Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso
Published: 17th, May 2025 GMT
Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ƙaryata wani rahoto da ke yawo cewa yana shirin shiga sabuwar haɗakar siyasa.
A wani gajeren saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar, Kwankwaso ya bayyana rahoton a matsayin “karya, ba shi da tushe kuma makircin wasu ‘yan siyasa ne.”
Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta saniYa gargaɗi jama’a da ka da su yarda da irin waɗannan labarai marasa tushe.
“An jawo hankalina kan wani rahoto wanda ke bayyana matsayina a haɗin gwiwar siyasa a Najeriya.
“Ina so na fayyace cewa irin waɗannan rahotannin ƙarya ne, ba su da tushe kuma makircin siyasa ne kawai,” in ji Kwankwaso.
Tsohon ministan tsaron, ya bayyana cewa ya zaɓi ka da ya riƙa yin magana a fili kan wasu abubuwan da ke faruwa a siyasar ƙasar nan, amma zai yi magana a lokacin da ya dace.
“Na daɗe da daina yin sharhi kan abubuwan da ke faruwa a siyasa, kuma zan ci gaba da kaucewa yin haka a halin yanzu,” ya ƙara da cewa.
Kwankwaso ya buƙaci ’yan Najeriya da su dinga dogaro da hanyoyin sadarwarsa a hukumance idan suna son sanin matsayinsa ko ra’ayinsa game da wani abu.
“Dangane da hakan, ina roƙon jama’a da su riƙa duba ko sauraron saƙonni da ke fitowa daga shafukana da sauran hanyoyin sadarwarta kawai,” in ji shi.
Aminiya ta ruwaito cewa Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, har yanzu yana ɗaya daga cikin manyan ’yan siyasar da ake sa ido a kansu kan yiwuwar yin haɗaka da wata tafiya ta siyasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Haka zalika, sun ki bayyana takamaiman wajen da za a daura auren, har sai bayan an kammala, inda suka bayyana yin hakan a matsayin wata hanya ta kawar da cece-kuce daga al’umma.
Kazalika a ‘yan watannin da suka gabata kuma, an sake daura auren jaruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau tare da angonta Ibrahim Garba, a wani biki wanda za a iya kira da na sirri da aka gudanar a birnin Kaduna, daura auren shahararriyar jarumar Kannywood din, Rahma Sadau da mijinta Ibrahim Garba, wanda aka gudanar a ranar Asabar, ya yi matukar bai wa mutane mamaki, duba da cewa; kafin daurin auren babu wata alama ko sanarwa da aka fitar daga makusantan mijin ko matar.
An yi bikin da safe, a Masallacin Atiku Auwal da ke Unguwar Rimi, inda ‘yan’uwa da abokan arziki suka halarta, Rahma yayin da take magana da manema labarai ta bayyana cewa; ta zabi yin bikin cikin natsuwa ne, domin kauce wa hayaniya, bayan labarin ya bayyana a kafafen sada zumunta, ta tabbatar da daura auren nata.
Rahma ta shahara a fina-finan Kannywood da kuma wasu daga cikin fina-finan Nollywood, bayan da aka daura auren, masoyanta da abokan aikinta, suka tura mata sakwannin taya murna daga sassa daban-daban na Nijeriya, wannan aure ya zo ne watanni kadan bayan rasuwar mahaifinta, wanda ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.
Haka yasa ake saka alamar tambaya a kan jaruman masana’antar ta Kannywood, a kan cewa; me ya sa suke daura aurensu a sirrance? Yayin da wasu ke ganin yin hakan a matsayin wata hanya ce da jaruman ke bi wajen kauce wa bakin mutane, wasu kuma na ganin wannan a matsayin wata hanya ta nuna girman kai ko isa da jaruman ke bi, domin nuna wa duniya cewa; su ba kamar sauran al’umma ba ne.
Koma dai mene ne, akwai bukatar jaruman su tuna cewa; suna da dimbin mutane da ke kiran kansu a matsayin masoyan jaruman, wanda ko babu komai dai, bai dace a ce masoyinka ba shi da labarin wani abin alherin da ya same ka ba, musamman harka ta aure, wadda ka iya zama silar daina fitowa a fina-finai ga jarumai mata da mazajensu, ba su amince su ci gaba da harkar fim ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA