Adadin kudaden harkar soji a nahiyar Afirka a bara, musamman a Aljeriya da kasashen kawancen Sahel, ya karu.

A cewar wani bincike da Cibiyar Nazarin Zaman Lafiya ta Duniya ta Stockholm (SIPRI) ta gudanar, kashe kudaden soji a Afirka ya karu zuwa dala biliyan 52.1 a shekarar 2024 a fadin Nahiyar, wanda ya karu da kashi 3 bisa 100 a shekarar 2023 da kuma karuwar kashi 22 cikin 100 a shekarar 2015.

A cewar rahoton na SIPRI, kudaden da ake kashe wa sojojin na Arewacin Afirka ya kai dala biliyan 30.2 a shekarar 2024, ya kuma karu da kashi 4 cikin 100 a shekarar 2024.

Kudaden da Aljeriya da Maroko kadai suka kashe ya kai kashi 90% na adadin kudaden da yankin ya kashe.

A Kasashen kudu da hamadar sahara, Adadin kudin da ake kashewa na soji ya ragu da dalar Amurka biliyan 21.9 a shekarar 2024, dan kadan ya ragu da kashi 3.2 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023 da kashi 13 cikin 100 idan aka kwatanta da 2015.

Kasar Afrika ta Kudu, wadda ta fi kowacce kasa kashe kudi a fannin soji a wannan yanki, an rage kasafin kudin sojojinta na shekara ta hudu a jere, zuwa dala biliyan 2.8 a shekarar 2024, raguwar kashi 6.3 cikin 100 daga shekarar 2023 da kuma raguwar kashi 25 cikin 100 daga shekarar 2015.

Bayanin ya ci gaba da cewa kudaden soji da kawancen kasashen yankin Sahel na AES sukayi wato Mali da Burkina Faso da Nijar sun kashe dala biliyan 2.4 don harkar soji a shekara ta 2024.  

Wadannan kasashe sun yanke hadin gwiwa da Faransa a fannin tsaro.

Burkina Faso ta kara yawan kudaden da take kashewa a wannan fanni da kashi 108 cikin 100 tsakanin shekarar 2021 zuwa 2024, yayin da Nijar ta karu da kashi 56 cikin 100 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2024. Haka abin yake ga Chadi, wadda ta kawo karshen hadin gwiwarta da Faransa a cikin 2024.    

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a shekarar 2024 dala biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya bar Abuja domin ziyarar aiki zuwa ƙasashen Japan da Brazil.

Ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da misalin ƙarfe 11:15 na safiyar Juma’a, inda zai tsaya a Birnin Dubai na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC

Manyan jami’an gwamnati da suka raka shi, sun haɗa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkar Tsaro, Nuhu Ribadu.

Sauran sun haɗa da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila; da Ministan Kuɗi, Wale Edun.

A Japan, Shugaba Tinubu zai halarci Taron Ci Gaban Afirka karo na tara (TICAD9) wanda zai gudana a birnin Yokohama daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta.

Taken taron shi ne “Haɗa Hannu Wajen Samar da Ingantacciyar Mafita ga Afirka”.

Taron zai mayar da hankali kan inganta tattalin arziƙin Afirka, kyautata yanayin kasuwanci, da samar da zaman lafiya, tsaro, da ci gaba mai ɗorewa ta hanyar jari-hujja da ƙirƙire-ƙirƙire daga kamfanoni masu zaman kansu.

Bayan taron Japan, Tinubu zai nufi ƙasar Brazil, domin ziyarar aiki ta kwana biyu daga ranar 24 zuwa 25 ga watan Agusta.

Tinubu zai je ƙasar ne bayan gayyatar da Shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva ya yi masa.

A Brazil, zai gana da shugaban ƙasar, sannan zai halarci taron kasuwanci, kuma ya tattauna hanyoyin bunƙasa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

Tawagarsa za ta kuma yi aiki wajen ƙulla yarjejeniyoyi da haɗin gwiwa da gwamnatin Brazil.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil
  • Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
  • Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
  • Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons
  • NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.