Aminiya:
2025-07-04@13:05:57 GMT

Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa

Published: 16th, May 2025 GMT

Sojojin Najeriya sun kai wani mummunan harin ramuwar gayya kan sansanonin ’yan ta’adda a Dajin Sambisa, inda suka kashe mayaƙa da dama tare da tarwatsa maɓoyar miyagun.

Sojoji sun ƙaddamar da wannan farmaki ne bayan kisan abokan aikinsu huɗu da ’yan ta’adda suka yi a farkon wannan makon.

Kai tsaye sojojin suka kai hari kan sansanonin ’yan ta’addar da ke Garin Malam Ali da Garin Glucose da kuma da Ukuba, waɗanda ke cikin Dajin Sambisa.

Wannan matakin da aka ɗauka ya biyo bayan jerin hare-hare da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai a ranar Talata kan sansanonin sojoji guda uku a Rann da Gajiram da kuma da Dikwa a Jihar Borno, wanda ya yi sanadiyar mutuwar sojoji hudu.

NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027? An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina

Duk da cewa sojojin sun yi nasarar murƙushe wadancan hare-haren na farko, tare da yi wa ’yan tayar da ƙayar bayan ɓarna a Dikwa da Gajiram, aikin ramuwar gayya da ya biyo baya na nufin gurgunta ƙarfin ’yan ta’addar.

Majiyoyin soji, waɗanda suka nemi a sakaya sunansu saboda muhimmancin lamarin, sun bayyana cewa haɗin gwiwar da aka yi da mayaƙan Civilian CJTF ya ɗauki sama da sa’o’i shida, daga misalin karfe 6 na safe a ranar Laraba har zuwa tsakar rana a ranar Alhamis.

Wani hafsan soja ya bayyana cewa, “Aikin ba mai sauƙi ba ne, amma duk mun yi farin ciki da nasarar da aka samu,” yana mai jaddada ƙudurinsu na ci gaba da yaƙi.

Ya ci gaba da cewa, “Ana ci gaba da aikin, muna cikin shirin yaƙi, kuma ya kamata mu yi nasara wannan yakin.”

Jami’in ya kuma tabbatar da cewa wasu ’yan ta’addar sun gudu da raunukan harbin bindiga, inda suka bar makamai da kayan aiki, ciki har da kayan hada abubuwan fashewa, yayin da aka “kashe” da dama daga cikinsu.

Babban Jami’in Yada Labarai na Sojoji a Hedikwatar Rundunar Sojoji ta Kasashe (MNJTF) a N’djamena, Chadi, Laftanar Kanar Olaniyi Osoba, ya tabbatar da wannan aikin, da cewa, “Dakarun Operation Hadin Kai na Arewa maso Gabas da Civilian JTF sun tarwatsa maɓoyar ’yan ta’adda a Dajin Sambisa a ranar 15 ga Mayu, 2025.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan ta’addar sun tsere, inda suka bar makamai, alburusai, da kayan haɗa bama-bamai. Wannan aikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na ƙwace Dajin Sambisa da kuma daƙile ayyukan ’yan ta’adda.”

Nasarar wannan aikin ta nuna ƙudirin rundunar sojin Najeriya na ci gaba da bin diddigi tare da raunana ƙarfin ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas bayan hare-hare kan dakarunta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare hari yan ta addar yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Kwalejin Koyar Da Aikin Jinya Ta Jigawa Za Ta Fara Bada Shaidar Babbar Difiloma

Tsangayar Kwalejin koyar da aikin Jinya ta Jihar Jigawa dake garin Birnin kudu ta gudanar da bikin kaddamar da sabbin dalibai 116 da za su yi karatun difloma ta kasa da babbar difloma ta kasa karon farko na shekarar karatu ta 2024 zuwa 2025.

