Aminiya:
2025-11-03@03:12:29 GMT

Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa

Published: 16th, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun kai wani mummunan harin ramuwar gayya kan sansanonin ’yan ta’adda a Dajin Sambisa, inda suka kashe mayaƙa da dama tare da tarwatsa maɓoyar miyagun.

Sojoji sun ƙaddamar da wannan farmaki ne bayan kisan abokan aikinsu huɗu da ’yan ta’adda suka yi a farkon wannan makon.

Kai tsaye sojojin suka kai hari kan sansanonin ’yan ta’addar da ke Garin Malam Ali da Garin Glucose da kuma da Ukuba, waɗanda ke cikin Dajin Sambisa.

Wannan matakin da aka ɗauka ya biyo bayan jerin hare-hare da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai a ranar Talata kan sansanonin sojoji guda uku a Rann da Gajiram da kuma da Dikwa a Jihar Borno, wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojoji hudu.

NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027? An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina

Duk da cewa sojojin sun yi nasarar murƙushe wadancan hare-haren na farko, tare da yi wa ’yan tayar da ƙayar bayan ɓarna a Dikwa da Gajiram, aikin ramuwar gayya da ya biyo baya na nufin gurgunta ƙarfin ’yan ta’addar.

Majiyoyin soji, waɗanda suka nemi a sakaya sunansu saboda muhimmancin lamarin, sun bayyana cewa haɗin gwiwar da aka yi da mayaƙan Civilian CJTF ya ɗauki sama da sa’o’i shida, daga misalin karfe 6 na safe a ranar Laraba har zuwa tsakar rana a ranar Alhamis.

Wani hafsan soja ya bayyana cewa, “Aikin ba mai sauƙi ba ne, amma duk mun yi farin ciki da nasarar da aka samu,” yana mai jaddada ƙudurinsu na ci gaba da yaƙi.

Ya ci gaba da cewa, “Ana ci gaba da aikin, muna cikin shirin yaƙi, kuma ya kamata mu yi nasara wannan yakin.”

Jami’in ya kuma tabbatar da cewa wasu ’yan ta’addar sun gudu da raunukan harbin bindiga, inda suka bar makamai da kayan aiki, ciki har da kayan hada abubuwan fashewa, yayin da aka “kashe” da dama daga cikinsu.

Babban Jami’in Yada Labarai na Sojoji a Hedikwatar Rundunar Sojoji ta Kasashe (MNJTF) a N’djamena, Chadi, Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, ya tabbatar da wannan aikin, da cewa, “Dakarun Operation Hadin Kai na Arewa maso Gabas da Civilian JTF sun tarwatsa maɓoyar ’yan ta’adda a Dajin Sambisa a ranar 15 ga Mayu, 2025.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan ta’addar sun tsere, inda suka bar makamai, alburusai, da kayan haɗa bama-bamai. Wannan aikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na ƙwace Dajin Sambisa da kuma daƙile ayyukan ’yan ta’adda.”

Nasarar wannan aikin ta nuna ƙudirin rundunar sojin Najeriya na ci gaba da bin diddigi tare da raunana ƙarfin ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas bayan hare-hare kan dakarunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare hari yan ta addar yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific

Babban Kwamishinan Kare Hakkin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya soki hare-haren sama da Amurka ta kai wa jiragen ruwa a yankin Caribbean da Pacific, wanda ya kasance keta dokokin kare hakkin dan adam na duniya.

“An ruwaito cewa an kashe mutane sama da 60 a jerin hare-haren da sojojin Amurka ke kai wa jiragen ruwa a Caribbean da Pacific tun farkon watan Satumba, wadanda ake zargin suna da hannu a safarar miyagun kwayoyi, a cikin wani yanayi da ba su da hujja a karkashin dokokin kasa da kasa,” in ji Volker Turk a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a.

Babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana hare-haren a matsayin “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya bukaci Washington da ta “kawo karshen irin wadannan hare-hare ta kuma dauki dukkan matakan da suka dace don hana kisan gillar da ake yi wa mutanen da ke cikin wadannan jiragen ruwa ba bisa ka’ida ba, ba tare da la’akari da laifukan da ake zarginsu da aikatawa ba.”

Amurka ta yi ikirarin cewa wadannan ayyuka wani bangare ne na yaki da safarar miyagun kwayoyi da ta’addanci.

Duk da haka, Turk ya nuna cewa yaki da safarar miyagun kwayoyi a kan iyakoki “al’amari ne na tilasta bin doka.”

“Dangane da ƙarancin bayanai da hukumomin Amurka suka bayyana a bainar jama’a, da alama mutanen da ke cikin jiragen ruwan da aka kai hari ba su da wata barazana ga rayukan wasu, kuma ba a yi amfani da karfin soji mai tsanani a kansu ba a karƙashin dokokin kasa da kasa,” in ji shi.

Volker Turk ya yi kira da a “yi bincike mai zaman kansa cikin sauri, kuma ya yi kira ga Amurka da ta yaki fataucin na haramtacciyar hanya ta hanyar kamawa, da gurfanar da wadanda ake tuhuma cikin adalci, da kuma bin ka’ida.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar