Iran ta bayyana cewa za ta yi zama gobe Juma’a da kasashen nan na turai guda uku da ake kira E3, wato Biritaniya, Jamus da kuma Faransa kan shirinta na nukiliya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya bayyana cewa, a ranar Juma’a 16 ga watan Mayu ne za a yi shawarwari karo na hudu da Teheran da kasashen Turan da suka kulla yarjejeniyar nukiliyar 2015.

Ya ce za a gudanar da taron ne a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.

Babban ajandar taron dai shi ne ci gaba da tuntubar juna da kasashen uku, musamman kan shawarwarin dake tsakanin Tehran da Washington.

Ya zuwa yanzu dai Iran da kasashen turai sun gudanar da shawarwari guda uku kan batun nukiliyar kasar Iran.

Tun da farko an shirya gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawa tsakanin Iran da Turai a birnin Rome a ranar 30 ga watan Afrilu, gabanin tattaunawar karo ta hudu da Amurka. To sai dai kuma saboda dage ganawar, aka samu jinkiri wajen guduanar da taron da kasashen Turai.

Ganawar da za’ayi gobe Juma’a ta biyo bayan zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Tehran da Washington, wanda aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata a karkashin jagorancin masarautar Oman.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta zargi dan jarida kuma mai shiga tsakani da ’yan ta’addar da suka sace fasinjojin jrigin kasan Kaduna-Abuja a shekarar 2022, Tukur Mamu, da karbar Naira miliyan 50 daga kudin fansar fasinjojin.

Ana zargin Tukur Mamu da karbar kudin ne daga jagoran ’yan bindigar da ake kira da “Shugaba”.

Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000 Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi

Mamu na fuskantar tuhumar laifukan ta’addanci, ciki har da karɓar kuɗin fansa daga iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a harin jirgin Kaduna na ranar 28 ga Maris, 2022, hulɗa da kuɗaɗen ’yan ta’adda, hana aikin kwamitin babban hafsan tsaron kasa da aka kafa domin tattaunawa da masu garkuwa da mutanen, musayar saƙonnin murya da mai magana da yawun Boko Haram, da sauransu.

A ci gaba da shari’ar a ranar Talata, shaida na hukumae ta DSS na shida ya shaida wa kotu cewa ƙungiyar ta’addan ta nemi Mamu ya koya musu yadda ake buɗe shafin yanar gizo domin gudanar da ayyukansu.

Tun da farko, DSS ta bayyana cewa Mamu ya ba da shawara ga ƙungiyar ’yan ta’addan da su tattauna kai tsaye da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su, ba tare da shiga kwamitin babban hafsan tsaron da gwamnatin tarayya ta kafa ba.

Shaidar ya yi wannan bayani ne yayin fassara saƙonnin murya na Mamu a lokacin da ake yi masa tambayoyi a ƙasar Masar kafin a dawo da shi Najeriya.

A halin yanzu, Mamu ya shigar da Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN) kara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bisa kiran shi da dan ta’adda.

Ya ce ya shigar da ƙarar ce kan kiran nasa da dan ta’adda da ministan ya yi, alhali ana tsaka da shari’ar tuhumar laifukan ta’addanci kuma har yanzu ba a kai ga yanke hukunci ba.

Alƙali ya dage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Fabrairun 2026, domin amincewa da jawaban ƙarshe na ɓangarorin da abin ya shafa bisa tanadin Sashe na 49 na Dokar da kuma Sashe na 36 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi
  • Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai
  • An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin