Al-Husy: Yakin Gaza Shi Ne Kisan Kiyashi Mafi Muni A Cikin Karni Daya
Published: 9th, May 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-husy ya bayyana cewa kisan kiyashin da HKI take yi wa Falasdinawa a tsawon watanni 19 a jere, shi ne laifi mani muni akan bil’adama da ya faru a cikin karni daya.
Sayyid Abdulmalik al-Husi ya kuma ce, abinda ya kara munin wannan laifin shi ne yadda yake faruwa a tsakiyar duniyar musulunci,kuma dukkanin duniya tana Kallon abinda yake faruwa.
Shugaban kungiyar ta “Ansarullah” ya kuma yi gargadin cewa da akwai sakamakon da zai biyo bayan wadannan manyan laifuka,yana mai kara da cewa. Alummar musulmi, a sahun gaba larabawa suna da alhakin abinda yake faruwa.
Haka nan kuma ya jaddada cewa babu wani dalili da zai sa a yi watsi da jihadi saboda Allah da kuma kalubalantar azzalumai, sannan ya kara da cewa, yin watsi da wannan farilla mai tsarki, zai iya jefa al’umma cikin fushin Allah madaukakin sarki, da hakan yake tattare da mummunan sakamako a duniya da lahira.
Sayyid Abdulmalik ya kuma bayyana cewa; Ci gaba da kau da kai da al’umma take yi akan abinda yake faruwa a Gaza, bai dauke mata nauyin da ya rataya a wuyanta ba,yana mai kara da cewa; Sakamakon da za a fuskanta daga Allah yana karuwa gwargwadon yadda ake samun koma-baya wajen yin abinda ya kamata akan al’ummar Falasdinu.
Akan tsayin dakar al’ummar Falasdinu kuwa, shugaban kungiyar ta “Ansarullah” ya jaddada cewa, ‘yan gwgawarmaya suna da dukkanin abinda suke bukatuwa da shi domin ci gaba da fuskantar ‘yan sahayoniya. Ya kuwa jinjinawa gwagwarmayar da kuma al’ummar Falasdinu baki daya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yake faruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
Wani sabon kudiri da ke gaban Majalisar Dokokin Amurka ya nemi a hana ’yan kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah da Miyetti Allah Kautal Hore bizar shiga Amurka.
Kudurin, wanda dan majalisa Christopher Smith ya gabatar a ranar Talata, ya kuma bukaci kwace kadarorin mambobin kungiyar.
An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwaWannan na daga cikin matakan da gwamnatin Amurka ke ɗauka don dakile abin da ta kira take hakkin ’yancin addini ga Kiristocin Najeriya.
Kudirin dai na neman hukunta mutane da ƙungiyoyi da ke da hannu ko goyon baya wajen take hakkin ’yancin addini mai, a ƙarƙashin dokar kasa da kasa ta IRFA.
Christopher ya yaba wa Shugaba Trump bisa sake ayyana Najeriya a matsayin Ƙasa Mai Ƙalubale Na Musamman, yana mai ambato rahotannin ci gaba da hare-hare kan al’ummomin Kirista a sassan ƙasar.
Kudirin ya kuma ambaci ’yan ta’adda Fulani da ke kai hare-hare a jihohin Binuwai da Filato a cikin kungiyoyin da ake sa’ido a kansu, wani matsayi da Amurka ke warewa ga ’yan ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba da ake zargi da take hakkin addini.
Sauran irin wadannan kungiyoyin da aka ayyana a baya a ƙarƙashin dokar sun haɗa da Boko Haram, ISWAP, ISIS-Sahel, Taliban da kuma Houthi.
Idan aka amince da kudirin, zai bai wa hukumomin Amurka damar hana biza da kuma kulle kadarorin mutanen da ke da alaƙa da waɗannan ƙungiyoyi.
An gabatar da kudirin ne bayan watanni na kiraye-kirayen yin hakan daga ’yan majalisar dokokin Amurka da ƙungiyoyin Kiristoci masu tsattsauran ra’ayin.
Shugaban Amurka Donald Trump dai ya yi zargin ana yi wa Kiristoci a Najeriya kisan kiya, amma gwamnatin kasar ta yi fatali da zarge-zargen inda ta kira shi a matsayin na karya.