BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban Runkunin Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya bayyana shirinsa na karya farashin shinkafa a Najeriya, yana mai cewa nan gaba kadan wadanda suka saye shinkafar suka boye suna jiya ta yi tsada, za su tafka mummunar asara.
Dan kasuwar ya kuma bayyana cewa suna tattunawa da Shugaban Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, kan hanyoyin da za su bi domin ganin sun daidaita farashin siminti.
BUA ya bayyana haka ne a yayin ganawarsa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Fadar Shugaban Kasa.
“Farashin kayan abinci na saukowa a Najeriya kuma muna yin duk abin da za mu iya na ganin cewa mun mara wa gwamnati baya a kan hakan,” kamar yadda ya bayyana,
Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina FasoYa ci gaba da cewa, “Kun san shugaban kasa ya dage harajin shiga da kayan abinci kamar shinkafa da masara da alkama da dawa.
“A lokacin farashinsu ya tsahi sosai; a bara sai dai kudin buhun shinkafa ya kai N100,000, alkama da fulawa suka kai N80,000, masara ta kai N60,000, taliya kuma kwali ya kai N20,000.”
Ya bayyana cewa abin da ke faruaw shi ne, mutane ke saye shansherar shinkafa a lokacin kaka su boye, daga baya su tsawwarala farashin.
“Idan kaka ta wuce sai su ninka farashin. Wanna shi ne matsalar, kuma ba manoma ke cin moriyar karin farshin ba, saboda tun da kaka sun riga sun sayar wa ’yan kasuwar da ton daya a kan N400,000 ko N500,000.
“Su kuma wadanda suka saye suka boye, da zarar kaka ta wuce sai su ninka kudin ton zuwa N500,000,” in ji BUA.
Ya bayyana cewa amma janye harajin shigo da abinci da gwamnati ta yi ya rikita lissafin masu boye abincin, kuma a halin yanzu sun fara kokawa saboda irin asarar da suke tafkawa.
Ya ce, “duk da cewa ya kamata mu kare manomanmu, amma kuma yana da muhimmanci mu fahimci cewa yawan al’ummar kasar nan ya kai mutum miliyan 250, kuma yawancinsu ana sayar musu da kaya da tsadar da ta wuce misali, a sakamakon abin da wasu tsirarun kamfanoni ko mutane ke yi.
“Muna fata zuwa karshen wannan shekara farashin shinkafa ba zai fi yadda yake a yanzu ba. Na tabbata da zarar lokaci ya yi manoma za su samu shinkafa a farashin da suka saba, kuma ba zai karu ba a kasuwa, saboda mutane sun shirin masu boye ta, kuma idan sun boyen ma, asara suke yi,” in ji dan kasuwan.
Game da tsadar siminit, BUA ya danganta matsalar a faduwar darajar naira a kan dala.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farashin shinkafa shanshera
এছাড়াও পড়ুন:
Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa da shi da Sule Lamido har yanzu suna kan kujerar mulki, da sun fito ƙarara sun ƙalubalanci Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Amaechi ya bayyana haka ne a wajen ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar Sule Lamido mai suna ‘Being True to Myself’ da aka gudanar a Abuja.
Ko yanzu aka yi zaɓe Tinubu ne zai yi nasara — Oshiomhole DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A Najeriya“Da mun fito da ƙarfinmu, mun ƙalubalanci gwamnati, mun kalubalanci shugaban ƙasa,” in ji Amaechi.
“Haka muka saba a lokacin muna Gwamnoni. Muna da kishin ƙasa da ƙwarin gwiwar sauya al’amura.”
Ya bayyana yadda dangantakar siyasar da ke tsakaninsa da Lamido, inda ya ce duk da kasancewar suna da alaƙa a wancan lokaci, sun raba gari ne lokacin da Lamido ya ƙi komawa jam’iyyar APC domin su haɗa ƙarfi wajen kayar da tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan.
“A lokacin, Lamido ya zaɓi kafa sabuwar jam’iyya – SDP, amma mu mun yarda cewa za mu fi samun nasara a jam’iyyar APC,” in ji Amaechi.
“Wannan ne ya sa hanyoyinmu suka rabu.”
Shugaba Tinubu, wanda Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya wakilta a taron, ya ce shugaban ƙasa ya amince da mahawara mai ma’ana, amma hakan ba zai hana shi yi wa ƙasar nan abin da ya dace ba.
Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ma ya yi jawabi a wajen taron, inda ya bayyana Lamido a matsayin jagoran da ke da gaskiya da tsayawa kan aƙidarsa, inda ya ce lokacin da Lamido ke Ministan Harkokin Waje, ya taimaka wajen dawo da mutuncin Najeriya a idon duniya.
Obasanjo ya ce, “Sule ya taɓa faɗa, ‘Idan ka ga ban cancanta ba, ka ba ni minti biyar kawai na yi murabus. Amma ka da ka tambaye ni takardar murabus da ba ta da kwanan wata.’ Na girmama wannan matsayi nasa.”
Tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, Farfesa Attahiru Jega, wanda ya wakilci Janar Abdulsalami Abubakar, ya jinjina wa littafin Lamido da cewa ya bayyana tarihin siyasar Najeriya da darusan da matasa za su amfana da su.
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dokta Iyorchia Ayu, wanda ya yi nazari a kan littafin, ya soki gwamnatin APC da cewa ta zama annoba ga Najeriya.
Ya buƙaci Lamido da ya ci gaba da rubuta littattafai domin su zama jagora ga ’yan Najeriya.