Aminiya:
2025-10-13@20:04:42 GMT

Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC

Published: 15th, May 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci zauren Majalisar Wakilai a ranar Alhamis domin ganewa idanunsa ficewar wasu mambobi biyu na Jam’iyyar adawa ta NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

’Yan majalisar biyu, sun haɗa da: Dan Majalisar Wakilai, Abdullahi Sani Rogo mai wakiltar mazaɓar Rogo/Karaye da kuma Ɗan Majalisar Wakilai Kabiru Alhassan Rurum mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Rano/Bunkure/Kibiya, sun sauya sheƙa a ranar Alhamis.

Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista

Hakazalika mamba mai wakiltar mazaɓar Ijesha Oriade/Obokun na Jihar Osun, Wole Oke, ya kuma bayyana ficewarsa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC.

Shugaban Majalisar Wakilai Tajudden Abbas  wanda ya sanar da sauya sheƙar, ya bayyana cewa mambobin sun bayyana dalilansu na ficewa daga jam’iyyarsu zuwa APC.

Sai dai Babban mai tsawatarwa na Marasa Rinjaye, Isa Ali JC, ya nuna rashin amincewarsa da cewa sauya sheƙar ya sabawa kundin tsarin mulkin ƙasar.

Ganduje wanda ya samu rakiyar wasu jami’an jam’iyyar, ya fice bayan sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi October 10, 2025 Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC  October 9, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana
  • An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa