Aminiya:
2025-09-17@21:51:32 GMT

Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa

Published: 16th, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun kai wani mummunan harin ramuwar gayya kan sansanonin ’yan ta’adda a Dajin Sambisa, inda suka kashe mayaƙa da dama tare da tarwatsa maɓoyar miyagun.

Sojoji sun ƙaddamar da wannan farmaki ne bayan kisan abokan aikinsu huɗu da ’yan ta’adda suka yi a farkon wannan makon.

Kai tsaye sojojin suka kai hari kan sansanonin ’yan ta’addar da ke Garin Malam Ali da Garin Glucose da kuma da Ukuba, waɗanda ke cikin Dajin Sambisa.

Wannan matakin da aka ɗauka ya biyo bayan jerin hare-hare da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai a ranar Talata kan sansanonin sojoji guda uku a Rann da Gajiram da kuma da Dikwa a Jihar Borno, wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojoji hudu.

NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027? An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina

Duk da cewa sojojin sun yi nasarar murƙushe wadancan hare-haren na farko, tare da yi wa ’yan tayar da ƙayar bayan ɓarna a Dikwa da Gajiram, aikin ramuwar gayya da ya biyo baya na nufin gurgunta ƙarfin ’yan ta’addar.

Majiyoyin soji, waɗanda suka nemi a sakaya sunansu saboda muhimmancin lamarin, sun bayyana cewa haɗin gwiwar da aka yi da mayaƙan Civilian CJTF ya ɗauki sama da sa’o’i shida, daga misalin karfe 6 na safe a ranar Laraba har zuwa tsakar rana a ranar Alhamis.

Wani hafsan soja ya bayyana cewa, “Aikin ba mai sauƙi ba ne, amma duk mun yi farin ciki da nasarar da aka samu,” yana mai jaddada ƙudurinsu na ci gaba da yaƙi.

Ya ci gaba da cewa, “Ana ci gaba da aikin, muna cikin shirin yaƙi, kuma ya kamata mu yi nasara wannan yakin.”

Jami’in ya kuma tabbatar da cewa wasu ’yan ta’addar sun gudu da raunukan harbin bindiga, inda suka bar makamai da kayan aiki, ciki har da kayan hada abubuwan fashewa, yayin da aka “kashe” da dama daga cikinsu.

Babban Jami’in Yada Labarai na Sojoji a Hedikwatar Rundunar Sojoji ta Kasashe (MNJTF) a N’djamena, Chadi, Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, ya tabbatar da wannan aikin, da cewa, “Dakarun Operation Hadin Kai na Arewa maso Gabas da Civilian JTF sun tarwatsa maɓoyar ’yan ta’adda a Dajin Sambisa a ranar 15 ga Mayu, 2025.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan ta’addar sun tsere, inda suka bar makamai, alburusai, da kayan haɗa bama-bamai. Wannan aikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na ƙwace Dajin Sambisa da kuma daƙile ayyukan ’yan ta’adda.”

Nasarar wannan aikin ta nuna ƙudirin rundunar sojin Najeriya na ci gaba da bin diddigi tare da raunana ƙarfin ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas bayan hare-hare kan dakarunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare hari yan ta addar yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.

Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.

Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.

“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.

Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.

Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin