Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
Published: 15th, May 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa sabuwar rundunar masu tsaron daji a faɗin ƙasar nan domin tinkarar matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a cikin dazukan Najeriya.
A ƙarƙashin wannan sabon shiri, za a ɗauki sama da mutane 130,000 aiki da za su samu horo na musamman da kayan yaƙi na zamani domin kare dazuka guda 1,129 da ke sassa daban-daban na ƙasar nan.
Wannan na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Sunday Dare, ya fitar a shafinsa na X.
Sanarwar ta bayyana cewa an amince da shirin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta tarayya da aka gudanar ranar Litinin.
A cewar sanarwar, shugaba Tinubu, ya umarci kowace jiha da ta ɗauki ma’aikata daga 2,000 zuwa 5,000 bisa ƙarfin kasafin kuɗinta, domin zama ’yan tsaron daji.
Ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro da ma’aikatar muhalli za su sanya ido a kan tsarin ɗaukar ma’aikatan da horar da su.
Babban aikin waɗannan masu tsaron dajin shi ne fatattakar ’yan ta’adda da miyagu da ke ɓuya a dazuka suna aikata laifuka.
Sanarwar ta ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya bayyana buƙatar a bai wa masu aikin horo mai kyau da makamai na zamani domin kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
An sake tabbatar wa ma’aikatan Gwamnatin Tarayya FG da suka yi ritaya cewa za a biya su wani bangare na kudaden ariyas a cikin wannan watan, kamar yadda hukumomin da abin ya shafa suka yi alkawari.
Mataimakin Sakataren ƙungiyar masu karɓar fansho ta ƙasa, Alhaji Ahmed Gazali, ya bayar da wannan tabbaci yayin da ake tattaunawa da shi ta wayar tarho daga Abuja.
Alh. Ahmed Gazali, ya yi bayanin cewas daraktan dake kula da kudade na ofishin akanta janar na tarayya ya tabbatar da daukan matakin hakan na biyan kudaden.
Ya bayyana fatan ganin kudirin FG na gaggauta biyan kudade, domin dakatar da duk wata zanga zanga wanda hakan bai dace ba ga ma’aikatan da suka yi ritaya domin bata martaban kasan nan.
Hakan kuma masu karban fensho a Radion Tarayya na kasa FRCN da Gidan talabijin na kasa NTA dake Kaduna sun nuna damuwarsu game da zargin da ake yi cewa ana kokarin wulakanta shugabannin kungiyar ma’aikatan da suka yi ritaya karkashin jagorancin kwamaret Munkaila Ogunbote.
DAGA SULEIMAN KAURA