Aminiya:
2025-08-15@07:45:14 GMT

Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC

Published: 15th, May 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci zauren Majalisar Wakilai a ranar Alhamis domin ganewa idanunsa ficewar wasu mambobi biyu na Jam’iyyar adawa ta NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

’Yan majalisar biyu, sun haɗa da: Dan Majalisar Wakilai, Abdullahi Sani Rogo mai wakiltar mazaɓar Rogo/Karaye da kuma Ɗan Majalisar Wakilai Kabiru Alhassan Rurum mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Rano/Bunkure/Kibiya, sun sauya sheƙa a ranar Alhamis.

Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista

Hakazalika mamba mai wakiltar mazaɓar Ijesha Oriade/Obokun na Jihar Osun, Wole Oke, ya kuma bayyana ficewarsa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC.

Shugaban Majalisar Wakilai Tajudden Abbas  wanda ya sanar da sauya sheƙar, ya bayyana cewa mambobin sun bayyana dalilansu na ficewa daga jam’iyyarsu zuwa APC.

Sai dai Babban mai tsawatarwa na Marasa Rinjaye, Isa Ali JC, ya nuna rashin amincewarsa da cewa sauya sheƙar ya sabawa kundin tsarin mulkin ƙasar.

Ganduje wanda ya samu rakiyar wasu jami’an jam’iyyar, ya fice bayan sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

An zabi sabuwar firaminista a Luthuania

Shugaban ƙasar Lithuania, Gitanas Nauseda, ya zabi ’yar majalisa Inga Ruginiene ta jam’iyyar Social Democrat, a matsayin firaminista, bayan Gintautas Paluckas ya yi murabus sakamakon binciken rashawa da ake gudanarwa a kansa.

Sai dai Ruginiene ta taba fuskantar suka kasancewar tana da alaka da ’yan uwa a Rasha, wadanda ta ziyarta a shekarun 2015 da 2018.

Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC Tinubu ya cancanci yabo kan daidaita tattalin arzikin Nijeriya —Ngozi

Sai dai ta ce yanzu daina kai musu ziyara, kuma ta jaddada cewa tun farko Ukraine take mara wa baya a yakin da take yi da Rasha, wadda ta kaiwa mamaya a 2022.

Majalisar dokokin ƙasar za ta amince da nadinta tare da ministocinta kafin ta kama aiki.

A makon da ya gabata ne gwamnatin Paluckas ta yi murabus, bayan jam’iyyar Democrat  ta janye goyon bayan hadin gwiwar da ke kunshe da jam’iyyar populist ta Nemunas Dawn, lamarin da ya haifar da rikicin siyasa.

Hukumar kula da laifukan kudi (FNTT) ta kama ɗan uwan Paluckas a ranar Alhamis tare da wasu mutum huɗu a wani bincike kan kamfanonin da ake alaka da tsohon firaministan.

Sai dai har yanzu babu wata tuhuma da aka gabatar a kan Paluckas.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • An zabi sabuwar firaminista a Luthuania
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita
  • Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna