Al-Husy: Yakin Gaza Shi Ne Kisan Kiyashi Mafi Muni A Cikin Karni Daya
Published: 9th, May 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-husy ya bayyana cewa kisan kiyashin da HKI take yi wa Falasdinawa a tsawon watanni 19 a jere, shi ne laifi mani muni akan bil’adama da ya faru a cikin karni daya.
Sayyid Abdulmalik al-Husi ya kuma ce, abinda ya kara munin wannan laifin shi ne yadda yake faruwa a tsakiyar duniyar musulunci,kuma dukkanin duniya tana Kallon abinda yake faruwa.
Shugaban kungiyar ta “Ansarullah” ya kuma yi gargadin cewa da akwai sakamakon da zai biyo bayan wadannan manyan laifuka,yana mai kara da cewa. Alummar musulmi, a sahun gaba larabawa suna da alhakin abinda yake faruwa.
Haka nan kuma ya jaddada cewa babu wani dalili da zai sa a yi watsi da jihadi saboda Allah da kuma kalubalantar azzalumai, sannan ya kara da cewa, yin watsi da wannan farilla mai tsarki, zai iya jefa al’umma cikin fushin Allah madaukakin sarki, da hakan yake tattare da mummunan sakamako a duniya da lahira.
Sayyid Abdulmalik ya kuma bayyana cewa; Ci gaba da kau da kai da al’umma take yi akan abinda yake faruwa a Gaza, bai dauke mata nauyin da ya rataya a wuyanta ba,yana mai kara da cewa; Sakamakon da za a fuskanta daga Allah yana karuwa gwargwadon yadda ake samun koma-baya wajen yin abinda ya kamata akan al’ummar Falasdinu.
Akan tsayin dakar al’ummar Falasdinu kuwa, shugaban kungiyar ta “Ansarullah” ya jaddada cewa, ‘yan gwgawarmaya suna da dukkanin abinda suke bukatuwa da shi domin ci gaba da fuskantar ‘yan sahayoniya. Ya kuwa jinjinawa gwagwarmayar da kuma al’ummar Falasdinu baki daya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yake faruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lallai zai kara rura wutar rikici a ci gaba da yakin da ake yi tsakanin Iran da Isra’ila.
Sai dai ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai da cewa “abin takaici ne” sannan ya ce Iran ta tanadi “dukkan zabin kare ‘yancinta”, yana mai jaddada cewa Amurka za ta fuskanci “tsauraran sakamako”.
Araghchi ya kara da cewa, Amurka ta keta kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya a matsayinta na mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.
Bugu da kari, wani dan Majalisar kasar Iran, ya kara da cewa, “babu wani mummunan lahani a wuraren, kuma dama tun kafin harin, an riga an kwashe duk wasu abubuwa masu muhimmanci na tashoshin nukiliyar”.
Tun da farko, Tehran ta yi gargadin cewa za ta kai hari kan muradun Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya domin daukar fansa kan duk wani hari da Amurka ta kai, kuma ya zuwa yanzu ta harba makamai masu linzami kan Isra’ila, inda aka ji karar fashewar wasu abubuwa a birnin Kudus.
A halin da ake ciki, kawunan ‘yan majalisar dokokin Amurka ya rabu dangane da shigar kasar, inda ‘yan jam’iyyar Republican suka yabawa Trump, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat suka yi gargadin cewa an jefa Amurka cikin wani yakin da ba nata ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp