Leadership News Hausa:
2025-05-17@14:48:57 GMT

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

Published: 17th, May 2025 GMT

Za Mu Ci Gaba Da Binciko Mai A Arewa — Ojulari

“Dangote ya taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba wanda ya cancanci yabo. Muna kan tattauna yadda za a kawo karshen rigimar. Nan gaba, za mu yi aikin hadin gwiwa domin tabbatar da samar da wadataccen mai ga al’ummar Nijeriya,” in ji shi.

Ya nuna cewa ta hanyar zaman sulhu za su kawo karshen matsalar, “Nan gaba kadan ba za ku ji wata rigima tsakanin NNPCL da matatar mai ta Dangote ba.

Za mu yi aikin hadin guiwa domin amfanuwar ‘yan kasa.”

Ojulari ya kuma yi tsokaci kan faduwar farashin danyen mai a duniya a baya-bayan nan, wanda ya rage kudaden shiga da ake sa ran Nijeriya za ta samu.

“Wannan raguwar ta shafi kasafin kudin Nijeriya tun da babban bangarenta ya dogara ne kan kudin shigar mai,” in ji shi.

Sai dai ya bayyana cewa kamfanin na NNPC yana kokarin rage kudin gudanar da aiki domin cin gajiyar abin da suke samu daga siyar da mai da iskar gas.

Da yake mayar da martani ga koke-koken jama’a na cewa farashin man fetur na cikin gida ba ya raguwa ko da farashin duniya ya fadi, Ojulari ya bayyana cewa dillalan na bukatar lokaci don daidaitawa.

“Idan sun sayi man fetur a farashi mafi girma kafin faduwar, za su bukaci sayar da wannan tsohon farashin. Amma tare da sababbin sayayya a farashin kananan, muna sa ran farashin gida zai nuna canji,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Ya ƙaryata zargin cewa an ci zarafin waɗanda ake zargin, yana mai cewa an bi doka da ƙa’idoji na ƙasa da na duniya a duk matakan binciken da aka gudanar.

Ya ƙara da cewa bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta an shirya shi ne domin yaudarar jama’a da neman tausayi tare da ɓata suna da amincin rundunar.

Nguroje ya yi gargaɗi game da yaɗa labaran ƙarya da ka iya janyo cikas ga binciken da ake yi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa
  • Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya
  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Minista Ya Ƙaryata Ji-ta-ji-tar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
  • BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa
  • Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista
  • Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo
  • Jagora: Yin Shirun da  Kasashen Duniya Sun Yi Kan ABinda Yake Faruwa A Gaza Abun Mamaki Ne
  • ’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa