Dole Ne Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Samar Da Ayyukan Yi Da Rage Talauci — Bankin Duniya
Published: 17th, May 2025 GMT
Habakar matsayi na kasafin kudi ya inganta a cikin 2024, ta hanyar habaka kudaden shiga. Gibin kasafin kudi ya ragu daga kashi 5.4 na kudin shiga a shekarar 2023 zuwa kashi 3.0 na kudin shiga a shekarar 2024, babban ci gaban da aka samu sakamakon karuwar kudaden shiga na daukacin tarayyar kasar, wanda ya karu daga naira tiriliyan 16.
Rahoton ya kara da cewa hauhawar farashin kayayyaki ya tsaya tsayin daka amma ana sa ran zai fadi zuwa matsakaicin shekara da kashi 22.1 cikin 100 a shekarar 2025, yayin da tsayin daka mai tsayi ya tabbatar da amincin manufofin kudi tare da rage tsammanin hauhawar farashin kayayyaki.
Ko da yake, ya nuna cewa kalubalen shi ne don karfafa kwanciyar hankali na tattalin arzikin kasa da habaka yanayin tattalin arziki ta hanyar zurfafa gyare-gyare mai fa’ida.
“Akwai bukatar tattalin arziki ya samar da karin ayyukan yi masu inganci da kuma rage talauci a tsakanin al’umma.”
Mukaddashin Daraktan Bankin Duniya a Nijeriya, Taimur Samad ya ce, “Nijeriya ta samu ci gaba mai ban sha’awa don maido da kwanciyar hankali a fannin tattalin arziki, tare da ingantuwar yanayin kasafin kudi, yanzu Nijeriya na da damar inganta adadi da ingancin kashe kudade na ci gaba, kara saka hannun jari kan rayuwar Dan’adam, kariyar zamantakewa, da ababen more rayuwa.
“Rarraba dukiyar al’umma na iya fara kaucewa tsarin da ba a dawwama a baya, a maimakon haka wajen biyan manyan bukatu na ci gaban Nijeriya, ciki har da gwamnati ta taka muhimmiyar rawa wajen samar da muhimman ayyukan gwamnati da kuma zama mai ba da damar ci gaban kamfanoni masu zaman kansu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Bankin Duniya Nijeriya Tattalin Arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.
Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.
Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.
Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.
Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.
Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp