Kudaden da sojojin Afirka suka kashe a bara ya karu da dala biliyan 52 a shekarar 2024
Published: 17th, May 2025 GMT
Adadin kudaden harkar soji a nahiyar Afirka a bara, musamman a Aljeriya da kasashen kawancen Sahel, ya karu.
A cewar wani bincike da Cibiyar Nazarin Zaman Lafiya ta Duniya ta Stockholm (SIPRI) ta gudanar, kashe kudaden soji a Afirka ya karu zuwa dala biliyan 52.1 a shekarar 2024 a fadin Nahiyar, wanda ya karu da kashi 3 bisa 100 a shekarar 2023 da kuma karuwar kashi 22 cikin 100 a shekarar 2015.
A cewar rahoton na SIPRI, kudaden da ake kashe wa sojojin na Arewacin Afirka ya kai dala biliyan 30.2 a shekarar 2024, ya kuma karu da kashi 4 cikin 100 a shekarar 2024.
Kudaden da Aljeriya da Maroko kadai suka kashe ya kai kashi 90% na adadin kudaden da yankin ya kashe.
A Kasashen kudu da hamadar sahara, Adadin kudin da ake kashewa na soji ya ragu da dalar Amurka biliyan 21.9 a shekarar 2024, dan kadan ya ragu da kashi 3.2 cikin dari idan aka kwatanta da shekarar 2023 da kashi 13 cikin 100 idan aka kwatanta da 2015.
Kasar Afrika ta Kudu, wadda ta fi kowacce kasa kashe kudi a fannin soji a wannan yanki, an rage kasafin kudin sojojinta na shekara ta hudu a jere, zuwa dala biliyan 2.8 a shekarar 2024, raguwar kashi 6.3 cikin 100 daga shekarar 2023 da kuma raguwar kashi 25 cikin 100 daga shekarar 2015.
Bayanin ya ci gaba da cewa kudaden soji da kawancen kasashen yankin Sahel na AES sukayi wato Mali da Burkina Faso da Nijar sun kashe dala biliyan 2.4 don harkar soji a shekara ta 2024.
Wadannan kasashe sun yanke hadin gwiwa da Faransa a fannin tsaro.
Burkina Faso ta kara yawan kudaden da take kashewa a wannan fanni da kashi 108 cikin 100 tsakanin shekarar 2021 zuwa 2024, yayin da Nijar ta karu da kashi 56 cikin 100 tsakanin shekarar 2022 zuwa 2024. Haka abin yake ga Chadi, wadda ta kawo karshen hadin gwiwarta da Faransa a cikin 2024.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a shekarar 2024 dala biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da ƙaddamar bincike a game da harin da dakarunta suka kai kan wata cibiyar intanet da ke yankin Gaza, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar ɗimbin fararen hula a jiya Litinin.
Hukumar kare lafiyar fararen hula ta Falasɗinu, ta ce wasu daga cikin makaman da Isra’ila ta harba a jiya Litinin sun faɗa kan kasuwar kwamfuta ta ‘Al-baqa’ da ke gaɓar teku da ke birnin Gaza, kuma a wannan cibiyar kaɗai mutane 24 ne suka rasa raukansu.
Ɗaya daga cikin masu magana da yawun rundunar sojin Isra’ila ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa, tabbatas sun kai hare-hare kan wurare da dama da dakarun Hamas ke fakewa don gudanar da ayyukansu a Gaza, to amma sun ɗauki dukkanin matakan da suka wajaba domin taƙaita illolin farmakin ga fararen hula.
Ahmed al-Nayrab, mai shekaru 26 a duniya kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira da rayukansu a wannan farmaki, ya ce lokacin da aka kai harin, akwai ɗimbin mutane da suka haɗa da masu shan shayi da kuma waɗanda suka zo don samun sadarwar intanet.
Ahmed ya ci gaba da cewa, “abin da ya faru a wannan wuri ba ya da bambanci da kisan kiyashi”, yana mai cewa “a duk inda ka duba sassan gaɓoɓi ne da kuma gangar jikunan mutane ne, yayin da wasu daga cikin gawarwakin ke ci da wuta kana wasu ke kwance jina-jina’’.