Aminiya:
2025-06-14@02:20:04 GMT

Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano

Published: 17th, May 2025 GMT

Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Tsaro da Gyaran Matasa, ya kama ’yan daba 31 a wani samame da ya gudana a unguwanni bakwai a jihar.

An kai samamen ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Mayu, 2025 ƙarƙashin jagorancin Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata.

Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno

Unguwannin da aka kai samamen sun haɗa da Ɗorayi, Ja’in, Sharada, Unguwar Dabai, Dukawa, Kabuga, Kofar Mata da sauransu, wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka.

Daga cikin waɗanda aka kama, mutum 25 ana zargin ’yan daba ne, yayin da shida ake zarginsu dallacin miyagun ƙwayoyi.

A cikin kayan da jami’an suka ƙwato akwai bindigogi na gargajiya guda huɗu, wuƙaƙe da adduna tara, sanduna uku, tabar wiwi da kuma ƙwayoyi irin su Exol guda 173 da wasu miyagun ƙwayoyi daban-daban.

Haka kuma, jami’an sun kama wasu riƙaƙƙun ’yan daba da suka daɗe suna addabar al’ummar Dorayi, ciki har da Dan Abba, Bola, Baka Kashi, Ramos, Abba Maciji da Abdul Baki.

“Dukkanin ’yan daban 25 da muka kama an gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 16 da ke kan titin Zungeru, kuma an tasa ƙeyarsu zuwa gidan gyaran hali.

“Sauran masu sayar da ƙwayoyi guda shida, ciki har da Rabi’u Hamza, an miƙa su ga hukumar NDLEA don ci gaba da bincike kafin a gurfanar da su a kotu,” in ji Dokta Kofar Mata.

Ya bayyana wannan samame a matsayin babban ci gaba wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya ce unguwanni kamar Dorayi sun sha fama da rikice-rikicen faɗan daba sama da shekaru 20.

Kama waɗannan ɓata-gari zai iya kawo ƙarshen wannan matsala.

Ya ƙara da cewa kwamitin ya ƙunshi jami’an tsaro da jami’an gwamnati domin haɗa kai wajen tsaftace birnin Kano da kuma taimaka wa matasan da suka ɓace su koma turbar gaskiya.

“Kwamitin Haɗin Gwiwa zai ci gaba da jajircewa domin ganin an samar da ingantaccen tsaro da kuma zaman lafiya ba tare da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ba a Kano,” in ji kwamitin.

Ga hotunan wasu daga cikin kayan da kwamitin ya ƙwato:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamiti kwayoyi Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia

Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.

Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Kamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.

A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”

An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.

Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”

Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.

Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya