Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
Published: 16th, May 2025 GMT
Aƙalla mutum 10 ne suka rasu, yayin da aka sace shanu da dama a wani sabon rikici da ya ɓarke a Ƙaramar Hukumar Riyom da ke Jihar Filato.
Sabon rikicin ya samo asali ne daga lalata gonaki, sace shanu, da kuma kai wa dabbobi hari, wanda mutane daga ɓangaren Fulani da Berom ke zargin juna da aikatawa.
Ce-ce-ku-ce ya ɓarke kan bayyanar Sheikh Alƙali a shirin ‘Gabon talkshow’ Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS
A cewar sanarwar da rundunar Operation Safe Haven ta fitar, matsalar ta fara ne a ranar Litinin, 12 ga watan Mayu, 2025, bayan wasu matasa da ake zargi sun kashe shanu da suka shiga gonakinsu a ƙauyen Dayan, da ke Ƙaramar Hukumar Riyom.
Wasu da ake zargin makiyaya ne sun kai harin ramuwar gayya ƙauyen Danchindo da yammacin a ranar 13 ga watan Mayu, inda suka kashe mutane huɗu.
A ranar 14 ga watan Mayu, an kashe shanu 26, wasu kuma sun jikkata a ƙauyen Darwat, lamarin da ake zargin ramuwar gayya ce saboda kashe mutane da aka yi.
Daga bisani wasu da ake zargin ‘yan bindigar Fulani ne sun kai hari wani ƙauye da ke kusa da al’ummar Wereng Kam, inda suka kashe mutane shida.
Bayan samun rahoton tashin hankali a Riyom, jami’an haɗin gwiwar tsaro sun shiga tsakani tare da ganawa da wakilan jama’a domin kwantar da tarzoma, da kuma gargaɗin jama’a kan ɗaukar doka a hannunsu.
A bisa zargin sace shanu da kisa, an kama mutum ɗaya wanda ake ci gaba da bincike a kansa, tare da ƙwato shanu 130 a hannunsa.
Sanarwar ta kuma ce, tsayin dakan da sojoji suka yi ne ya hana maharan ƙone ƙauyen Wereng gaba ɗaya.
An fara sintiri domin kama waɗanda suka gudu, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da kasancewa a yankin domin wanzar da zaman lafiya.
Manjo Janar Folusho Oyinlola, kwamandan Operation Safe Haven kuma shugaban runduna ta 3, ya kai ziyara yankin inda ya gana da shugabanni da wakilan al’umma.
Yanzu haka an fara samun zaman lafiya yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da tabbatar da tsaro a yankin.
Wannan lamarin ya faru ne kwanaki huɗu bayan wasu ’yan bindiga sun kai hari kasuwa a Ƙaramar Hukumar Wase, inda suka sace ’yan kasuwa biyar kuma suka kwashe kayayyaki.
Har ila yau, an ruwaito cewar maharan sun isa kasuwar ne a babura a ranar Litinin, lokacin da kasuwa ta cika da ’yan kasuwa da masu sayayya daga sassa daban-daban.
Sun fara harbe-harbe wanda ya sa mutane suka tsere domin tsira da rayukansu.
A baya-bayan nan, ɗaruruwan mutane sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka rasa muhallansu sakamakon hare-haren da ake yawan kai wa wasu sassan Jihar Filato.
Gwamna Caleb Muftwang na Jihar Filato, ya bayyana waɗannan hare-hare a matsayin yunƙurin kisan ƙare dangi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya
Ana zargin wata mata mai suna Khadija kan zargin kashe ’yarta mai shekaru 11, Fadila, saboda Naira 100 da ta samu a yawon Sallah a unguwar Tukur Tukur da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar kafin sallar Magariba, inda lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a unguwar har maƙwabta suka ƙi yi wa gawar yarinyar sallah saboda tsoron abin da zai biyo baya.
Ranar Dimokuraɗiyya: Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3Wasu maƙwabta sun bayyana cewa Khadija ta doke Fadila da taɓarya ne saboda ta zargi yarinyar da satar Naira 100.
Sun ce irin wannan ɗabi’a na duka da tsangwama ba sabon abu ba ne domin sau da dama idan ta tura Fadila talla aka samu matsala, sai ta lakaɗa mata dukan tsiya.
Wani mutum ya ce: “Dalilin da ya sa muka ƙi yi mata sallah shi ne, ba a ɗauki matakin da ya dace ba. An zubar da gaskiya. Saboda haka mu ma muka yanke shawarar ba za mu yi mata sallah ba.”
Amma mahaifiyar da ake zargi, wato Khadija, ta musanta zargin cewa ta yi wa ’yarta da duka da taɓarya.
Ta ce a lokacin da ta ke dukan yarinyar, ba kowa a gidan sai yara.
Mijin matar, Malam Mustapha Musa, ya shaida wa wakilinmu cewa lokacin da lamarin ya faru ba ya gida, don haka bai san yadda abin ya wakana ba.
Tuni mahaifin Fadila ya ɗauki gawar ’yarsa zuwa ƙauyensu da ke ji6har Kano domin yi mata sutura.
Ya ce: “Na bar komai da hannun Allah.”
Wani jami’in tsaron sa-kai wanda ya buƙaci a sakaya sunansa ya ce sun gayyaci Khadija da mijinta ofishinsu domin amsa tambayoyi, amma daga baya sai suka janye bayan sun ga ’yan sanda sun isa wajen.
Wakilinmu ya kai ziyara babban ofishin ’yan sanda da ke Ɗan Magaji, amma ya tarar babban jami’in ba ya nan.
Mataimakinsa ya ce ba su da masaniya game da lamarin.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya ce: “Ka jira, zan tuntuɓi ofishin yankin don jin yadda lamarin yake.”
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani daga ’yan sandan ba.