suka halattar taron tattaunawa ta 22th da ake gudanarwa a birnin na Oslo babban birnin kasar Norway.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa bangarorin biyu sun yi maganar rikice-rikicen da ke faruwa a yankin da kuma hanyar warwaresu.

Taron oslo na shekara shekara dai a wannan karon ya maida hankali ne kan abubuwan da suke faruwa a yankin Asiya da kuma hanyoyin da yakamata abi don rage halin da ake ciki a yankin. Musamman matsalar yaki da kima kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza da kuma yadda HKI ta sabawa dukkan dokokin kasa da kasa a yakin.

Jaridar The National ta kasar Amurka ta bada labarin cewa kasashen Iran da masar wadanda basa da dangantakar Diblomasiyya na kimani shekar 40 sun tattauna batun maida huldar jakadanci a tsakaninsu, inda daga cikin ministan harkokin wajen Masar ya bukaci a shafin hoton Khalid Islam buli wanda ya kashe tsohon shugabann kasar Masar a shekara 1980 wanda aka sanya a kan wani babban titi a birnin Tehran. Har yanzun dai ba’aji ta bakin gwamnatinn kasar Iran kan hakan ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Shugabannin Sin Da Kongo (Brazaville) Sun Aike Da Wasikun Taya Murna Ga Taron Ministocin Kula Da Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC
  • Falasdinawa Masu Yawa Sun Yi Shahada A Cibiyoyin Raba Kayan Agaji
  • Tawagar Fursininin Yaki Na Rasha Sunn Koma Gida Daga Kieve