A yau ne za a gudanar da tattaunawar zaman lafiya kan yaƙin da ke tsakanin Ukraine da Rasha a birnin Istanbul da ke ƙasar Turkiyya, – amma fadar Kremlin ta bayyana cewa shugaban Rasha, Vladimir Putin, ba ya cikin jerin jami’an da za su halarci tattaunawar.

Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai sun ce shugaban Amurka Donald Trump shima ba zai halarci taron ba – duk da cewa ya nuna sha’awar halarta jiya idan har Putin zai je.

Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, zai kuma kasance a babban birnin Turkiyya, Ankara a yau don ganawa da shugaba Recep Tayyip Erdogan inda ya ce zai je taron tattaunawar da Rasha a Istanbul ne kawai idan Putin ya halarta.

Tun daga watan Disamba na shekarar 2019 ne ba a sake ganawa a zahiri tsakanin Putin da Zelensky ba.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rasha

এছাড়াও পড়ুন:

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Ƴan majalisar tarayya guda biyu daga jihar Kano, Kabiru Usman da Abdullahi Sani, sun sanar da barin jam’iyyar NNPP zuwa APC a yayin zaman majalisar ranar Alhamis, suna mai nuni da rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyar.

Shugaban majalisar Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙun ficewarsu a zaman majalisar, inda ya bayyana cewa Usman na wakiltar mazabar Rano/Bunkure/Kibiya, yayin da Sani na wakiltar Karaye/Rogo.

Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC Gwamna Yusuf Ya Yi Barazanar Ƙwace Lasisin Jerin Gidajen Kwankwasiyya, Amana Da Bandirawo 

Ko da a kwanan baya ma Sanata AbdulRahman Kawu Sumaila da wasu  sun fice daga jam’iyyar NNPP, su ma dai sun ce rikicin ne ya fitar da shi.

Shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Ganduje da wasu manyan ƙososhin jam’iyyar sun halarci taron sauyin sheƙar a majalisar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
  • Shuagabn Kasar Amurka Ya  Sanar Da Kusancin Kulla  Yarjejeniya Da Iran
  • Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
  • Babban Sakataren MDD Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Biya Rabonsu Na Kudaden Tsaron Kasa Da Kasa
  • Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
  •  An Bude  Taron Karawa Juna Sani Akan Makamashin Nukiliyar Iran Karo Na 31 A birnin Mashhad
  • Za A Samar Da Na’urar Kula Da Lafiyar Zuciya A Jami’ar Dan Fodio Da Ke Sakkwato
  • Majalisar Kaduna Za Ta Sanya Mutane 700 Cikin Tsarin Kiwon Lafiya Na Jiha