Manya-Manyan Jami’an  gwamnatin kasar Iran da tokwarorinsu na kasashen turai uku wadanda ake kira,  E3 zasu fara tattaunawa a tsakaninsu dangane da tattaunawa dangane da makamashin nukliya tsakanin Iran da Amurka wanda ke ci gaba a halin yanzu.

Kasashen E3 dai sun hhada da Faransa, Jamus da kuma Ingila wadanda suke sanyawa yarjeniyar JCPOA hannu a shekara ta 2015.

Manufar taron ko kuma tuntubar juna tsakanin Iran da wadannan kasashe uku itace sanyasu a kan hanya kan yadda tattaunawar take tafiya, da kuma yadda ake son a gabatar da sauye-sauye wa yarjeniyar JCPOA, tunda Amurka ta waresu daga wannan tattaunawar.

JMI tana ganin idan har an cimma wata yarjeniya da Amurka kan shirinta na makamashin nukliya ba zai bambanta sosai da JCPOA ba.

Yarjeniyar JCPOA sai ta shiga rudu tun bayan da shugaban Amurka mai ci ya fidda Amurka daga yarjeniyar a shekara ta 2018. Sannan kasashen Turai wadanda suka sanyawa yarjeniyar hannu a shekara ta 2015 suka biyewa Amurka suka dakatar da amfani da yarjeniyar.  

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghaei ya tabbatar da hakan , ya kuma bayyana cewa za’a fara gudanar da taron a gobe Jumma’a 17 ga watan Mayu a birnin Istambul na kasar Turkiyya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga

Wani yaro mai kimanin shekaru goma a duniya ya harbe mahaifinsa wanda jami’in ɗan sanda ne mai mukamin sufeto a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya.

Haka kuma, wakilinmu ya ruwaito cewa yaron ya harbi wani yayansa da bindigar mahaifin nasa ta aiki kirar AK-47.

Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Kakakin ya ce an gaggauta kai jamin asibiti domin a ceto rayuwarsa amma likitoci suka tabbatar da cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Sanarwar ta ce “a ranar Lahadi 15 ga watan Yuni, dan gidan wani jami’in dan sanda mai kimanin shekara goma da haihuwa ya harbe mahaifinsa har lahira ya kuma jiwa yayan sa mummunan rauni.

“Abin bakin ciki muna sanar da ku mutuwar jami’inmu mai mukamin sufeto, Okolie Amechi, bisa harbe shi da dansa ya yi a gidansa.

“Wannan ba karamin abin takaici ba ne da kaddara,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Kakakin Gwamnatin Iran Ta Ce daga Yau Lahadi Wuraren Fakewa A Bude Suke Sa’o’I 24 A Tehran
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida