Aminiya:
2025-08-18@01:44:07 GMT

Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano

Published: 17th, May 2025 GMT

Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Tsaro da Gyaran Matasa, ya kama ’yan daba 31 a wani samame da ya gudana a unguwanni bakwai a jihar.

An kai samamen ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Mayu, 2025 ƙarƙashin jagorancin Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata.

Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno

Unguwannin da aka kai samamen sun haɗa da Ɗorayi, Ja’in, Sharada, Unguwar Dabai, Dukawa, Kabuga, Kofar Mata da sauransu, wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka.

Daga cikin waɗanda aka kama, mutum 25 ana zargin ’yan daba ne, yayin da shida ake zarginsu dallacin miyagun ƙwayoyi.

A cikin kayan da jami’an suka ƙwato akwai bindigogi na gargajiya guda huɗu, wuƙaƙe da adduna tara, sanduna uku, tabar wiwi da kuma ƙwayoyi irin su Exol guda 173 da wasu miyagun ƙwayoyi daban-daban.

Haka kuma, jami’an sun kama wasu riƙaƙƙun ’yan daba da suka daɗe suna addabar al’ummar Dorayi, ciki har da Dan Abba, Bola, Baka Kashi, Ramos, Abba Maciji da Abdul Baki.

“Dukkanin ’yan daban 25 da muka kama an gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 16 da ke kan titin Zungeru, kuma an tasa ƙeyarsu zuwa gidan gyaran hali.

“Sauran masu sayar da ƙwayoyi guda shida, ciki har da Rabi’u Hamza, an miƙa su ga hukumar NDLEA don ci gaba da bincike kafin a gurfanar da su a kotu,” in ji Dokta Kofar Mata.

Ya bayyana wannan samame a matsayin babban ci gaba wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya ce unguwanni kamar Dorayi sun sha fama da rikice-rikicen faɗan daba sama da shekaru 20.

Kama waɗannan ɓata-gari zai iya kawo ƙarshen wannan matsala.

Ya ƙara da cewa kwamitin ya ƙunshi jami’an tsaro da jami’an gwamnati domin haɗa kai wajen tsaftace birnin Kano da kuma taimaka wa matasan da suka ɓace su koma turbar gaskiya.

“Kwamitin Haɗin Gwiwa zai ci gaba da jajircewa domin ganin an samar da ingantaccen tsaro da kuma zaman lafiya ba tare da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ba a Kano,” in ji kwamitin.

Ga hotunan wasu daga cikin kayan da kwamitin ya ƙwato:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamiti kwayoyi Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Kano: NNPP ta yi watsi da sakamakon zaɓen Ghari/Tsanyawa

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano, ta ƙi amincewa da sakamakon zaɓen ɗan majalisar jiha da aka gudanar a mazaɓar Ghari/Tsanyawa.

Jam’iyyar ta ce Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da wasu ’yan siyasa sun yi maguɗi.

Jauro Jatau: Al’umma sun roƙi gwamnati ta samar musu da wutar lantarki APC ta lashe zaɓen cike gurbi a Zariya

Shugaban jam’iyyar na jihar, Kwamared Hashimu Sulaiman Dungurawa, ya shaida wa ’yan jarida cewa INEC ta “tauye wa jama’a haƙƙinsu” bayan ta bayyana ɗan takarar jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Ya ce zaɓen ya kamata a gudanar da shi ne a rumfunan zaɓe 10 da kotun ɗaukaka ƙara ta soke.

NNPP ta ce INEC ta ƙwace sakamakon da aka gudanar a rumfunan 10, tare da yin amfani da tsohon sakamakon da kotu ta riga ta soki.

“A Ghari, jama’a sun yi zaɓe lafiya a rumfunan 10, amma saboda maguɗi da wasu ’yan siyasa da jami’an INEC suka shirya, sai aka bayyana ɗan takarar APC a matsayin wanda ya yi nasara,” in ji jam’iyyar.

NNPP ta kuma zargi INEC da bayyana sakamakon a hedikwatarta ta Kano maimakon a cibiyar tattara sakamako na mazaɓar, abin da ta ce ya bayar da damar tafka maguɗi.

Jam’iyyar ta yi alƙawarin ci gaba da ƙalubalantar abin da ta kira rashin adalci da nuna son kai.

Ta kuma ce sakamakon da jami’an rumfunan zaɓe suka sanya hannu a kai shi ne ya kamata a tabbatar da shi.

Sai dai NNPP ta yaba da zaɓen cike gurbi da aka yi a Shanono/Bagwai inda ɗan takararta ya yi nasara.

Jam’iyyar ta bayyana zaɓen a matsayin mai inganci, ta kuma gode wa jami’an tsaro da kuma jama’a da suka fito ƙwansu da kwarkwata suka kaɗa ƙuri’a.

“Muna girmama jarumtar jama’armu da suka tsaya tare da mu, suka kuma zaɓi ’yan takarar NNPP a dukkanin zaɓukan da aka gudanar,” in ji shugaban jam’iyyar.

INEC da APC ba su ce komai ba tukuna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano: NNPP ta yi watsi da sakamakon zaɓen Ghari/Tsanyawa
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • APC ta nemi INEC ta soke zaɓen cike gurbin Kano
  • APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano
  • An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano
  • Zaɓen cike gurbi: An kama ’yan daba 100 a Bagwai — INEC
  • An kama shi da N25m na sayen kuri’u a zaɓen Kaduna
  • Mali: An kama wasu Manyan Janar-Janar dan kasar Faransa bisa zargin yunkurin juyin mulki
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi