HausaTv:
2025-05-17@03:05:55 GMT

Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-hare A Kasar Yemen

Published: 16th, May 2025 GMT

Majiyar tsaron kasar Yemen ta ce; Jragen HKI sun kai wasu jerin hare-hare akan tasoshin jiragen ruwa na Hudaidah, da Salif a gudunar Hudaidah dake yammacin kasar.

Majiyar tsaron ta Yemen ta ci gaba da cewa; An yi amfani da bama-bamai masu yawa da aka jefa akan wadannan tasoshin jiragen ruwan,kuma fiye da jiragen sama na yaki 10 ne su ka kai harin.

Wata majiyar HKI ta fada wa tashar talabijin din “Kan”  cewa; manufar kai wadannan hare-haren su ne kakaba wa Yemen takunkumi ta ruwa.”

A ranar 6 ga watan nan na Mayu da ake ciki, ma HKI ta kai wani harin akan filin saukar jiragen saman a Sana’a tare da kona jirgen saman kasar da dama.

Ita dai kungiyar “Ansarullah” ta kasar Yemen ta sha bayyana cewa ba za ta daina kai wa HKI hare-hare ba har sai idan ta daina kai wa Gaza hari.

Jagoran kungiyar ta “Ansarullah” Sayyid Abdulmalik Al-Husi ya bayyana cewa; Matsayar da Yemen ta dauka na taimakawa Gaza, ba zai fuskanci tawaya ba ko ya ja da baya, zai ci gaba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Human Rights Watch : Katange Gaza mataki ne na share al’umma

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da amfani da katangewar da ta yi wa Gaza a matsayin makamin kawar da wata al’umma.

A wani rahoto data fitar yau  Alhamis, kungiyar ta Human Rights Watch ta zargi Isra’ila da yin amfani da shingen da aka yi wa Zirin Gaza a matsayin “wani makami na share al’umma,” yayin da hukumomin Isra’ila suka hana shigar da duk wani agajin jin kai cikin yankin Falasdinu tun ranar 2 ga Maris.

Katange zirin da Isra’ila ta yi ya fi karfin dabarun soji, ya kai wani yunkuri na share al’umma inji Federico Borello, darakan zatarwa mai riko na kungiyar a cikin wata sanarwa da ya caccaki shirin Isra’ila na zaunar da mutanan Gaza miliyan biyu a wani shinge da aka takaice lamura tare da maida yankin wani kufai da ba za’a iya rayuwa a ciki ba.

Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a zirin Gaza a ranar 18 ga Maris, ta hanyar keta yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyar Hamas, inda suka kashe dubban Falasdinawa tare da raunata wasu da dama.

Akalla Falasdinawa 53,010 aka kashe, akasari mata da kananan yara, yayin da wasu 119,998 suka jikkata a munanan hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta fada bay abaya nan cewa a shirye ta ke ta shiga tattaunawa cikin gaggawa domin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta mai dorewa a zirin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Mashawarci tsohon shugaban Ƙasa kan Sufuri Jiragen Sama ya rasu
  • Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa
  • Sojojin Yemen Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Babban Filin Jirgin Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Human Rights Watch : Katange Gaza mataki ne na share al’umma
  • Iran Ta Nuna Damuwarta Akan Tabarbarewar Harkokin Tsaro A Kasar Libya
  • Shuagabn Kasar Amurka Ya  Sanar Da Kusancin Kulla  Yarjejeniya Da Iran
  • Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ta Musayar Kai Hare-Hare Kan Junansu
  • Sojojin HKI  Sun Sake Yin Kisan Kiyashi Mai Firgitarwa A Cikin Asibitin Gaza