Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza
Published: 16th, May 2025 GMT
Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Amurka tana da hannu dumu-dumu a muggan ayyukan da gwamnatin ‘yan shayoniyya suka aikata nakisan kare dangi a Gaza
Jakada kuma wakilin dindindin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya yi nuni da ire-iren laifuffukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya suke ci gaba da aikatawa kan al’ummar Falastinu, yana mai bayyana wadannan laifuka a matsayin wani misali karara na kisan kiyashi yana kuma daukar Amurka a matsayin babbar kawa a aikata wadannan muggan laifuka.
A yayin zama na musamman a Majalisar Dinkin Duniya a yammacin jiya Alhamis kan batun boren Falasdinawa “Ankaba” na musamman ya bayyana cewa: Gwamnatin yahudawan sahayoniyya tana so da cikakken goyon baya da taimakon Amurka ta hanyar kaddamar da harte-haren wuce gona da iri da gangan ta rusa asibitoci, makarantu, kashe mata da yara, kaiwatar da kisan gilla kan ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya da ‘yan jarida da sauransu, lamarin da a halin yanzu ya yi sanadin shahadar mutane kusan 60,000 da jikkata wasu da kuma bacewar wasu da dama.
Babban jami’in diflomasiyyar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Munanan laifukan da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta aikata, ba za a iya musantawa ba, kuma kungiyoyin duniya, kotun duniya da sauran hukumomin shari’a na da masaniya kan irin girman wadannan munanan ayyukan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Iran a Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Amurka Ya Samu Damar Shimfida Munanan Muradun Kasarsa Kan Sabuwar Gwamnatin Siriya
Bukatun da shugaban Amurka ya fara gabatarwa shugaban gwamnatin Siriya al-Julani a gamuwarsu ta farko
Fadar shugabanci ta Amurka White House ta bayyana cikakken bayani kan ganawar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi da shugaban gwamnatin rikon kwarya ta Siriya, Ali al-Julani, a birnin Riyadh fadar mulkin kasar Saudiyya a ranar Laraba.
A cikin wata sanarwa da fadar White House ta fitar ta ce: Trump ya karfafa al-Julani da yin abin da ya bayyana a matsayin wani babban aiki ga al’ummar Siriya, wato sanya hannu kan yarjejeniyar kyautata alakar jakadanci da gwamnatin yahudawan sahayoniyya, a karkashin tsarin da kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa, Bahrain da Morocco suka kulla alaka da gwamnatin mamayar Isra’ila a shekara ta 2020.
Trump ya kuma yi kira ga al-Julani da ya kori Falasdinawa daga Siriya, yana nufin manyan shugabannin kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinu.
Trump ya kuma yi kira ga al-Julani da ya yi aiki don hana sake bullowar kungiyar ta’addanci ta Da’ish wato ISIS a Siriya.