Aminiya:
2025-07-03@09:20:34 GMT

Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso 

Published: 17th, May 2025 GMT

Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ƙaryata wani rahoto da ke yawo cewa yana shirin shiga sabuwar haɗakar siyasa.

A wani gajeren saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar, Kwankwaso ya bayyana rahoton a matsayin “karya, ba shi da tushe kuma makircin wasu ‘yan siyasa ne.”

Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani

Ya gargaɗi jama’a da ka da su yarda da irin waɗannan labarai marasa tushe.

“An jawo hankalina kan wani rahoto wanda ke bayyana matsayina a haɗin gwiwar siyasa a Najeriya.

“Ina so na fayyace cewa irin waɗannan rahotannin ƙarya ne, ba su da tushe kuma makircin siyasa ne kawai,” in ji Kwankwaso.

Tsohon ministan tsaron, ya bayyana cewa ya zaɓi ka da ya riƙa yin magana a fili kan wasu abubuwan da ke faruwa a siyasar ƙasar nan, amma zai yi magana a lokacin da ya dace.

“Na daɗe da daina yin sharhi kan abubuwan da ke faruwa a siyasa, kuma zan ci gaba da kaucewa yin haka a halin yanzu,” ya ƙara da cewa.

Kwankwaso ya buƙaci ’yan Najeriya da su dinga dogaro da hanyoyin sadarwarsa a hukumance idan suna son sanin matsayinsa ko ra’ayinsa game da wani abu.

“Dangane da hakan, ina roƙon jama’a da su riƙa duba ko sauraron saƙonni da ke fitowa daga shafukana da sauran hanyoyin sadarwarta kawai,” in ji shi.

Aminiya ta ruwaito cewa Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, har yanzu yana ɗaya daga cikin manyan ’yan siyasar da ake sa ido a kansu kan yiwuwar yin haɗaka da wata tafiya ta siyasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwaso Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran

Hukumomin Iran sun bayyana cewa aƙalla mutum 935 ne suka rasa rayukansu a hare-haren Isra’ila yayin yaƙin kwanaki 12 da ya gudana tsakaninsu da ƙasar.

Cikin waɗanda suka mutu sun haɗa har da mata 132 da yara 38, kamar yadda mai magana da yawun Hukumar Shari’a, Asghar Jahangir, ya bayyana a wata sanarwa a ranar Litinin, wacce kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito.

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe HOTUNA: Sabon shugaban rikon APC APC ya jagoranci taron Majalisar Gudanarwa

A baya, Ma’aikatar Lafiya ta ce adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila ya kai 606, sannan mutane 5,332 da suka jikkata.

Jahangir ya ce hare-haren Isra’ila kan gidan yari na Evin da ke Arewa maso Yammacin Tehran sun yi sanadin mutuwar mutum 79, ciki har da fursunoni da ma’aikatan gidan yari, da mazauna yankin.

Ya kara da cewa gidan yarin Evin ya zama ba zai iya aiki ba, kuma an kwashe fursunonin, yana mai kiran harin a matsayin “tauye hakkin ɗan’adam da kuma karya dokokin kasa da kasa.”

A ranar 13 ga watan Yunin nan ne yaƙi ya tsakanin Isra’ila da Iran ya barke, lokacin da Tel Aviv ta ƙaddamar da hare-haren sama kan sansanonin soja, nukiliya, da fararen hula na Iran.

Amurka ma ta kai hari kan cibiyoyin nukiliya na Fordow, Natanz, da Isfahan na Iran, wanda ya ƙara tsananta rikicin.

Tehran ta mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa kan Isra’ila, inda suka kashe aƙalla mutane 29 tare da jikkata fiye da 3,400, kamar yadda Jami’ar Hebrew ta Jerusalem ta bayyana.

Kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa yaƙin ya tsaya sakamakon wata yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta dauki nauyi, wacce ta fara aiki a ranar 24 ga Yuni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
  • Malaman Sunna A Kasar Iran Sun Bayyana Gwagwarmaya Da HKI Wajibi Ne A Sharia
  • Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI
  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki