Aminiya:
2025-08-15@15:05:47 GMT

BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa

Published: 16th, May 2025 GMT

Shugaban Runkunin Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya bayyana shirinsa na karya farashin shinkafa a Najeriya, yana mai cewa nan gaba kadan wadanda suka saye shinkafar suka boye suna jiya ta yi tsada, za su tafka mummunar asara.

Dan kasuwar ya kuma bayyana cewa suna tattunawa da Shugaban Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, kan hanyoyin da za su bi domin ganin sun daidaita farashin siminti.

BUA ya bayyana haka ne a yayin ganawarsa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Fadar Shugaban Kasa.

“Farashin kayan abinci na saukowa a Najeriya kuma muna yin duk abin da za mu iya na ganin cewa mun mara wa gwamnati baya a kan hakan,” kamar yadda ya bayyana,

Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa Ƙungiya mai alaƙa da Alƙa’ida ta yi iƙirarin kashe sojoji 200 a Buarkina Faso

Ya ci gaba da cewa, “Kun san shugaban kasa ya dage harajin shiga da kayan abinci kamar shinkafa da masara da alkama da dawa.

“A lokacin farashinsu ya tsahi sosai; a bara sai dai kudin buhun shinkafa ya kai N100,000, alkama da fulawa suka kai N80,000, masara ta kai N60,000, taliya kuma kwali ya kai N20,000.”

Ya bayyana cewa abin da ke faruaw shi ne, mutane ke saye shansherar shinkafa a lokacin kaka su boye, daga baya su tsawwarala farashin.

“Idan kaka ta wuce sai su ninka farashin. Wanna shi ne matsalar, kuma ba manoma ke cin moriyar karin farshin ba, saboda tun da kaka sun riga sun sayar wa ’yan kasuwar da ton daya a kan N400,000 ko N500,000.

“Su kuma wadanda suka saye suka boye, da zarar kaka ta wuce sai su ninka kudin ton zuwa N500,000,” in ji BUA.

Ya bayyana cewa amma janye harajin shigo da abinci da gwamnati ta yi ya rikita lissafin masu boye abincin, kuma a halin yanzu sun fara kokawa saboda irin asarar da suke tafkawa.

Ya ce, “duk da cewa ya kamata mu kare manomanmu, amma kuma yana da muhimmanci mu fahimci cewa yawan al’ummar kasar nan ya kai mutum miliyan 250, kuma yawancinsu ana sayar musu da kaya da tsadar da ta wuce misali, a sakamakon abin da wasu tsirarun kamfanoni ko mutane ke yi.

“Muna fata zuwa karshen wannan shekara farashin shinkafa ba zai fi yadda yake a yanzu ba. Na tabbata da zarar lokaci ya yi manoma za su samu shinkafa a farashin da suka saba, kuma ba zai karu ba a kasuwa, saboda mutane sun shirin masu boye ta, kuma idan sun boyen ma, asara suke yi,” in ji dan kasuwan.

Game da tsadar siminit, BUA ya danganta matsalar a faduwar darajar naira a kan dala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farashin shinkafa shanshera

এছাড়াও পড়ুন:

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari
  • Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 126
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125
  • Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Liberia Don Inganta Noman Shinkafa
  • Iran: Janar Hatami ya karbi bakuncin babban hafsan hafsoshin sojin Afirka ta kudu
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita