Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
Published: 15th, May 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa sabuwar rundunar masu tsaron daji a faɗin ƙasar nan domin tinkarar matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a cikin dazukan Najeriya.
A ƙarƙashin wannan sabon shiri, za a ɗauki sama da mutane 130,000 aiki da za su samu horo na musamman da kayan yaƙi na zamani domin kare dazuka guda 1,129 da ke sassa daban-daban na ƙasar nan.
Wannan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Sunday Dare, ya fitar a shafinsa na X.
Sanarwar ta bayyana cewa an amince da shirin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka gudanar ranar Litinin.
A cewar sanarwar, shugaba Tinubu, ya umarci kowace jiha da ta ɗauki ma’aikata daga 2,000 zuwa 5,000 bisa ƙarfin kasafin kuɗinta, domin zama ’yan tsaron daji.
Ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro da ma’aikatar muhalli za su sanya ido a kan tsarin ɗaukar ma’aikatan da horar da su.
Babban aikin waɗannan masu tsaron dajin shi ne fatattakar ’yan ta’adda da miyagu da ke ɓuya a dazuka suna aikata laifuka.
Sanarwar ta ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya bayyana buƙatar a bai wa masu aikin horo mai kyau da makamai na zamani domin kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ya fito ƙarara ya goyi bayan shugaban ƙasa wanda ba a cikin jam’iyyarsu yake, Soludo ya ce goyon bayansa ga Tinubu ba sabon abu ba ne.
“An samar da waɗannan huluna tun lokacin da Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Anambra kuma kun ga allunan talla da sauran abubuwa da ke bayyana cewa masu ra’ayin kowa ci gaba suna aiki tare ne da juna,” in ji Soludo.
“Bayan haka, wannan wata babbar manufa ce da na yi imani da ita sosai, cewa ya kamata dukkan jam’iyyun siyasa da ke ikirarin ra’ayin ci gaba su haɗu a ƙarƙashin wata babbar ƙawance don zurfafa tunani da kawo ci gaba ba kawai a tafarkin dimokuradiyyarmu ba, har ma da ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasarmu.”
Gwamnan ya jaddada cewa kiransa na ganin masu ra’ayin ci gaba sun yi aiki tare ya samo asali ne daga yaƙini da kuma daɗaɗɗiyar alaƙar da ke tsakaninsa da Shugaban Ƙasa.
“Idan na ce masu ra’ayin ci gaba su yi aiki tare, kira ne ga duk masu magana kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu… Ina nufin, ba ni da wani uzuri game da hakan.
“Shugaba Tinubu abokina ne, abokina ne tun shekaru 22 da suka gabata zuwa yanzu.
“Abokina ne, ina goyon bayansa, kuma na gamsu da matakan da ya ɗauka, musamman a fannin tattalin arziki, kuma na bayyana hakan ba sau ɗaya ba, muna kan hanyar ƙwarai kuma muna buƙatar mu ci gaba a haka,” in ji Soludo.
Game da halin tsaro a Jihar Anambra, gwamnan ya ce gwamnatinsa ta ɗauki wani tsari na bai-daya tun daga watan Janairu, biyo bayan zartar da dokar tsaron cikin gida a jihar.
“Ana kokarin tunkarar matsalar rashin tsaro ne tun daga tushe. Dukkanin miyagun ‘yan ta’adda sun tsere daga jihar saboda su ne ke yaudarar matasanmu da kuma jefa su cikin aikata laifuka,” in ji shi.
Soludo ya ce gwamnati na amfani da matakan karfi da na lallashi don magance matsalar rashin tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp