Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano
Published: 17th, May 2025 GMT
Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Tsaro da Gyaran Matasa, ya kama ’yan daba 31 a wani samame da ya gudana a unguwanni bakwai a jihar.
An kai samamen ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Mayu, 2025 ƙarƙashin jagorancin Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata.
Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a BornoUnguwannin da aka kai samamen sun haɗa da Ɗorayi, Ja’in, Sharada, Unguwar Dabai, Dukawa, Kabuga, Kofar Mata da sauransu, wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka.
Daga cikin waɗanda aka kama, mutum 25 ana zargin ’yan daba ne, yayin da shida ake zarginsu dallacin miyagun ƙwayoyi.
A cikin kayan da jami’an suka ƙwato akwai bindigogi na gargajiya guda huɗu, wuƙaƙe da adduna tara, sanduna uku, tabar wiwi da kuma ƙwayoyi irin su Exol guda 173 da wasu miyagun ƙwayoyi daban-daban.
Haka kuma, jami’an sun kama wasu riƙaƙƙun ’yan daba da suka daɗe suna addabar al’ummar Dorayi, ciki har da Dan Abba, Bola, Baka Kashi, Ramos, Abba Maciji da Abdul Baki.
“Dukkanin ’yan daban 25 da muka kama an gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 16 da ke kan titin Zungeru, kuma an tasa ƙeyarsu zuwa gidan gyaran hali.
“Sauran masu sayar da ƙwayoyi guda shida, ciki har da Rabi’u Hamza, an miƙa su ga hukumar NDLEA don ci gaba da bincike kafin a gurfanar da su a kotu,” in ji Dokta Kofar Mata.
Ya bayyana wannan samame a matsayin babban ci gaba wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
Ya ce unguwanni kamar Dorayi sun sha fama da rikice-rikicen faɗan daba sama da shekaru 20.
Kama waɗannan ɓata-gari zai iya kawo ƙarshen wannan matsala.
Ya ƙara da cewa kwamitin ya ƙunshi jami’an tsaro da jami’an gwamnati domin haɗa kai wajen tsaftace birnin Kano da kuma taimaka wa matasan da suka ɓace su koma turbar gaskiya.
“Kwamitin Haɗin Gwiwa zai ci gaba da jajircewa domin ganin an samar da ingantaccen tsaro da kuma zaman lafiya ba tare da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ba a Kano,” in ji kwamitin.
Ga hotunan wasu daga cikin kayan da kwamitin ya ƙwato:
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwamiti kwayoyi Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Hari: An kashe makiyaya 1 da shanu sama da 100 a Filato
A wasu rahotanni sun ce an kashe makiyayi guda ɗaya da shanu sama da 100 a wasu hare-hare da aka kai hari kan makiyaya a wasu ƙauyuka biyu da ke ƙananan hukumomin Jos ta Kudu da Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Hare-haren da ake zargin wasu ’yan bindiga ne da suka buɗe wa makiyaya wuta a lokacin da suke kiwo, wanda ke nuna rashin tsaro a yankunan da aka daɗe ana fama da rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya, lamarin da ke janyo asarar rayuka.
Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a JigawaSakataren Ƙungiyar Miyetti Allah Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) na jihar Ibrahim Yusuf Babayo ya tabbatar da faruwar lamarin tare da zargin ’yan ƙabilar rukunin Berom daga na da hannu wajen kai harin.
Sai dai shugabannin Ƙungiyar matasan Berom sun musanta zargin da ake yi musu, inda suka yi watsi da hakan a matsayin farfaganda.
Daily Trust ta samu rahoton cewa, harin farko ya faru ne da yammacin ranar Talata a unguwar Gero da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Kudu, yayin da na biyu kuma ya faru ne da safiyar Laraba a unguwar Darwat da ke Ƙaramar hukumar Riyom.
A cewar Babayo, makiyaya uku sun samu raunuka a harin na Gero. A halin yanzu ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa na yin jinya a wani Asibiti da ke Jos, yayin da sauran biyun kuma ke jinya a Asibitin Sojoji da ke barikin Rukuba a Jos.
“A ranar 13 ga Mayu, 2025, matasan Berom daga Gero, Gundumar Ngel a Jos ta Kudu, sun haɗa baki suka farwa makiyayan shanu, inda suka kashe shanu kusan 70.
“Sun yanka wasu daga cikin shanun tare da sace naman, sojojin hedikwatar Operation Safe Haɓen sun shiga tsakani suka kama wasu mutane uku da aka samu da naman shanun da aka yanka,” in ji Babayo.
Ya ci gaba da cewa, “A ranar 14 ga Mayu, 2025, matasan Berom a Darwat sun zo da yawa, suka fara harbin shanu na mambobinmu.
“Sun kashe shanu sama da 40, sun yanka wasu, suka kwashe naman, ba tare da wata tsokana ba, haka kawai suka fara harbe-harbe a kan dabbobin, harin da ake zargin an shirya ne, ba mu da wata kariya, na sanar da hukumar rundunar GOC 3 da kuma daraktan tsaro na jihar halin da ake ciki.”
Babayo ya kuma bayyana cewa waɗannan hare-haren wani ɓangare ne na tada hankali.
Ya ƙara da cewa, “A cikin makonni biyun da suka gabata, an samu irin wannan harin inda aka kai wa makiyaya da shanunsu hari, waɗannan hare-haren sun yi sanadin asarar rayukan mutane da kuma satar dabbobi, a ranar Litinin kaɗai, an ce an samu ɓacewar wani makiyayi, an kuma yi awon gaba da shanu 41 a Bisichi.”
“A kullum ana kashe mu, da alama ana tsokanar mu, muna kira ga gwamnati da ƙasashen duniya da su lura da abin da ke faruwa a Jihar Filato, a matsayinmu na ’yan ƙasa masu bin doka, muna kira ga mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, muna kuma kira ga hukumomin tsaro da su kawo ƙarshen wannan kashe-kashe na rashin hankali da kuma kare Fulani makiyaya daga ci gaba da kai hari,” in ji Babayo.