Rasha Da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga domin tattaunawa a Turkiyya
Published: 15th, May 2025 GMT
Rasha da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga dukkansu domin gudanar da tattaunawa ta kai tsaye tsakanin kasashen dake rikici da juna.
Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya aike da tawagar Ukraine zuwa birnin Istanbul na kasar Turkiyya domin ganawa da wakilan Rasha domin tattaunawa kan zaman lafiya, amma shi da kansa ba zai je can ba, kamar yadda wani babban jami’in Ukraine ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Jami’in ya ce “Shugaban ya yanke shawarar cewa Ukraine za ta shiga tattaunawa da Rasha a Istanbul amma Volodymyr Zelensky ba zai je Istanbul ba saboda taron “ba a matakin shugabanni ba.
Ita ma fadar Kremlin ta sanar da jerin sunayen wakilan kasar don tattaunawa da Ukraine a Istanbul.
Amma ta ce Shugaban kasar ko kuma ministan harkokin waje ba zasu jagoranci tawagar ba.
Shugaban tawagar kasar Rasha Vladimir Medinsky ya bayyana cewa, babban aikin shawarwarin da za a yi tsakanin Rasha da Ukraine shi ne kawar da musabbabin rikicin da samar da zaman lafiya mai dorewa.
Ya jaddada cewa Rasha na kallon sabuwar tattaunawar a matsayin ci gaba da shirin zaman lafiya da aka yi a shekarar 2022.
Rasha ta abkawa Ukraine ne a ranar 24 ga Fabrairu na 2022, bayan amincewa da Moscow ta yi da ‘yancin kai na Jamhuriyar Donbass.
Matakin da Kasashen yammaci da kawayensu suka yi tir da shi, tare da laftawa Rasha jerin takunmumai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
Biyo bayan wani rahoto da ma’aikatar lafiya ta tarayya ta fitar na cewa sama da likitoci 16,000 ne suka bar Najeriya a cikin shekaru bakwai da suka gabata domin neman aiki a wasu kasashe, gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri na cike gurbin da likitocin suka haifar.
Da yake zantawa da manema labarai a Katsina, Shugaban Hukumar Kula da Ilimi ta Kasa (TETFund), Alhaji Aminu Bello Masari, ya ce hukumar ta kaddamar da wani shiri na musamman domin horar da karin likitoci, ma’aikatan jinya, masu harhada magunguna da kwararrun dakin gwaje-gwaje a manyan makarantun kasar nan.
Ya ce tuni hukumar ta TETFUND ta zuba sama da Naira biliyan 100 a manyan makarantu goma sha takwas domin kara karfinsu na horar da dalibai a fannin ilimin likitanci, ta hanyar samar da dakunan karatu, dakunan gwaje-gwaje da sauran abubuwan da suka shafi ababen more rayuwa da ilimi.
Masari ya ce, wannan matakin shiri ne don ba da damar tsarin kiwon lafiya ya farfado daga ficewar ma’aikatan lafiya tare da kara karfin ma’aikata a fannin.
Ya bayyana cewa an zabo manyan makarantu guda uku a kowace shiyyar siyasar kasar nan saboda kowace cibiya ta samu Naira biliyan 4 don gudanar da ayyuka da kuma sayan kayan aikin da ake bukata domin kara karfin daukar dalibai da horar da dalibai a fannin ilimin likitanci.
Masari ya bayyana cewa sun dauki matakin ne saboda muradin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na ganin an magance karancin ma’aikata a fannin kiwon lafiya da ke yin illa ga ayyukan hidima a fannin.
“A shekarun baya-bayan nan, likitoci da ma’aikatan jinya da yawa da masana harhada magunguna da kwararrun likitoci da sauran kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sun bar kasar nan don neman aiki mai gwabi a kasashen waje.
Isma’il Adamu/Katsina