Iran za ta gudanar da taro da kasashen Turai a Istanbul kan shirinta na nukiliya
Published: 15th, May 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa za ta yi zama gobe Juma’a da kasashen nan na turai guda uku da ake kira E3, wato Biritaniya, Jamus da kuma Faransa kan shirinta na nukiliya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya bayyana cewa, a ranar Juma’a 16 ga watan Mayu ne za a yi shawarwari karo na hudu da Teheran da kasashen Turan da suka kulla yarjejeniyar nukiliyar 2015.
Ya ce za a gudanar da taron ne a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.
Babban ajandar taron dai shi ne ci gaba da tuntubar juna da kasashen uku, musamman kan shawarwarin dake tsakanin Tehran da Washington.
Ya zuwa yanzu dai Iran da kasashen turai sun gudanar da shawarwari guda uku kan batun nukiliyar kasar Iran.
Tun da farko an shirya gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawa tsakanin Iran da Turai a birnin Rome a ranar 30 ga watan Afrilu, gabanin tattaunawar karo ta hudu da Amurka. To sai dai kuma saboda dage ganawar, aka samu jinkiri wajen guduanar da taron da kasashen Turai.
Ganawar da za’ayi gobe Juma’a ta biyo bayan zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Tehran da Washington, wanda aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata a karkashin jagorancin masarautar Oman.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh
Shugaban kasar Amurka Donal trump da shugaban kasar Masar Abdulfatta Assisi ne zasu jagoranci bikin rattaba hannu kann yarjeniyar Sulhu wacce ta kawo karshen yaki da kuma kissan kiyashin da HKI ta yi a Gaza na tsawon shekaru 2, daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa ranar Alhamis 8 ga watan Octoban shekara ta 2025.
Shafin yanar gizo na labarai ArabNews ya bayyana cewa babban sakataren MDD Antonio Gutteres da shuwagabanin kungiyoyin kasashen Larabawa da Turai zasu halittu taron na gobe litinin a sharam Sheikh na kasar Masar.
Labarin ya kara da cewa za’a gudanar da taron ne a gobe litinin, bayan azahar kuma ana saran shuwagabannin kasashe fiye da 20.
Firai ministan kasar Burtaniya Keir Starmer, na Italiya, Giorgia Meloni da kuma Pedro Sanchez firai ministan kasar Spain. Da kuma shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron zai sami halattan taron.
Labarin ya kamala da cewa babu tabbas kan cewa Benyamin Natanyahu Firai ministan HKI zai halarci taron saboda yadda wasu shuwagabannin da suke halattan taron suke kinsa. Hossam Badran na kungiyar Hamas yace reshen kungiyar Hamas bata cikin yarjeniyar. Za’a fara aiwatar da musayar Fursinoni a gobe litinin tsakanin bangarorin biyu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar . October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci