Iran za ta gudanar da taro da kasashen Turai a Istanbul kan shirinta na nukiliya
Published: 15th, May 2025 GMT
Iran ta bayyana cewa za ta yi zama gobe Juma’a da kasashen nan na turai guda uku da ake kira E3, wato Biritaniya, Jamus da kuma Faransa kan shirinta na nukiliya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya bayyana cewa, a ranar Juma’a 16 ga watan Mayu ne za a yi shawarwari karo na hudu da Teheran da kasashen Turan da suka kulla yarjejeniyar nukiliyar 2015.
Ya ce za a gudanar da taron ne a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.
Babban ajandar taron dai shi ne ci gaba da tuntubar juna da kasashen uku, musamman kan shawarwarin dake tsakanin Tehran da Washington.
Ya zuwa yanzu dai Iran da kasashen turai sun gudanar da shawarwari guda uku kan batun nukiliyar kasar Iran.
Tun da farko an shirya gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawa tsakanin Iran da Turai a birnin Rome a ranar 30 ga watan Afrilu, gabanin tattaunawar karo ta hudu da Amurka. To sai dai kuma saboda dage ganawar, aka samu jinkiri wajen guduanar da taron da kasashen Turai.
Ganawar da za’ayi gobe Juma’a ta biyo bayan zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Tehran da Washington, wanda aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata a karkashin jagorancin masarautar Oman.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran
A safiyar yau ne aka gudanar da tattakin jana’izar shahidai kimani 60 a nan Tehran, wadanda suka hada da kwamandojin sojojin kasar da da masana fasahar Nukliya da sauran mutane maza da mata.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto cewa, an fara tattakin Jana’izar ne daga danganlin inkilabi ko juyin juya hali har zuwa dandalin yenci dake tsakiyar birnin na Tehran . Ana dauke da gawakin shahidan rufe da tutan Iran a cikin akwatuna.
Daga cikin manya-manyan bakin da suka halarci tattakin har da shugaban kasa Dr Masoud Pezeshkiyan da kuma wasu ministocinsa . A ranar 13 ga watan Yuni ne HKI ta fara kaiwa kasar Iran yaki inda ta kashe mutane da dama daga daga ciki har da manya-manyan kwamandojojin sojojin kasar da masana fasahar Nukliya da kuma sauran mutanen gari maza da mata da yara. Muta ne kimani 600 ne suka yi shahadi a cikin yakin kwanaki 12 da HKI ta kai hare-haren.
Bayan yan sa’o’I ne sojojin kasar ta Iran suka fara maida martani da dandazon makamai masu linzami. Wadanda suka lalata biranen HKI, har sai da suka nemi tsagaita wuta. Kafin karshen yakin dai sojojin Iran sun kai dandazon makamai har sau 22. An tsagaita wuta ne a ranar 24 ga watan Yuni.