A jawabinsa wajen taron kaddamar  da daliban,  kwamishinan ma’aikatar lafiya na jihar Jigawa Dr. Muhammad Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin sa na farko daga samun wannan mukami shi ne batun kafa hukumar Gudanarwar Kwalejin da sake fasalin Kwalejin, wanda hakan ya bada damar tantancewa da kuma samun amincewar Cibiyar kula da makarantun aikin Jinya ta Najeriya.

Yana mai cewar, daukar wannan mataki ya bada damar kara yawan dalibai da Kwalejin take dauka daga 120 zuwa 240, wanda hakan zai bada damar yaye dalibai masu yawa.

A cewarsa, jihar tana da ma’aikatan jinya 1,669 wanda ke nuni da gibin 1,883 in aka kwatanta da bukatar irin wadannan ma’aikata 3,552 domin kula da marasa lafiya a asibitoci.

Dr Kainuwa ya kuma taya murna ga tsangayoyin Kwalejin da ke Babura da Birnin kudu bisa kyakkyawan sakamako da suka samu a jarrabawar da ta gabata, inda su ka zamo kan gaba a tsakanin jihohin kasar nan.

Ya bayyana kiwon lafiya a matsayin kan gaba cikin kudurorin Gwamna Malam Umar Namadi guda 12, yana mai jaddada aniyar gwamnati na cigaba da bada kulawa sosai ga harkokin lafiya wanda yanzu haka ana inganta matsakaitan asibitoci 181 da kayan aiki da sauransu.

A jawabin shugaban Hukumar Gudanarwar Kwalejin Malam Salele Abdul, ya bukaci iyayen dalibai da kada su saki hannu bayan samun guraben karatu a kwalejin, domin kuwa akwai bukatar cigaba da ba su kulawa domin su kai ga nasara zuwa karshen karatunsu.

Malam Salele Abdul ya bayyana kwamishinan lafiya Dr Muhammad Kainuwa a matsayin Garkuwan Aikin Jinya bisa nasarorin da aka cimma a lokacinsa.

Kazalika, ya godewa wakilan hukumar gudanarwar da shugabannin Kwalejin bisa gudummawar da su ke bayarwa ga cigaban harkokin kealejin.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban Kwalejin koyar da Aikin Jinya ta Jihar Jigawa, Malam Garba Adamu, wanda ya bayyana kudurinsa na ci gaba da samar da kyakkyawan yanayin koyo da koyarwa, ya kuma baiwa iyayen dalibai tabbacin horas da ‘ya’yansu kan doron Ilimi da kyakkyawar tarbiyya.

Daraktar Kwalejin Aikin Jinya Hajiya Rasheeda Musa Ya’u ta gabatar da sabbin daliban 116 maza da Mata ga Magatardar Kwalejin Malam Muhammad Sale Korau wanda ya lakana musu rantsuwar kaddamarwa.

Shima a jawabinsa, shugaban kwamatin shirye shiryen taron kuma shugaban sashen koyar da Aikin Jinya na kwalejin Malam Abubakar Garba Muhammad, ya ce bikin kaddamar da daliban na daga cikin sharuddan Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’oi da Manyan Makarantu ta Kasa wato (JAMB) domin fara karatun Difloma ta kasa da Babbar Difloma ta kasa a fannin aikin jiyya.

Ya kuma godewa dukkan wadanda suka bada gudummawa wajen samun nasarar taron.

Sakataren kungiyar ma’aikatan Jiyya ta kasa reshen jihar Jigawa Comrade Nurse Kamal Ahmad ya isar da sakon shugaban kungiyar ga taron, yayin da mukaddashin shugaban sashen kula da ayyukan jiyya na ma’aikatar lafiya Nurse Aminu Isa da iyalai da abokan arzikin dalibai na daga cikin maharta taron.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  • Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Kwalejin Koyar Da Aikin Jinya Ta Jigawa Za Ta Fara Bada Shaidar Babbar Difiloma
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare
  • Magajin Garin Birnin Tehran Ya Karyata Da’awar ‘Yan Sahayoniyya
  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno