Iran Da Kasashen Turai uku wato E3 Zasu Bude Tattaunawa A Tsakaninsu A Birnin Istambul A Gobe Jumma’a
Published: 15th, May 2025 GMT
Manya-Manyan Jami’an gwamnatin kasar Iran da tokwarorinsu na kasashen turai uku wadanda ake kira, E3 zasu fara tattaunawa a tsakaninsu dangane da tattaunawa dangane da makamashin nukliya tsakanin Iran da Amurka wanda ke ci gaba a halin yanzu.
Kasashen E3 dai sun hhada da Faransa, Jamus da kuma Ingila wadanda suke sanyawa yarjeniyar JCPOA hannu a shekara ta 2015.
JMI tana ganin idan har an cimma wata yarjeniya da Amurka kan shirinta na makamashin nukliya ba zai bambanta sosai da JCPOA ba.
Yarjeniyar JCPOA sai ta shiga rudu tun bayan da shugaban Amurka mai ci ya fidda Amurka daga yarjeniyar a shekara ta 2018. Sannan kasashen Turai wadanda suka sanyawa yarjeniyar hannu a shekara ta 2015 suka biyewa Amurka suka dakatar da amfani da yarjeniyar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghaei ya tabbatar da hakan , ya kuma bayyana cewa za’a fara gudanar da taron a gobe Jumma’a 17 ga watan Mayu a birnin Istambul na kasar Turkiyya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
An watsa shirin talibijin mai taken “Yawon bude ido a Tuscany” a Florence na Italiya, da babban rukunin gidan radiyo da talibijin kasar Sin CMG da hukumar yawon bude ido ta yankin Tuscany na Italiya suka tsara da kuma gabatar cikin hadin gwiwa. Shugaban CMG Shen Haixiong da babban jami’in hukumar sun shaida bikin gabatarwar, kuma sun yi musanyar ra’ayi mai zurfi game da daukar shirye-shirye cikin hadin gwiwa da gabatar da albarkatun yawon bude ido da kiyaye al’adu da sauransu. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp