Iran Da Kasashen Turai uku wato E3 Zasu Bude Tattaunawa A Tsakaninsu A Birnin Istambul A Gobe Jumma’a
Published: 15th, May 2025 GMT
Manya-Manyan Jami’an gwamnatin kasar Iran da tokwarorinsu na kasashen turai uku wadanda ake kira, E3 zasu fara tattaunawa a tsakaninsu dangane da tattaunawa dangane da makamashin nukliya tsakanin Iran da Amurka wanda ke ci gaba a halin yanzu.
Kasashen E3 dai sun hhada da Faransa, Jamus da kuma Ingila wadanda suke sanyawa yarjeniyar JCPOA hannu a shekara ta 2015.
JMI tana ganin idan har an cimma wata yarjeniya da Amurka kan shirinta na makamashin nukliya ba zai bambanta sosai da JCPOA ba.
Yarjeniyar JCPOA sai ta shiga rudu tun bayan da shugaban Amurka mai ci ya fidda Amurka daga yarjeniyar a shekara ta 2018. Sannan kasashen Turai wadanda suka sanyawa yarjeniyar hannu a shekara ta 2015 suka biyewa Amurka suka dakatar da amfani da yarjeniyar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghaei ya tabbatar da hakan , ya kuma bayyana cewa za’a fara gudanar da taron a gobe Jumma’a 17 ga watan Mayu a birnin Istambul na kasar Turkiyya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta cafke wasu maza biyu bisa zargin yi wa ƙananan yara mata fyaɗe a lokuta daban-daban a jihar.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, inda ya ce sun kama wani mutum mai shekara 47, da zargin yi wa ‘yar matarsa mai shekara biyu fyaɗe a Tudun Wada, Shamaki a ranar 5 ga watan Mayu.
’Yan bindiga sun kashe jarirai, sun bai wa karnuka namansu a Zamfara Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — AmaechiBayan samun rahoton daga matarsa, rundunar ’yan sandan ta garzaya gidansu inda ta kama wanda ake zargin, sannan suka kai yarinyar Asibitin Ƙwararru na Gombe domin duba lafiyarts.
Ya ce za a yi amfani da rahoton binciken asibitin a kotu.
Hakazalika, an kama wani mutum mai shekara 35 da ke unguwar Golkos a Ƙaramar Hukumar Billiri, bisa zargin yi wa wata yarinya ’yar shekara shida fyaɗe a unguwar Awai.
Mahaifiyar yarinyar ce ta rahoton faruwar lamarin, inda ’yan sanda suka kama wanda ake zargin, sannan suka garzaya da da yarinyar Asibitin Kaltungo domin duba lafiyarta.
DSP Abdullahi ya ƙara da cewa rundunar ta kama wasu mutane 18 daban da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar.