Rasha Da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga domin tattaunawa a Turkiyya
Published: 15th, May 2025 GMT
Rasha da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga dukkansu domin gudanar da tattaunawa ta kai tsaye tsakanin kasashen dake rikici da juna.
Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya aike da tawagar Ukraine zuwa birnin Istanbul na kasar Turkiyya domin ganawa da wakilan Rasha domin tattaunawa kan zaman lafiya, amma shi da kansa ba zai je can ba, kamar yadda wani babban jami’in Ukraine ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Jami’in ya ce “Shugaban ya yanke shawarar cewa Ukraine za ta shiga tattaunawa da Rasha a Istanbul amma Volodymyr Zelensky ba zai je Istanbul ba saboda taron “ba a matakin shugabanni ba.
Ita ma fadar Kremlin ta sanar da jerin sunayen wakilan kasar don tattaunawa da Ukraine a Istanbul.
Amma ta ce Shugaban kasar ko kuma ministan harkokin waje ba zasu jagoranci tawagar ba.
Shugaban tawagar kasar Rasha Vladimir Medinsky ya bayyana cewa, babban aikin shawarwarin da za a yi tsakanin Rasha da Ukraine shi ne kawar da musabbabin rikicin da samar da zaman lafiya mai dorewa.
Ya jaddada cewa Rasha na kallon sabuwar tattaunawar a matsayin ci gaba da shirin zaman lafiya da aka yi a shekarar 2022.
Rasha ta abkawa Ukraine ne a ranar 24 ga Fabrairu na 2022, bayan amincewa da Moscow ta yi da ‘yancin kai na Jamhuriyar Donbass.
Matakin da Kasashen yammaci da kawayensu suka yi tir da shi, tare da laftawa Rasha jerin takunmumai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
Ɗan Majalisar Tarayya mai Wakiltar Sabon Gari Daga Jihar Kaduna, Sadiq Ango Abdullahi, ya fice daga Jam’iyyarsa ta PDP.
Honorabul Abdullahi wanda shi ne Mataimakin Shugaban Kwamishinan Hukumar Kula da Hanyoyi (FERMA) ya alaƙanta ficewarsa da rikicin cikin gida da rabuwar kai da ya ki ci ya ƙi cinyewa a jam’iyyar.
A ranar Litinin ya aike da wasikar ta ficewa ga Shugaban PDP na Mazabar Hanwa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, yana mai cewa rikicin ya hana shi taɓukawa matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Tarayya.
Ya cewa saboda haka yana dacewar ficewarsa daga jam’iyyar ba tare da la’akari da siyasa ba, domin amfanin ɗauƙacin al’ummar mazabar.
Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjayeYa yaba wa jam’iyyar bisa damar da kuma gudummawar da ta ba shi domin hidimta wa al’umma.