HausaTv:
2025-06-30@09:56:59 GMT

Rasha Da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga domin tattaunawa a Turkiyya

Published: 15th, May 2025 GMT

Rasha da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga dukkansu domin gudanar da tattaunawa ta kai tsaye tsakanin kasashen dake rikici da juna.

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya aike da tawagar Ukraine zuwa birnin Istanbul na kasar Turkiyya domin ganawa da wakilan Rasha domin tattaunawa kan zaman lafiya, amma shi da kansa ba zai je can ba, kamar yadda wani babban jami’in Ukraine ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP.

Jami’in ya ce “Shugaban ya yanke shawarar cewa Ukraine za ta shiga tattaunawa da Rasha a Istanbul amma Volodymyr Zelensky ba zai je Istanbul ba saboda taron “ba a matakin shugabanni ba.

Ita ma fadar Kremlin ta sanar da jerin sunayen wakilan kasar don tattaunawa da Ukraine a Istanbul.

Amma ta ce Shugaban kasar ko kuma ministan harkokin waje ba zasu jagoranci tawagar ba.

Shugaban tawagar kasar Rasha Vladimir Medinsky ya bayyana cewa, babban aikin shawarwarin da za a yi tsakanin Rasha da Ukraine shi ne kawar da musabbabin rikicin da samar da zaman lafiya mai dorewa.

Ya jaddada cewa Rasha na kallon sabuwar tattaunawar a matsayin ci gaba da shirin zaman lafiya da aka yi a shekarar 2022.

Rasha ta abkawa Ukraine ne a ranar 24 ga Fabrairu na 2022, bayan amincewa da Moscow ta yi da ‘yancin kai na Jamhuriyar Donbass.

Matakin da Kasashen yammaci da kawayensu suka yi tir da shi, tare da laftawa Rasha jerin takunmumai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin aure da aka kashe a Jihar Filato.

Tun da farko, Hakimin Basawa, Haruna Abubakar ne, ya wakilci Sarkin lokacin da lamarin ya faru, saboda Sarkin ya yi tafiya.

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Sarkin, ya bayyana baƙin cikinsa bisa wannan mummunan lamari, inda ya roƙi iyalan da su ɗauki wannan a matsayin ƙaddara.

Ya yaba da yadda suka yi haƙuri kuma suka bar komai ga hukuma, ba tare da ɗaukae doka a hannunsu ba.

Sarkin ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin an bi wa waɗanda abin ya shafa haƙƙinsu.

Ya ƙara da cewa zaman lafiya da haƙuri su ne mafita ga duk wata matsala, kuma hakan zai kawo ci gaba a tsakanin al’umma.

A yayin ziyarar, Sarkin ya samu rakiyar wasu daga cikin ’yan majalisarsa da hakimai.

Ya sake roƙon jama’a da su ci gaba da zaman lafiya tare da miƙa lamarin ga Allah.

Da yake magana a madadin iyalan garin, Mallam Muhammadu Dan Bami, ya gode wa Sarkin bisa ziyarar da ya kawo, tare da bayyana cewa mutanen garin masu bin doka da son zaman lafiya ne.

Daga ƙarshe, ya roƙi Sarkin da ya taimaka wajen ganin gwamnati ta cika alƙawarin da ta ɗauka na bi masu haƙƙinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
  • Majaliar Dokokin Kasar Corsica Ta Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu Sannan Ta Ki Amincewa Da HKI
  • Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador