A lokacin da yake jawabi a wurin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa da hawansa mulki a watan Mayun 2023, ya ci karo da tsarin kiwon lafiya da ya tabarbare saboda rashin kulawa.

Ya ce, “Gwamnatinmu, ƙarƙashin ginshiƙan shirye-shiryen ceto, nan da nan ta fara tantance abubuwan da asibitoci ke buƙata, inda sakamakon ya zama abin tsoro kuma ya nuna akwai jan-aiki.

“Alal misali, a jihar da ke da mutane kusan miliyan 6 tare da tarin ƙalubale, na’urar duban ɗan tayi ɗaya ce kawai a cikin dukkan cibiyoyin da gwamnati ta mallaka, kuma shi ma duk faci ne a jikinsa da salataf ko’ina! Nan take na ayyana dokar ta-baci a bangaren kiwon lafiya don dawo da ababen more rayuwa, samar da kayan aiki a asibitocinmu tare da samar da kwarin gwiwa da horarwa ga ƙwararru a fannin kiwon lafiya.

“Don inganta ayyukan more rayuwa, mun kuma ba da kwangilar samar da kayayyaki, sakawa, gwadawa, da horar da ma’aikata kan yadda za su yi amfani da na’urorin na zamani.

“Kamar yadda aka saba a wannan gwamnati ta Jihar Zamfara, muna tabbatar da cewa duk kayan aikin da aka kawo da kuma sanya su sun kasance masu inganci kuma sun cika ƙa’idojin da ake da su.

“Bari in jaddada cewa wannan ƙaddamarwar wani bangare ne na sake fasalin jihar Zamfara bakiɗaya a fannin kiwon lafiya, za ku iya tuna cewa mun riga mun samar da manyan asibitocin da aka gyara a garuruwan Ƙaura, Maradun, Maru, da Nasarawa Burkullu.

“Har ila yau, ana shirin ƙaddamar da wasu muhimman asibitocin da suka haɗa da Asibitin Ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura, Gusau, Babban Asibitin Talata Mafara, Shinkafi, da Babban Asibitin Tsafe, da dai sauransu.

“Bugu da ƙari, bayan amincewar majalisar zartarwa ta jiha, Ma’aikatar Lafiya ta fara aikin samar da cikakken kayan aiki ga manyan asibitocin da ke Anka, kuma wannan ya haɗa da samar da kayan aiki na zamani tare da horar da ma’aikatan kiwon lafiya.

“Ya ku ’yan uwa maza da mata, waɗannan ayyukan suna nuna hangen nesan mu na gina tsarin kiwon lafiya na zamani, mai aiki da kuma ɗorewa wanda zai rage yawan tura marasa lafiya zuwa wasu asibitoci a wajen jihar tare da tabbatar da cewa ’yan jihar mu sun sami ingantaccen kulawa kusa da gida.

“Yayin da muke murnar wannan nasarar, ina so in jawo hankalin mahukuntan asibitin kan buƙatar yin taka-tsan-tsan wajen amfani da kuma kula da wannan wuri.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) a Jihar Gombe ta ce ta lalata wata babbar gonar Tabar wiwi a Karamar Hukumar Kaltungo a jihar Gombe.

Hukumar ta kuma ce ta kama miyagun kwayoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025.

’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Kwamandan Hukumar a jihar, Mallam Maijama’a Muhammad ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyarar kulla zumunci da ya kai wa Darakta-Janar na kafar yada labarai mallakar jihar Gombe (GMC), Ibrahim Isa.

Ya ce an kama mutum 69 maza da mata da suke kokarin shigar da miyagun kwayoyi cikin jihar a wasu lokuta.

Muhammad ya kuma ce hukumar na amfani da dabarun rage samarwa da rage bukatar miyagun kwayoyi, tare da kira ga karin hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki.

Daga nan sai ya gode wa gwamnatin Jihar bisa bayar da motocin aiki guda biyu da gyaran ofishin hukumar, da inganta cibiyar farfado da masu shan miyagun kwayoyi

A nasa jawabin, Daktan kafar yada labaran, Ibrahim Isa, ya tabbatar wa NDLEA da goyon bayan kafar ta GMC, ciki har da bayar da lokacin watsa shirye-shirye kyauta, tare da alkawarin ci gaba da yin aiki tare wajen yakar ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
  • Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari
  • Gwamna Namadi Ya Nada Kwamishina Na Farko A Ma’aikatar Cigaban Kiwon Dabbobi
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara
  • NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe
  • Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Liberia Don Inganta Noman Shinkafa
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Lafiyar Tinubu kalau – Soludo