BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban Runkunin Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya bayyana shirinsa na karya farashin shinkafa a Najeriya, yana mai cewa nan gaba kadan wadanda suka saye shinkafar suka boye suna jiya ta yi tsada, za su tafka mummunar asara.
Dan kasuwar ya kuma bayyana cewa suna tattunawa da Shugaban Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, kan hanyoyin da za su bi domin ganin sun daidaita farashin siminti.
BUA ya bayyana haka ne a yayin ganawarsa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Fadar Shugaban Kasa.
“Farashin kayan abinci na saukowa a Najeriya kuma muna yin duk abin da za mu iya na ganin cewa mun mara wa gwamnati baya a kan hakan,” kamar yadda ya bayyana,
Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina FasoYa ci gaba da cewa, “Kun san shugaban kasa ya dage harajin shiga da kayan abinci kamar shinkafa da masara da alkama da dawa.
“A lokacin farashinsu ya tsahi sosai; a bara sai dai kudin buhun shinkafa ya kai N100,000, alkama da fulawa suka kai N80,000, masara ta kai N60,000, taliya kuma kwali ya kai N20,000.”
Ya bayyana cewa abin da ke faruaw shi ne, mutane ke saye shansherar shinkafa a lokacin kaka su boye, daga baya su tsawwarala farashin.
“Idan kaka ta wuce sai su ninka farashin. Wanna shi ne matsalar, kuma ba manoma ke cin moriyar karin farshin ba, saboda tun da kaka sun riga sun sayar wa ’yan kasuwar da ton daya a kan N400,000 ko N500,000.
“Su kuma wadanda suka saye suka boye, da zarar kaka ta wuce sai su ninka kudin ton zuwa N500,000,” in ji BUA.
Ya bayyana cewa amma janye harajin shigo da abinci da gwamnati ta yi ya rikita lissafin masu boye abincin, kuma a halin yanzu sun fara kokawa saboda irin asarar da suke tafkawa.
Ya ce, “duk da cewa ya kamata mu kare manomanmu, amma kuma yana da muhimmanci mu fahimci cewa yawan al’ummar kasar nan ya kai mutum miliyan 250, kuma yawancinsu ana sayar musu da kaya da tsadar da ta wuce misali, a sakamakon abin da wasu tsirarun kamfanoni ko mutane ke yi.
“Muna fata zuwa karshen wannan shekara farashin shinkafa ba zai fi yadda yake a yanzu ba. Na tabbata da zarar lokaci ya yi manoma za su samu shinkafa a farashin da suka saba, kuma ba zai karu ba a kasuwa, saboda mutane sun shirin masu boye ta, kuma idan sun boyen ma, asara suke yi,” in ji dan kasuwan.
Game da tsadar siminit, BUA ya danganta matsalar a faduwar darajar naira a kan dala.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farashin shinkafa shanshera
এছাড়াও পড়ুন:
An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
Mahukunta a Jakarta, babban birnin Indonesia, sun haramta sayarwa da cin naman karnuka, kyanwa da jemagu, a wani yunƙuri na daƙile yaɗuwar cutar nan ta Mahaukacin Kare da a Turance ake kira rabies.
Da yake jawabi a wannan Talatar, Gwamnan Jakarta, Pramono Anung, ya sanar da rattaba hannu kan dokar da ke hana duk wani nau’in kasuwanci ko mu’amala da waɗannan dabbobi a matsayin abinci.
An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara baDokar wadda za ta fara aiki bayan wa’adin watanni shida, ta ayyana cewa duk wanda ya karya ta zai iya fuskantar hukunci daga kan gargaɗi na rubuce har zuwa janye lasisin kasuwanci gaba ɗaya.
Indonesia na daga cikin ƙasashen da har yanzu ake cin naman karnuka da kyanwa, duk da cewa wasu birane sun daina wannan al’ada a ’yan shekarun nan.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin dabbobi sun yaba da sabon matakin, suna mai cewa ya dace da manufofin kare lafiyar al’umma.
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce mutane da dama kan mutu da cutar rabies a kowace shekara a Indonesia, inda rahoton Ma’aikatar Lafiya ya nuna cewa mutane 25 suka mutu daga watan Janairu zuwa Maris 2025.
Duk da cewa a yawancin yankunan Indonesia ana kallon karnuka a matsayin dabbobin da ba su da tsabta, wasu ƙananan ƙabilu na ci har yanzu, musamman ma saboda samun naman a farashi mai sauƙi.