Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso
Published: 17th, May 2025 GMT
Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ƙaryata wani rahoto da ke yawo cewa yana shirin shiga sabuwar haɗakar siyasa.
A wani gajeren saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar, Kwankwaso ya bayyana rahoton a matsayin “karya, ba shi da tushe kuma makircin wasu ‘yan siyasa ne.”
Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta saniYa gargaɗi jama’a da ka da su yarda da irin waɗannan labarai marasa tushe.
“An jawo hankalina kan wani rahoto wanda ke bayyana matsayina a haɗin gwiwar siyasa a Najeriya.
“Ina so na fayyace cewa irin waɗannan rahotannin ƙarya ne, ba su da tushe kuma makircin siyasa ne kawai,” in ji Kwankwaso.
Tsohon ministan tsaron, ya bayyana cewa ya zaɓi ka da ya riƙa yin magana a fili kan wasu abubuwan da ke faruwa a siyasar ƙasar nan, amma zai yi magana a lokacin da ya dace.
“Na daɗe da daina yin sharhi kan abubuwan da ke faruwa a siyasa, kuma zan ci gaba da kaucewa yin haka a halin yanzu,” ya ƙara da cewa.
Kwankwaso ya buƙaci ’yan Najeriya da su dinga dogaro da hanyoyin sadarwarsa a hukumance idan suna son sanin matsayinsa ko ra’ayinsa game da wani abu.
“Dangane da hakan, ina roƙon jama’a da su riƙa duba ko sauraron saƙonni da ke fitowa daga shafukana da sauran hanyoyin sadarwarta kawai,” in ji shi.
Aminiya ta ruwaito cewa Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, har yanzu yana ɗaya daga cikin manyan ’yan siyasar da ake sa ido a kansu kan yiwuwar yin haɗaka da wata tafiya ta siyasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta bayyana cewa babu wata rubutaciyar shawara data samu daga Amurka.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya musanta ikirarin samun rubutaccen sako daga Amurka kan yarjejeniyar nukiliya.
“Iran ba ta sami wata rubutacciyar shawara daga Amurka ba, kai tsaye ko a kaikaice,” in ji Araghchi a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a.
Wannan matsayi na zuwa ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa Iran ta samu wata shawara daga kasarsa.
Ya kara da cewa sakonnin da muke samu, kamar wanda duniya ke samu, suna cike da rudadi da kace-nace.
Amma matsayin Iran, na daram kuma babu ja da baya, ‘’ ku amince da hakkinmu ku kum akawo karshen takunkumai, idan hakan ya samu to za’a iya cimma matsaya.
Ministan hakokin wajen kasar ta Iran, ya kuma kara da cewa babu wani abu da zai sa Iran ta dakatar da hakkinta na inganta sanadarin uranium na zaman lafiya ba wanda yake kunshe a cikin ‘yancin da aka baiwa dukkan kasashen da suka sanya hannun kan yarjejeniyar hana yaduwar makamman nukiliya.
A koyaushe muna maraba da tattaunawa bisa mutunta juna, sannan muna watsi da duk wani yunkuri na tilastawa ko matsin lamba. »